Sashe 11
Kyautar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*D* eedat ya kasa jurewa shi ya sa ya azalzali da a biyo sahu. Ganinsu ya sa Nurat tsuke baki.
“Ke nake saurare Nurat, ba komai ki yi magana kin ji”.
Kawai Nurat ta yi qasa da kanta.
“Ummi ta ce, duk lokacin da na bari namiji ya tava min hannu zan samu ciki in haifi shege, idan na haifi shege mutuwa za ta yi, kuma su… su… sun tavan hannu…”
Ta qarasa cikin saka gursheqen kuka.
Deedat ya harba cikin tunani, gaba xaya jikinsa ya hau tsuma, wani irin tsoro ya ziyarci zuciyarsa tare da wani irin abu wanda ya kasa tantance ko me ye.
“Amma wannan zancen banza ne ta ya za a xora ki a kan wan…”
Deedat ya yi saurin dakatar da Malama Aisha, “Haka ne, Ammi ta yi gaskiya, ai na ga hannunsu bai tava naki ba sosai, yanzu za mu je asibiti in har da cikin za su gaya mana. Ki daina kuka kin ji ko”.
“Ina jin tsoro, za ta gane hakan ta faru, bana son na samu shege kowa zai tsane ni, bana son samun xan da ba shi da tsarki”.
Ba ya son jin kalamanta, da sauri ya yi waje, idanuwa sun sake rinewa, “Za mu je asibiti”. Ya faxa lokacin da ya bar ofis xin.
A can harabar makarantar Doctor Salim amininsa ya kira inda a taqaice ya ba shi labarin abin da ke faruwa, tare da sanar da shi ga shi nan tafe, yana kuma son a yi mata duk abin da zai sa ta samu nutsuwa. Ya yi saurin katse wayar daidai lokacin da Principal ya yi parking xin mota a gabanshi. A can baya ya hangi Nurat gidan gaba ya shiga, yana gano yadda hawaye suke faman tsinkowa daga idanun Nurat. Ya yi saurin kawar da ido, yayin da gabansa ya dinga dukan uku-uku, yarinya ce qarama, sai dai akwai ta da kwarjini. Lokaci-lokaci ya dinga satar kallonta har suka isa asibitin.
Abin da ya bai wa Nurat mamaki, yadda sunan makarantar da na asibitin suka zamo xaya.
Dr. Samir sun tsara komai da Nurse kafin su qaraso, sirinji ya xauka ya yi umarnin da ta miqo hannunta zai xauki jini domin gwaji. Nan fa idanunta suka yo waje, ji ta ke kamar ta sa gudu, sai ga wasu sababbin hawayen.
Dr. Samir babu wani abin da za a yi, maimakon xaukar jinin?” Deedat ya faxa.
“Dole dai sai dai jinin”.
Babu yadda ta iya haka ta runtse ido, ya shiga shirin zuqo jinin, inda Deedat ya xauko wayarsa a fakaice ya shiga xaukarta ta yadda babu mai lura da abin da yake yi.
Bayan an gama Nurse ta yi wani xaki da jinin, sun zauna sai ga sakamako ta shigo da shi. Ta miqa wa Dr. Salim, ya duba cikin gintse dariya a ciki, saboda yadda ya ga alamun tsoro qarara a idanun Nurat, sai da ya xan yi ‘yan rubuce-rubuce sannan ya sake xago kai cikin dubanta. Idanun nan sun yi luhu-luhu saboda kuka, tana jin kamar ta matsi bakinsa ya yi magana, Deedat kam yana iya jin bugun zuciyarta na tsananta, da yake shi ne a kusa da ita.
“Ina taya ki murna xalibar kirki, ba ki da matsala”.
Cike da farin ciki ta sake wani irin murmushi, dukan kumatunta suka lotsa. Wani irin wushirya mai xaukar hankali suka bayyana. Da sauri Deedat ya shiga xaukarta.
“Doctor na gode”. Ta ce.
Ya miqa mata ambulan, “Doctor na bar maka”.
Ya yi murmushi.
“Ki dai tafi da shi”.
Ta karva.
“Abu na gaba ina son kada wannan maganar ta fita ko a gida kada ki faxa kin ji ko?”
“Insha Allahu babu wanda zai ji”.
Cikin farin xiki ta ke magana.
Deedat ya shiga duniyar tunani, yana tunanin a inda ya san wannan muryar, sai dai duk iya yinsa haka ya haqura.
Sai da Principal ya sanya ta a mota aka maida ita makaranta, sannan ya dawo ofis xin Dr. Samir inda kowa ke faxin albarkacin bakinsa a kan al’amarin Nurat.
“Hakan na da kyau, ban yi tunanin akwai irin waxannan iyaye ba. babu wadda ta burge ni sai mahaifiyarta wacce ta xora ta a wannan turba”. In ji Salim.
Principal ya karve zancen, “Cikin class mate xinta ita ce mafi qanqantar shekaru, ga su nan ganxama-ganxama amma babu wadda ta kai ta qoqari. Qwaqwalwarta tamkar computer, irinsu ake ma laqabi da gifted. Na daxe ban ga yarinya kamarta ba, yadda xalibai da malamai ke qaunarta bai sa ta giggiwa ba, gaba xayanta ma tsoro ne da ita, ba ta shiga cikin mutane sosai. Ba qaramin abu ne zai sa ka ji bakinta a class ba, kullum ka ganta wala’Allah a makaranta ko a gida cikin hijabinta zumbulele kamar mai shirin tafiya masallaci. Su kansu malamai mata in sun zauna hirarta suke babu wanda ya tava kawo qararta’.
Haka ya yi ta bada labarinta, har sai da Deedat ya ji a cikin zuciyarsa babu masaqar tsinke, bai tava jin yadda yake ji game da ita ba a kan wata mace ba, shin me hakan ke nufi? Me ke shirin faruwa da shi?
“Ammi ta ce duk lokacin da na bari namiji ya tava min hannu zan samu cikin shege, idan na samu cikin shege mutuwa za ta yi”.
Sautin muryarta ya dinga yi masa kuwwa a kunne, ya shiga kai-komo, gaba xaya ya kasa samun nutsuwa. Bathroom ya shiga, gaba xayansa ya shige cikin shaya yana jin ko hakan zai saukar masa da nutsuwa. Babu abin da ya ragu, sai ma rikicewa da ya qara yi. Doguwar riga ya saka jallabiya mai yankakken hannu, ya yi zaman dirshan a kan carpet, kuka yake yi kamar qaramin yaro. Ya riqe kai yana juyawa cikin tafin hannunsa.
“Sun cutar da ni, sun cuce ni”.
Wani irin zazzavi mai zafi ya rufe shi har haqoransa na gwaruwa, barci ya sace shi. A can cikin baccin nasa babu abin da yake gani sai fuskar Nurat.
Tana zaune a farfajiyar gidan riqe da littafi a hannu tana karatu. Harxe hannu a qirji yana kallonta yana murmushi, bai qi ya tabbata a haka cikin kallon kyakkyawar fuskarta ba.
Jikinta ne ya ba ta akwai mutum tsaye a kanta, ta xan xago kai suka yi ido biyu. Ta yi saurin kawar da kai tare da faxin, “Zauna mana”.
Ta nuna masa kujera.
“Ban ji shigowarka ba”.
Yana murmushi, “kina zaune har na zo na shige na yi ciki, kin ga ke kam idan kina karatu ba kya ji ba kya gani”.
“Yaya Zaruk mun fa kusa fara jarabawa, ina son in karvi kyaututtuka a gurin Dad da Ammi, har ma da Yayata’.
Ya tafa hannu, “Da kyau yarinya mai wayo. To ki qara da tawa, zan yi miki kyautar da babu wanda zai yi miki irinta”.
Ta yi murmushi, cikin satar kallonsa.
“To, yanzu xan gaya mini kalar kyautar”.
“No, ki dai bari zan ba ki mamaki”.
“Allah ya nuna mana lokacin”.
Ta xan yi shiru tana tunanin wani abu.
“Wannan yarinya akwai magana a bakinki”.
“Yaya Zaruk inda a ce kowa zai riqe kyautarsa a yi mini alqawarin auren Yaya Aazeen, zan fi jin daxin haka fiye da komai”.
“Har yanzu ba ki bar wannan zancen ba? na ce da ke shi aure lokaci ne da zarar lokacin ya zo komai zai zamo labari”.
“Amma Yaya Zaruk Yayata ba ta rasa masoya ba, girman kanta ne ya rasa masoyan nata su tarke ta. Ka sani kuma ba ta da kirki kamar ba ‘yar gidan nan ba”.
“Ki bar ni da ita, ni ne nan zan yi mata miji, kuma ko ba ta so zan sa ta aure…”
Zumbur! Kamar wadda aka tsikara, “Yayana!”
“Na’am, qanwas?”
Ta gyara zama cikin muryar raxa, “Ashe kenan za ka iya taimaka mini na yi wa Yaya Aazeen miji?”
“Kina nufin ke za ki samo mata wanda za ta aura? To ta ya ya?”
“Mun haxu da shi ne ta sanadiyyar sava lamba, sau tari ina karvar wayar Yaya Aazeen na yi game ko na kira qawayena. Rannan na karvi wayar na sanya lambar qawata Hasina, ina kira aka xauki wayar, maimakon in ji muryarta sai na ji muryar namiji. Da farko na zaci yayanta ne, na ce da shi ina neman Hasina, sai ya ce ba ta nan. Hasina qawata ce sosai, sun tashi sun koma Lagos, na daxe ina neman layinta tun daga ranar na dinga bibiyar layin mutumin, ya iya magana, ba shi da wulaqanci, yana da tsananin haquri”.
Kawai Zaruk ya dinga binta da kallo.
“Mutumin da ba ki sani ba, ta ya ya ki ka iya xorar da halayyarsa?”
“Saboda a lokacin da na fahimci raina min hankali yake yi raina ya vaci, na kasa tanqwara zuciyata, na yi ta jifarsa da magana”.
Zaruk ya watsa mata harara.
“Ke xin har wani iya magana ki ka yi? Yaushe ne ma ki ka koyi magana?”
“Allah da gaske nake yi, ita magana zuwa ta ke yi. Ya ci gaba da haxiye duk wasu kalamaina, sannu a hankali muka fara sabawa da shi, idan ban kira shi ba na kan dinga jin kamar na rasa wani abu muhimmi. Bana son a ce zumuncinmu ya sha ruwa, ina ji a jikina yayata za ta so shi da zarar sun haxu sai dai idan na tuna ba shi ne irin mijin da ta ke mafarkin samu ba, ina jin tsoro, domin na fahimci shi xin ba wani mai qarfi ba ne”.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 8*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
“Ke nake saurare Nurat, ba komai ki yi magana kin ji”.
Kawai Nurat ta yi qasa da kanta.
“Ummi ta ce, duk lokacin da na bari namiji ya tava min hannu zan samu ciki in haifi shege, idan na haifi shege mutuwa za ta yi, kuma su… su… sun tavan hannu…”
Ta qarasa cikin saka gursheqen kuka.
Deedat ya harba cikin tunani, gaba xaya jikinsa ya hau tsuma, wani irin tsoro ya ziyarci zuciyarsa tare da wani irin abu wanda ya kasa tantance ko me ye.
“Amma wannan zancen banza ne ta ya za a xora ki a kan wan…”
Deedat ya yi saurin dakatar da Malama Aisha, “Haka ne, Ammi ta yi gaskiya, ai na ga hannunsu bai tava naki ba sosai, yanzu za mu je asibiti in har da cikin za su gaya mana. Ki daina kuka kin ji ko”.
“Ina jin tsoro, za ta gane hakan ta faru, bana son na samu shege kowa zai tsane ni, bana son samun xan da ba shi da tsarki”.
Ba ya son jin kalamanta, da sauri ya yi waje, idanuwa sun sake rinewa, “Za mu je asibiti”. Ya faxa lokacin da ya bar ofis xin.
A can harabar makarantar Doctor Salim amininsa ya kira inda a taqaice ya ba shi labarin abin da ke faruwa, tare da sanar da shi ga shi nan tafe, yana kuma son a yi mata duk abin da zai sa ta samu nutsuwa. Ya yi saurin katse wayar daidai lokacin da Principal ya yi parking xin mota a gabanshi. A can baya ya hangi Nurat gidan gaba ya shiga, yana gano yadda hawaye suke faman tsinkowa daga idanun Nurat. Ya yi saurin kawar da ido, yayin da gabansa ya dinga dukan uku-uku, yarinya ce qarama, sai dai akwai ta da kwarjini. Lokaci-lokaci ya dinga satar kallonta har suka isa asibitin.
Abin da ya bai wa Nurat mamaki, yadda sunan makarantar da na asibitin suka zamo xaya.
Dr. Samir sun tsara komai da Nurse kafin su qaraso, sirinji ya xauka ya yi umarnin da ta miqo hannunta zai xauki jini domin gwaji. Nan fa idanunta suka yo waje, ji ta ke kamar ta sa gudu, sai ga wasu sababbin hawayen.
Dr. Samir babu wani abin da za a yi, maimakon xaukar jinin?” Deedat ya faxa.
“Dole dai sai dai jinin”.
Babu yadda ta iya haka ta runtse ido, ya shiga shirin zuqo jinin, inda Deedat ya xauko wayarsa a fakaice ya shiga xaukarta ta yadda babu mai lura da abin da yake yi.
Bayan an gama Nurse ta yi wani xaki da jinin, sun zauna sai ga sakamako ta shigo da shi. Ta miqa wa Dr. Salim, ya duba cikin gintse dariya a ciki, saboda yadda ya ga alamun tsoro qarara a idanun Nurat, sai da ya xan yi ‘yan rubuce-rubuce sannan ya sake xago kai cikin dubanta. Idanun nan sun yi luhu-luhu saboda kuka, tana jin kamar ta matsi bakinsa ya yi magana, Deedat kam yana iya jin bugun zuciyarta na tsananta, da yake shi ne a kusa da ita.
“Ina taya ki murna xalibar kirki, ba ki da matsala”.
Cike da farin ciki ta sake wani irin murmushi, dukan kumatunta suka lotsa. Wani irin wushirya mai xaukar hankali suka bayyana. Da sauri Deedat ya shiga xaukarta.
“Doctor na gode”. Ta ce.
Ya miqa mata ambulan, “Doctor na bar maka”.
Ya yi murmushi.
“Ki dai tafi da shi”.
Ta karva.
“Abu na gaba ina son kada wannan maganar ta fita ko a gida kada ki faxa kin ji ko?”
“Insha Allahu babu wanda zai ji”.
Cikin farin xiki ta ke magana.
Deedat ya shiga duniyar tunani, yana tunanin a inda ya san wannan muryar, sai dai duk iya yinsa haka ya haqura.
Sai da Principal ya sanya ta a mota aka maida ita makaranta, sannan ya dawo ofis xin Dr. Samir inda kowa ke faxin albarkacin bakinsa a kan al’amarin Nurat.
“Hakan na da kyau, ban yi tunanin akwai irin waxannan iyaye ba. babu wadda ta burge ni sai mahaifiyarta wacce ta xora ta a wannan turba”. In ji Salim.
Principal ya karve zancen, “Cikin class mate xinta ita ce mafi qanqantar shekaru, ga su nan ganxama-ganxama amma babu wadda ta kai ta qoqari. Qwaqwalwarta tamkar computer, irinsu ake ma laqabi da gifted. Na daxe ban ga yarinya kamarta ba, yadda xalibai da malamai ke qaunarta bai sa ta giggiwa ba, gaba xayanta ma tsoro ne da ita, ba ta shiga cikin mutane sosai. Ba qaramin abu ne zai sa ka ji bakinta a class ba, kullum ka ganta wala’Allah a makaranta ko a gida cikin hijabinta zumbulele kamar mai shirin tafiya masallaci. Su kansu malamai mata in sun zauna hirarta suke babu wanda ya tava kawo qararta’.
Haka ya yi ta bada labarinta, har sai da Deedat ya ji a cikin zuciyarsa babu masaqar tsinke, bai tava jin yadda yake ji game da ita ba a kan wata mace ba, shin me hakan ke nufi? Me ke shirin faruwa da shi?
“Ammi ta ce duk lokacin da na bari namiji ya tava min hannu zan samu cikin shege, idan na samu cikin shege mutuwa za ta yi”.
Sautin muryarta ya dinga yi masa kuwwa a kunne, ya shiga kai-komo, gaba xaya ya kasa samun nutsuwa. Bathroom ya shiga, gaba xayansa ya shige cikin shaya yana jin ko hakan zai saukar masa da nutsuwa. Babu abin da ya ragu, sai ma rikicewa da ya qara yi. Doguwar riga ya saka jallabiya mai yankakken hannu, ya yi zaman dirshan a kan carpet, kuka yake yi kamar qaramin yaro. Ya riqe kai yana juyawa cikin tafin hannunsa.
“Sun cutar da ni, sun cuce ni”.
Wani irin zazzavi mai zafi ya rufe shi har haqoransa na gwaruwa, barci ya sace shi. A can cikin baccin nasa babu abin da yake gani sai fuskar Nurat.
Tana zaune a farfajiyar gidan riqe da littafi a hannu tana karatu. Harxe hannu a qirji yana kallonta yana murmushi, bai qi ya tabbata a haka cikin kallon kyakkyawar fuskarta ba.
Jikinta ne ya ba ta akwai mutum tsaye a kanta, ta xan xago kai suka yi ido biyu. Ta yi saurin kawar da kai tare da faxin, “Zauna mana”.
Ta nuna masa kujera.
“Ban ji shigowarka ba”.
Yana murmushi, “kina zaune har na zo na shige na yi ciki, kin ga ke kam idan kina karatu ba kya ji ba kya gani”.
“Yaya Zaruk mun fa kusa fara jarabawa, ina son in karvi kyaututtuka a gurin Dad da Ammi, har ma da Yayata’.
Ya tafa hannu, “Da kyau yarinya mai wayo. To ki qara da tawa, zan yi miki kyautar da babu wanda zai yi miki irinta”.
Ta yi murmushi, cikin satar kallonsa.
“To, yanzu xan gaya mini kalar kyautar”.
“No, ki dai bari zan ba ki mamaki”.
“Allah ya nuna mana lokacin”.
Ta xan yi shiru tana tunanin wani abu.
“Wannan yarinya akwai magana a bakinki”.
“Yaya Zaruk inda a ce kowa zai riqe kyautarsa a yi mini alqawarin auren Yaya Aazeen, zan fi jin daxin haka fiye da komai”.
“Har yanzu ba ki bar wannan zancen ba? na ce da ke shi aure lokaci ne da zarar lokacin ya zo komai zai zamo labari”.
“Amma Yaya Zaruk Yayata ba ta rasa masoya ba, girman kanta ne ya rasa masoyan nata su tarke ta. Ka sani kuma ba ta da kirki kamar ba ‘yar gidan nan ba”.
“Ki bar ni da ita, ni ne nan zan yi mata miji, kuma ko ba ta so zan sa ta aure…”
Zumbur! Kamar wadda aka tsikara, “Yayana!”
“Na’am, qanwas?”
Ta gyara zama cikin muryar raxa, “Ashe kenan za ka iya taimaka mini na yi wa Yaya Aazeen miji?”
“Kina nufin ke za ki samo mata wanda za ta aura? To ta ya ya?”
“Mun haxu da shi ne ta sanadiyyar sava lamba, sau tari ina karvar wayar Yaya Aazeen na yi game ko na kira qawayena. Rannan na karvi wayar na sanya lambar qawata Hasina, ina kira aka xauki wayar, maimakon in ji muryarta sai na ji muryar namiji. Da farko na zaci yayanta ne, na ce da shi ina neman Hasina, sai ya ce ba ta nan. Hasina qawata ce sosai, sun tashi sun koma Lagos, na daxe ina neman layinta tun daga ranar na dinga bibiyar layin mutumin, ya iya magana, ba shi da wulaqanci, yana da tsananin haquri”.
Kawai Zaruk ya dinga binta da kallo.
“Mutumin da ba ki sani ba, ta ya ya ki ka iya xorar da halayyarsa?”
“Saboda a lokacin da na fahimci raina min hankali yake yi raina ya vaci, na kasa tanqwara zuciyata, na yi ta jifarsa da magana”.
Zaruk ya watsa mata harara.
“Ke xin har wani iya magana ki ka yi? Yaushe ne ma ki ka koyi magana?”
“Allah da gaske nake yi, ita magana zuwa ta ke yi. Ya ci gaba da haxiye duk wasu kalamaina, sannu a hankali muka fara sabawa da shi, idan ban kira shi ba na kan dinga jin kamar na rasa wani abu muhimmi. Bana son a ce zumuncinmu ya sha ruwa, ina ji a jikina yayata za ta so shi da zarar sun haxu sai dai idan na tuna ba shi ne irin mijin da ta ke mafarkin samu ba, ina jin tsoro, domin na fahimci shi xin ba wani mai qarfi ba ne”.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 8*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```