Sashe 10
Kyautar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
ANNUR INTERNATIONAL SCHOOL makaranta ce wadda ke tashe, ta yi ma makarantu da yawa zarra, sam babu ragon Malamai, duk cikin malaman makarantar da yawancinsu a waje suka yi karatunsu, haka yawancin xaliban ciki Deedat na daukar nauyinsu su fita karatu waje, kudin makarantar bai cika tsada ba, sai dai duk da haka masu hannu da shuni suna barin tsadaddun makarantu su kawo su wannan, saboda karatun da ake yi a cikinta. Wannan makaranta sunanta ya kewaye gida da waje, ba wani ne mamallakin Annur International School ba face Ahmad Deedat.
karfe bakwai da rabi Deedat ya isa makarantar kamar yadda Maigadi ya sani, shi din abokin principal ne, gurinsa yake zuwa don haka yana yin parking din Lipan maigadi ya karasa gare shi yana yi masa sannu da zuwa.
“Ai kuwa Principal yanzun nan ya fita, sai dai na san ba nisa ya yi ba”. Maigadi ya fada.
“Okey bari na jira shi”.
“Ko a kawo maka abin zama?”
“A’a kada ka damu”.
Ya koma bakin aikinsa, shi kuma Deedat ya koma gindin wata bishiya ya tsaya yana kallon daliban da ke shigowa. Hankalinsa ya kai ga Nurat wadda ke ta faman sauri hade da waiwaye, abin da ya ja hankalinsa ke nan, ya san duban abin da ta ke waiwaye. Idanunsa suka kai ga wasu samari. Da alama ita suke bi.
“Na gaya maka in dai Nurat ce kun yi kun gama ba ‘yar hannu ba ce. Ita muguwar bagidajiya ce, sam ba ta waye ba saboda gidadanci, ko ‘yar kwalliyar nan ba ta yi”.
“Na ce ku sanya min ido duk gidadancinta sai na wayar da ita, zan ba ku mamaki, ni ne fa, kwana uku kawai za ku ba ni duk abin da ta ke takama da shi sai na sauke mata shi, na yi alkawari sai na sauya mata tunani”.
Gaba daya suka sa shewa.
Ya kasa gaskata abin da iska ya debo wa kunnuwansa. Ras! Ras!! Ya ji gabansa na bugawa, hankalinsa ya yi mugun tashi. Yana son gano yaran sai dai ya kasa tantance su. Tuni suka bace ma ganinsa, daga can nesa ya sake hangensu sun sha gabanta yana kallo ta ja da baya, ta kuma fada wani ajin, su kuma suka dauki wata hanyar.
“Ta ya ya aka samu irin wadannan yaran a cikin makarantar nan? Wannan babban kuskure ne, ba za mu laminci haka ba, duk inda yaran nan suke dole ne a zakulo su, ba za su bata mana sunan makaranta ba. Ba zai yiwu ba, wannan ba abu ne wanda za a bari ya wuce ba”.
Duk yadda suke da Principal, wato Zaid bai iya daga masa kafa ba. hankalin Zaid ya yi matukar tashi.
“Dole ne za mu nemo su, za mu je ajin da yarinyar ta shiga, hakan zai taimaka mu gano su”.
Karfe goma sha daya aka fito break, haka ne ya ba wa Deedat da Principal damar zaga ajujuwan don ganin abubuwan da suke buqatar gyara ko sakewa.
A can aji Nurat na zaune tana nazarin littafinta na English, Faisal Nura da Abdul suka kutso kai cikin ajin. Ba ta yi aune ba ji ta yi kawai an wafce littafin, a tsorace ta dago kai lokacin da ta lura da su ne jikinta ya hau bari.
“Ke ba ki ji ba, magana fa ake yi miki’.
Tamkar ba da ita suke ba, hakan ne ya sa su gaba daya suka katange ta, babu ta inda za ta iya guduwa. Faisal ya sa hannu yana shafar kuncinta, kawai ta naxe hannayenta cikin hijabi ta kuma runtse ido, kwalla suka soma tsinkawa a idanunta.
“Me ye a hannun naki da ki ke boyewa?” Abdul ya fada.
“Ni kuma sai na sumbaci hannun”. In ji Faisal.
“Don Allah ku yi hakuri”.
Hakan bai sa sun fasa kudirinsu ba, Faisal ya kai hannu ya damko hannunta. Ta qwalla ihun kuka, daidai lokacin Principal da Deedat suka kunno kai. Da sauri ya saki hannun, gaba daya suka yi tsuru-tsuru.
Wata uwar tsawa Principal ya daka musu, ta sake rushewa da kuka, Principal ya yi matukar tsorata a yadda ya ga kamannin Deedat sun sauya.
“Ina iyakacin kokarina ban san ta ya ya ake samun irin haka ba. ban taba cin karo da wannan matsalar ba, dole ne ku cancanci hukunci mai tsauri. Sai kun gwammace ba ku taba yin makaranta ba”.
Deedat hankalinsa na ga Nurat, tabbas ita ce yarinyar dazu, duk ya ji tausayinta.
Principal ya kira Displine master a waya, ba a wuce minti biyu ba sai ga shi. Ya umarce shi da ya yi ofis da su ya yi musu horon da ba a taba yi wa wani dalibi ba. daga nan ya sanar da assambly din gaggawa. A nan ma a hukunta su, daga nan a kore su ga iyayensu, kora na har abada.
su faisal sun cika samari amma hakan bai hana su kokawa ba, tare da ban haquri, musamman yadda suka rigaya suka san muguntar Displine master a lafiya ma yana mugunta ballantana wannan ganga-gangan laifin. Yau ne karo na farko da suka taba yin da na sani a irin kura-kuran da suke tafkawa, shi kam deedat duk hakan bai burge shi ba, ya fusata sosai, inda ya danganta laifin ga Principal.
Fuu! Ya yi waje, da sauri ya rufa masa baya cike da zullumi.
Can cikin ofis Deedat ya rikicewa Principal, ta inda yake tuhumarsa. Rantsuwa ya dinga yi yana yi masa magiya da ban hakuri, gaba daya ya gama jikewa sharkaf da gumi.
“Dole ne ka zamo jajirtacce, na tsorata da al’amarin nan, idan ita yarinyar ta sanar wa da iyayenta da me za mu kare kanmu? Wannan sakacin zai iya janyowa a rufe makarantar baki daya, ka sani rufewar ba zai dame ni ba, kamar yadda talakawan da suke mora za su dame ni”.
Cikin muryar lallashi Principal ke fadin, “Zan sanya idanu, hakan ba zai sake faruwa ba”.
Malama Aisha ce ta turo kai, inda ya umarce ta da ta kira Nurat. Shi kam Deedat ya shiga kai-komo, al’amarin ya gigita shi. Shesshekar Nurat ya tabbatar masa da sun karaso.
“Principal me ke faruwa da Nurat haka, na ga yarinyar ta shiga rudani da yawa”.
Principal ya dubi Nurat.
“Ko dai sun yi miki wani abin ne bayan abin da idanunmu suka gane mana?”
Fir! Ta ki magana.
“Ita ya kamata ta jata ta tambaye ta”. Deedat ya fada, kamar ya san halinta, Nurat akwai kunya. Principal ya dan ja ta gefe ya shaida mata abin da ya faru. Malama Aisha ta nufi ofis dinsu da ita, inda ta dinga tambayarta cikin dubara.
Da kyar ta iya budar baki cikin shesshekar kuka.
“Ammina ta ce duk lokacin da na bari namiji ya taba mini hannu, ciki zan samu, in…”
Daidai lokacin Principal da Deedat suka kutso kai cikin ofis din nata. Deedat ya kasa jurewa shi ya sa ya azalzali da a biyo sahu. Ganinsu ya sa Nurat tsuke baki.
“Ke nake saurare Nurat, ba komai ki yi magana kin ji”.
Kawai Nurat ta yi kasa da kanta.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 7*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*
karfe bakwai da rabi Deedat ya isa makarantar kamar yadda Maigadi ya sani, shi din abokin principal ne, gurinsa yake zuwa don haka yana yin parking din Lipan maigadi ya karasa gare shi yana yi masa sannu da zuwa.
“Ai kuwa Principal yanzun nan ya fita, sai dai na san ba nisa ya yi ba”. Maigadi ya fada.
“Okey bari na jira shi”.
“Ko a kawo maka abin zama?”
“A’a kada ka damu”.
Ya koma bakin aikinsa, shi kuma Deedat ya koma gindin wata bishiya ya tsaya yana kallon daliban da ke shigowa. Hankalinsa ya kai ga Nurat wadda ke ta faman sauri hade da waiwaye, abin da ya ja hankalinsa ke nan, ya san duban abin da ta ke waiwaye. Idanunsa suka kai ga wasu samari. Da alama ita suke bi.
“Na gaya maka in dai Nurat ce kun yi kun gama ba ‘yar hannu ba ce. Ita muguwar bagidajiya ce, sam ba ta waye ba saboda gidadanci, ko ‘yar kwalliyar nan ba ta yi”.
“Na ce ku sanya min ido duk gidadancinta sai na wayar da ita, zan ba ku mamaki, ni ne fa, kwana uku kawai za ku ba ni duk abin da ta ke takama da shi sai na sauke mata shi, na yi alkawari sai na sauya mata tunani”.
Gaba daya suka sa shewa.
Ya kasa gaskata abin da iska ya debo wa kunnuwansa. Ras! Ras!! Ya ji gabansa na bugawa, hankalinsa ya yi mugun tashi. Yana son gano yaran sai dai ya kasa tantance su. Tuni suka bace ma ganinsa, daga can nesa ya sake hangensu sun sha gabanta yana kallo ta ja da baya, ta kuma fada wani ajin, su kuma suka dauki wata hanyar.
“Ta ya ya aka samu irin wadannan yaran a cikin makarantar nan? Wannan babban kuskure ne, ba za mu laminci haka ba, duk inda yaran nan suke dole ne a zakulo su, ba za su bata mana sunan makaranta ba. Ba zai yiwu ba, wannan ba abu ne wanda za a bari ya wuce ba”.
Duk yadda suke da Principal, wato Zaid bai iya daga masa kafa ba. hankalin Zaid ya yi matukar tashi.
“Dole ne za mu nemo su, za mu je ajin da yarinyar ta shiga, hakan zai taimaka mu gano su”.
Karfe goma sha daya aka fito break, haka ne ya ba wa Deedat da Principal damar zaga ajujuwan don ganin abubuwan da suke buqatar gyara ko sakewa.
A can aji Nurat na zaune tana nazarin littafinta na English, Faisal Nura da Abdul suka kutso kai cikin ajin. Ba ta yi aune ba ji ta yi kawai an wafce littafin, a tsorace ta dago kai lokacin da ta lura da su ne jikinta ya hau bari.
“Ke ba ki ji ba, magana fa ake yi miki’.
Tamkar ba da ita suke ba, hakan ne ya sa su gaba daya suka katange ta, babu ta inda za ta iya guduwa. Faisal ya sa hannu yana shafar kuncinta, kawai ta naxe hannayenta cikin hijabi ta kuma runtse ido, kwalla suka soma tsinkawa a idanunta.
“Me ye a hannun naki da ki ke boyewa?” Abdul ya fada.
“Ni kuma sai na sumbaci hannun”. In ji Faisal.
“Don Allah ku yi hakuri”.
Hakan bai sa sun fasa kudirinsu ba, Faisal ya kai hannu ya damko hannunta. Ta qwalla ihun kuka, daidai lokacin Principal da Deedat suka kunno kai. Da sauri ya saki hannun, gaba daya suka yi tsuru-tsuru.
Wata uwar tsawa Principal ya daka musu, ta sake rushewa da kuka, Principal ya yi matukar tsorata a yadda ya ga kamannin Deedat sun sauya.
“Ina iyakacin kokarina ban san ta ya ya ake samun irin haka ba. ban taba cin karo da wannan matsalar ba, dole ne ku cancanci hukunci mai tsauri. Sai kun gwammace ba ku taba yin makaranta ba”.
Deedat hankalinsa na ga Nurat, tabbas ita ce yarinyar dazu, duk ya ji tausayinta.
Principal ya kira Displine master a waya, ba a wuce minti biyu ba sai ga shi. Ya umarce shi da ya yi ofis da su ya yi musu horon da ba a taba yi wa wani dalibi ba. daga nan ya sanar da assambly din gaggawa. A nan ma a hukunta su, daga nan a kore su ga iyayensu, kora na har abada.
su faisal sun cika samari amma hakan bai hana su kokawa ba, tare da ban haquri, musamman yadda suka rigaya suka san muguntar Displine master a lafiya ma yana mugunta ballantana wannan ganga-gangan laifin. Yau ne karo na farko da suka taba yin da na sani a irin kura-kuran da suke tafkawa, shi kam deedat duk hakan bai burge shi ba, ya fusata sosai, inda ya danganta laifin ga Principal.
Fuu! Ya yi waje, da sauri ya rufa masa baya cike da zullumi.
Can cikin ofis Deedat ya rikicewa Principal, ta inda yake tuhumarsa. Rantsuwa ya dinga yi yana yi masa magiya da ban hakuri, gaba daya ya gama jikewa sharkaf da gumi.
“Dole ne ka zamo jajirtacce, na tsorata da al’amarin nan, idan ita yarinyar ta sanar wa da iyayenta da me za mu kare kanmu? Wannan sakacin zai iya janyowa a rufe makarantar baki daya, ka sani rufewar ba zai dame ni ba, kamar yadda talakawan da suke mora za su dame ni”.
Cikin muryar lallashi Principal ke fadin, “Zan sanya idanu, hakan ba zai sake faruwa ba”.
Malama Aisha ce ta turo kai, inda ya umarce ta da ta kira Nurat. Shi kam Deedat ya shiga kai-komo, al’amarin ya gigita shi. Shesshekar Nurat ya tabbatar masa da sun karaso.
“Principal me ke faruwa da Nurat haka, na ga yarinyar ta shiga rudani da yawa”.
Principal ya dubi Nurat.
“Ko dai sun yi miki wani abin ne bayan abin da idanunmu suka gane mana?”
Fir! Ta ki magana.
“Ita ya kamata ta jata ta tambaye ta”. Deedat ya fada, kamar ya san halinta, Nurat akwai kunya. Principal ya dan ja ta gefe ya shaida mata abin da ya faru. Malama Aisha ta nufi ofis dinsu da ita, inda ta dinga tambayarta cikin dubara.
Da kyar ta iya budar baki cikin shesshekar kuka.
“Ammina ta ce duk lokacin da na bari namiji ya taba mini hannu, ciki zan samu, in…”
Daidai lokacin Principal da Deedat suka kutso kai cikin ofis din nata. Deedat ya kasa jurewa shi ya sa ya azalzali da a biyo sahu. Ganinsu ya sa Nurat tsuke baki.
“Ke nake saurare Nurat, ba komai ki yi magana kin ji”.
Kawai Nurat ta yi kasa da kanta.
*💖💕KYAUTAR ZUCIYA💖💞*
*NA*
*BILKISU H.MUHAMMAD*
_(Matar Auwalu By fos zage)_
*Free page 7*
*_Wanan littafin na kudine akan 300 kacal in kinsan zaki biya don ki fitarmin dashi Dan Allah ki barmin kayana yar uwa_*
*Ga jerin sunayan litattafai na da zaku samu a kasuwa*
*1. IZZATU*
*2. MULKIN MALLAKA*
*3. KAUNA CE*
*4. DACEWA*
*5. RASHIN RABO*
*6.TARAIRAYA*
*7. JINI BIYU*
*8. AKWAI BAMBANCI*
*9. TSALAR KAUNA*
*10. YA YI SAKE*
*11. ILLAR SABO*
*12. SO DA SANKARA*
*13. RASHIN RABO*
*14. WATA RAYUWA*
*15. HUBBAN SHADIDAN*
*16. BAKIN K'AZAFI*
*17. MATSALAR KAUNA*
*18. KYAN KUSKURE*
*19. WA YAFI SONTA?*
*20. GABA DA SO*
_NOW_
*KYAUTA ZUCIYA*
```Duka wanan litattafan sunanan akasuwa zaku sameso a shagunan sai da litattafai inasha Allah```
*_Wanan littafin na kudi ne, Mai bukata karanta shi zai turo 300 ta wanan account number din_*
*_2277439558 UBA Bank_*
Bilkisu H Muhammad_* *_idan an turo sai a turawa wanan number alter 08031307884 domin tabbatar da an turo din idan kuma VTU za'ayi ita dai number za'ai da ita ko katin MTN na 300 din sai in saki a group paid insha Allah_*
*_____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_____________________________________*