Sashe 5
Kyautar Zuciya Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read
Zaruk ta hango da Hajiya Rahma zaune suna cin abinci, ta sakar masa murmushi. Karasawa ta yi ta zauna. Ba a jima ba Alhaji Usman suka shigo da Aazeen rike da ledoji a hannu, su ma joining suka yi zaman cin abincin.
“Yau Rangida babu korafi, da alama abincin ya yi dadi”.
Nurat ta dubi Zaruk ya sakar mata murmushi.
“No Dad, kawai dai ina jin yunwa ne”.
“Da ma ai ke ba a taba iya miki”. Hajiya Rahma ta ce da ita.
“Ladidi ta cancanci tukwici kenan?” In ji Zaruk yana kallon Nurat, ya faki idonsu a hankali ya dinga motsa baki yana nufin zai fada.
Ta yi saurin kada kai tana rokonsa. Mikewa ya yi tsaye.
“Ni zan wuce Ammi, a yi wa kuku godiya sosai”. Ya fada yana murmushi.
ABUJA
“Ummi ya kamata ki saba, na yi tafiya zuwa qasashen waje bila’adadin, na zaga duniya komai bai same ni ba, nan zuwa Kano tafiyar mintina ne, da zarar jirginmu ya sauka shi kenan an wuce gurin. Ko kina tsoro ne kada jirgi ya fado da dan lelenki?”
Deedat ya fada yana kokarin tallafo kuncinta da hannayensa biyu. Ta sauke ajiyar zuciya cikin damuwa.
“Ba haka ba ne, kawai dai ina tsintar kaina cikin rudu duk lokacin da ka ambata cewar za ka Kano. Bana samun nutsuwa, ban san me ya sa haka ba”.
Ya yi murmushi cikin kokarin kwarara mata gwiwa.
“No, Ummina kada ki mance kirarina, in ka san ni ni ne, in ba ka sanni ba, ba ni ba ne. Ummina. Kowa ya san ba ni ba ne, kin ji sam ba ni ba ne babu wanda ya san ni, kuma ma ban da ke da abinki addu’arki fa na tare da ni, ba zan mutu YAUTAR ZUCIYA PAGE 2 3 4
NA BILKISU H MUHD
“Yau Rangida babu korafi, da alama abincin ya yi dadi”.
Nurat ta dubi Zaruk ya sakar mata murmushi.
“No Dad, kawai dai ina jin yunwa ne”.
“Da ma ai ke ba a taba iya miki”. Hajiya Rahma ta ce da ita.
“Ladidi ta cancanci tukwici kenan?” In ji Zaruk yana kallon Nurat, ya faki idonsu a hankali ya dinga motsa baki yana nufin zai fada.
Ta yi saurin kada kai tana rokonsa. Mikewa ya yi tsaye.
“Ni zan wuce Ammi, a yi wa kuku godiya sosai”. Ya fada yana murmushi.
ABUJA
“Ummi ya kamata ki saba, na yi tafiya zuwa qasashen waje bila’adadin, na zaga duniya komai bai same ni ba, nan zuwa Kano tafiyar mintina ne, da zarar jirginmu ya sauka shi kenan an wuce gurin. Ko kina tsoro ne kada jirgi ya fado da dan lelenki?”
Deedat ya fada yana kokarin tallafo kuncinta da hannayensa biyu. Ta sauke ajiyar zuciya cikin damuwa.
“Ba haka ba ne, kawai dai ina tsintar kaina cikin rudu duk lokacin da ka ambata cewar za ka Kano. Bana samun nutsuwa, ban san me ya sa haka ba”.
Ya yi murmushi cikin kokarin kwarara mata gwiwa.
“No, Ummina kada ki mance kirarina, in ka san ni ni ne, in ba ka sanni ba, ba ni ba ne. Ummina. Kowa ya san ba ni ba ne, kin ji sam ba ni ba ne babu wanda ya san ni, kuma ma ban da ke da abinki addu’arki fa na tare da ni, ba zan mutu YAUTAR ZUCIYA PAGE 2 3 4
NA BILKISU H MUHD