← Book details Jinin Abba Na Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 23

Sashe 23

Jinin Abba Na Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Harun ne yafara bawa Basma labarin Sumaiya , tad'anji kishi amma tunda ba shi ta aura ba ai shikenan , da isarsu gida aka bud'e musu get d'in , Basma ta gaji da zama a mota hakan yasata saukowa da k'yar , dariya Harun yake mata yana tsokanar ta , suna shiga parlor suka yada zango , Harun yashiga yimata tausa tana k'ara narkewa ."

*********************
Kwanci tashi babu wuya a gurin Allah .

Abubuwa sun faru da dama na rayuwa , ciki harda aihuwar Sumaiya , dakuma auran Bash yau satinsa d'aya , da auran Asma'u da Haidar , abin guwanin birgewa , kowane gida na cikin k'oshin lpy ."

Sumaiya ta haifi yaro namiji gatan da ake nunawa yaron ba'a magana , Allah sarki rayuwa kowa ya rasa iyaye yayi kuka , Khalid baiso Ammi ta d'auki , Sumaiya ba , itako Ammi ganin rawar kan tayi yawa yasata d'auke Sumaiya ."

Cikin Basma watanshi tara da kwana goma , tun lokacin da tayi zazza6i Hajiya ta d'aukota ta dawo gabansu , sam Harun baiji dad'in hakan ba , ko gurinta zashi , suna ganinshi , zasu fara tuhumarshi shiko ya tsani wanan lamarin shida matarsa amma ana yimasa haka."
Kulum cikin sa rai da aihuwa suke amma cikin ikon Allah shiru babu labari , ranar cikin yana wata tara da kwana goma sha d'aya , su Hajiya sukaje gidan wata rasuwa da akayi musu , akabar Basma dame aiki , Harun ne ya shigo sad'af sad'af ya wuce bedroom d'in kusada na Hajiya , kasancewar anan d'akin Basma take , tura k'ofar yayi a hankali , idanta biyu suka had'a ido dashi dariya tasa tace ”sai na fad'awa Hajiya , kafin ta gama magana ya had'e bakinsu guri d'aya , itama ta biye masa sukaci gaba , dawowa parlor nayi dan in huta kafin anjima na koma lol , bayan 30mints Basma ta fita haiyacinta ,Harun kamar wani zaki idanunsa sun rufe babu batun tausayi , saida yaji ta k'wala k'ara ya d'auketa da sauri ya kaita toilet , babu abinda zata iyayi , sbda hanunta na kan mararta tana kuka , wanka yayi mata tare da goge mata jiki ya sanya mata kayan da tacire yanzu , gudun kar azo a ga canji kuma a zargi ya shiga d'akin , shima wankan yayi ya dawo kusa da ita , abu kamar wasa ya zamo gaske , Basma ta koma abin tausayi a ciwon mara da baya daya sata gaba,

Sallamar su Hajiya ce tasa gaban Harun fad'uwa , Hajiya na shigowa gidan kai tsaye d'akin Basma ta nufa , ganinta kwance ,Harun nayi mata sannu yanayinshi duk sun sauya , bansan meta gani har ta gane , Harun ne silar ciwon ba , masifa tashiga yi tana cewa kai bakada tausayi ne ?"kasheta kakeso kayi ?"gashinan kaje ka tsonano mata nak'uda , sai ka fitoda mota muje adibiti , cikin rawa jiki Harun ya fito da mota aka rik'o Basma aka sata a ciki tare da kayan aihuwa Hajiya ta shiga mom dama bata dawoba suka nufi hospital, da isarsu aka wuce da ita labour room , su Hajiya nata adu'a , temakon gaggawa suka shiga bata kasancewarsu musulmai harda adu'oi suma sukayi , Hajiya dake zaune a bakin k'ofar d'akin , ta jiyo kukan jinjiri , da sauri ta fad'a d'akin , ana gyara d'aya akaga Basma na sabuwar nakuda , haka Allah cikin ikonsa takuma sam6alo mace ”mai kamada babanta , duk yaran kamar Harun suka d'auko ana gama gyrasu aka nad'esu , zuwa anjima kad'an aka yimusu wanka itama aka d'aurayeta , kai masha Allah , tunda garau take babu rashin lpy yasa doctors sallamar ta,

Gida ya cika da farinciki sosai , An sanarwa kowa na dangi , Bash kuwa kamar jira suke sai gashi da matarshi , mom bakinan yak'i rufuwa , haka momy ma cikin farinciki tazo , Sumaiya ma tazo kai aihuwa dai masha Allah yara sunfito cikin dangi mai kyau ."

Beauty bata k'ara dawowa ba , dan haka farinciki da zumunci dakuma had'in kai da kwanciyar hankali ya wsnzu a tsakaninsu .

ALHAMDULILH👏.

Allah nagode maka daka bani ikon kammala wanan littafi hak'ik'a masoya kunyi rawar gani gurin nunamin k'auna Allah yabar zumunci Allah kasa abubuwan dake ciki zasu amfani al Umma amen.

Ga masu buk'atar sabon littafina mai fitowa a 10.....3.....2021 zaku iya tun tu6ar wanan number 👇
08141799224

Please inba maganar book zakiyi ba karki yimin mgna 👏

FATAN ALKAIRI.
Chapter 23 · 0% Book details