Sashe 24
Dingishin Kwado Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
11
Deenah cakes and more -Kano
09038055790
IG @Deenah cakes and more
Snacks such as :
Birthday cakes
Cupcakes
Samosa
Springrolls
Meatpie
Frozen snacks
Event snacks
*Lafazi writer's*
Jiki na bari na amsa kiran. Ba wani karkasashi ya ce "Na ga tarin missed call dinki, hidima ta sha kaina ban samu sukunin kiranki back ba".
Na yi sororo da waya a hannuna. Domin a yadda na dauka babu hudimar da zata hana ya nemi ji daga gare ni, mussaman wayar dare da ta zame mana kaida.
Tsawon lokacin ban samu sukunin lalubar kalma ko guda ba.
Ya numfasa ya zarce da ce wa "Bilki so nake ki bani dama na turo a tsayar da maganar aure a tsakaninmu. Don so nake yi, na takaitawa kaina zullumi da fargabar rasa ki".
Gabana ya takarkara ya fadi. Aure kuma? Ban ci karfin karatuna ba, duk yadda nake son Sahal ban hakaito na yi aure a lokacin ba, domin dukkan sisters dinmu ba a aurar da su ba sai da suka kammala digiri. Ga Yaya Munira ma bata yi a aure ba sai ni?"
Da rawar murya na ce "Aure yanzu?'
Ga mamakina sai kawai ya katse wayar gabadaya. Ba tare da ya ce uffan ba.
Na rike wayar ina kallonta tamkar wacce zata fahimtar da ni dalilin sauyin da nake ga ni a tare da Sahal.
Gabadaya na sake rikicewa, na kasa gane mai yake yi mini dadi a duniyata. Kwanakin biyun da suka biyo baya masu tsauri ne domin gabadaya Sahal ya yi watsi da ni. Na kasa tattauna halin da nake cikin da kowa. Abida ce abokiyar hirar, sai dai ban isa na tunkareta da maganarsa ba. To ban fada mata matsalata da shi ba kullum a cikin yi mini habaci da shaguben son da nake yi masa ya zarce wanda yake yi mini take. Bare yanzu da take mini fushi akan ban so brothers dinta ba.
To ina kuma ga na bude baki na tabbtar mata damuwar da nake kwana na yini a cikinta Sahal ne sababinta.
Cikin rashin karsashi nake hada kayana na komawa makaranta tunda a sati mai zuwa hutunmu zai kare.
Kwanaki biyu ke nan da nutsuwa ta yi mini tutsu sosai a dalilin kullum lamarina da Sahal na sake cakalkalewa. Na gama tunanina nasan ban yi masa komai ba. Haka kuma nasan bamu samu sabanin ra'ayi ba.
Haka siddan matsalakan ya dauki zazzafan fushi da ni, dan kawai yasan zuciyata ta shaku da shi, ta kuma kambaba sha'aninsa.
*Lame.Ng Skin Beauty and wellness*
*Duk masu son sanin mayukan da azsu dace da skin dinsu to A lame skin Beauty and wellness zaku samu.*
*07036662633*
Ranar talata da daddare bayan Abida ta yi barci. Na lallaba na kira wayarsa domin na kai matukar gajiya wajen takura da yanayin da ya jefamu.
Bugu biyu ya dauka murya babu amo ya yi sallama.
Na amsa sai kuma na yi shiru. Na kasa ce wa kanzil.
Murya a dashen ya ce "Me ya hana ki barci Bili?"
Maimakon na amsa sai na jefa masa tambaya na ce "Ni kam mai yake faruwa ne. Tun zuwan da ka yi last gabadaya ka canja mini, na gama iya nazarina ban hango inda muka samu sabani ko na bata maka ba. Amma ina ta ganin changes masu yawa a tare da kai. Tun ina yi maka uzzirin ko yanayin rayuwa ne har na fahimci kawai dan ka ga na damu da kai ne shiyasa zaka yi amfani da hakan wajen gigita nutsuwata!
Na kammala maganata cikin yanayin damuwa ainun.
Ya numfasa ya kaurara murya ya ce *Bilkisu".*
Na kasa amsawa domin ban saba jin ya kama cikakken sunana ba, yafi ce wa Bilki ko Bily.
Ya zarce da fadin "Gaskiyar maganar ban ji dadin wulakanta ni da yayanku ya yi a gidanku ba!
Gabana ya takarkara ya tsinke. Na kasa hakaito wanne a cikin yayan nawa yake batu a kansa?
Ban kai ga ganowa ba ya ce " Bilki tuni na fahimci mafi yawa y'anuwanki basu sona tare da ke. Na gama tunanina ban samu gamshasshen dalilin da zai sa su washe ni irin haka ba. Amma daga ranar da muka yi ido hudu da Asad Funtua na gane shi suke marawa baya, haka nan muzanta ni da ya yi a gabanki ya tabbatar mini da ce wa sonki yake yi, an kuma shirya yaudarata ne shi ya sanya aka karbi iyayena da hannu bibbiyu."
Raina ya baci sosai. Da rawar murya na ce "Wa ya shirya yaudarar naka ni ko iyayena Sahal?"
Jin na harzuka da yawa sai ya yi maza ya sassauta ya ce "Ai idan muna magana a tsakaninmu iya ni da ke ta shafa, babu maganar iyayenmu a ciki don kuwa ba abokan wasanmu bane. Ke kike mini wasa da hankali. Domin yadda kika manta da ni daga isowar yayanki wajen da muke zaune ya tabbatar mini da cewar kema kina sonsa, kinsan kuwa duk yadda iyayenku zasu so ni ba kamar dansu ba ko?"
Na sauke nannauyar ajiyar zuciya na ce "Ba a mini dole akan lamarinka ba, da yawuna ka turo aka tambayar maka izinin neman aurena, menene zai tayar maka hankali akan Yaya Asad?"
Da azama ya ce "Soyayyarki da na ga ni cikin idanuwansa da gangar jikinsa ce ta dame ni".
A tausashe na ce "Indai ba a nawa idanuwan ka ga soyayyarsa ba, ban ga abin damuwa ba, domin kuwa na riga na zabe ka".
Maimakon ya ji dadin kalamaina ya gasgata ni, ya huce. Sai ya numfasa ya ce "Indai nine zabinki to zan turo a yi maganar aurenmu idan ba haka ba, to kuwa sai dai idan hakan ya zama lisisin korata. Ni ba zan iya jure zullumin da nake ciki akan wannan tafkeken dansandan ba".
Na murmusa na ce "Me yasa ka karaya haka? Me yasa ka rasa jarumtar gwarazan maza?"
Murya babu amo ya ce "saboda Baba babba ne ubansa. Kin sani, na sa ni kuma still baba babban ne mai bada aurenki, idan kuwa haka ne ko ban ce komai kin san ína da hujjoji da zasu karya dukkan confidence dina."
Na numfasa na ce "Dukkan sisters dina da aka aurar sai da suka kammala jamia, ni fa yanzu ne na gama shekarar farko ma, ka yarda kai ne zabina".
Ina rufe baki ya ce " Allah ya bamu alheri! Cikin fishi ya furta hakan, sannan ya katse kiran.
Na daure ban kira shi ba . Kwanaki biyu Muna cikin takaddama. Kan dole na hakura na bi ra'ayinsa na amince mu yi auren tunda shine samun masalaaha a tsakaninmu.
Domin gabadaya ya fittitke akan ko dai mu yi auren ko kuma na ya yi gaba ba zai yarda na cigaba da yaudararsa ba.
Bamu koma makaranta ba sai da ya turo aka yi maganar aure tare da kawo dukkan abubuwan da ake yi ja al'ada. A sanya aure watanni hudu masu zuwa wanda ya yi daidai da kammala zangon farko na aji biyu.
Mahaifana duka biyu basu wani so lamarin ba, domin kowa da dalilin da ya hana shi zumudi.
Baba karami so ya yi ace a cikin yayan Baba babba ne zai aure ni, yayin da mami take kuncin ga Munira nan da kammala digiri ba a yi mata aure ba sai ni dan bakar mugunta irin ta Baba babba.
Ni dai na kame bakina ban ce mata komai ba, amma nasan koma menene nice da alhakin komai tunda sai da baba babban ya tambaye ni, na amince Sannan ya basu damar zuwa da maganar aure.
Ansar na zugata, yayin da Yaya Sulaiman ya ce "Mami huce ki daina damuwa dan ta riga Munira da Abida aure ai ba wani abin bane. Kowa da yadda aka tsara masa rayuwarsa, kawai yi hakuri ki bita da addu'ar dacewa". A lokacin ya zo hutu.
Kan dole ta hakura amma ba dan ta so ba.
Murna da zumudi da Sahal ke cikinsu ba zai yiwu na iya hakaitosu ba. Domin gabadaya ya ninka kulawar da yake yi mini, yayin da ni kuma na takura gabadaya na kasa samun nutsuwa a zuciyata. Haka siddan nake jin tamkar na yiwa kaina garaje. Na rasa da wa zan tattauna, na rasa wa zan tunkara ko na samu na fita daga takura da na samu kaina a ciki.
Ana jibi zamu koma makaranta. Da hantsi na ji ana ta kiciniya a harabar gidanmu. Da yake dakinmu na sashen baba babba muna ganin harabar ta taga. Da yake bana iya barci a dalilin nauyin da zuciyata ta yi mini a kwanakin nan. Ya sanya na sauka daga gadona na isa jikin tagar na yaye labulen kadan dan kada haske ya isa ga fuskar Abida ta tashi ta rufar mini da bala'i. Tunda aka saka ranar aurena ta sake botsare mini fiye da kwanakin baya. Ba gaba take yi da ni ba, a a kawai ta sake kamewa daga shiga dukkan shirgina, yana wahalar gaske ta yi mini magana a karan kanta, amma idan na yi mata zata amsa ko da a takaice ne. Haka nan shekaranjiya bayan an kawo kudin aurena.
Ta kalle ni jikinta a sanayaye ta ce "Ina miki fatan alheri a cikin hukuncin da kika yankewa kanki. Ina miki fatan kada ki yi kuka a hannun Sahalu"
Daga haka ta bude littafin Jiki magayi ta hau bitarsa da haka Har barci ya sure ta.
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
11
Deenah cakes and more -Kano
09038055790
IG @Deenah cakes and more
Snacks such as :
Birthday cakes
Cupcakes
Samosa
Springrolls
Meatpie
Frozen snacks
Event snacks
*Lafazi writer's*
Jiki na bari na amsa kiran. Ba wani karkasashi ya ce "Na ga tarin missed call dinki, hidima ta sha kaina ban samu sukunin kiranki back ba".
Na yi sororo da waya a hannuna. Domin a yadda na dauka babu hudimar da zata hana ya nemi ji daga gare ni, mussaman wayar dare da ta zame mana kaida.
Tsawon lokacin ban samu sukunin lalubar kalma ko guda ba.
Ya numfasa ya zarce da ce wa "Bilki so nake ki bani dama na turo a tsayar da maganar aure a tsakaninmu. Don so nake yi, na takaitawa kaina zullumi da fargabar rasa ki".
Gabana ya takarkara ya fadi. Aure kuma? Ban ci karfin karatuna ba, duk yadda nake son Sahal ban hakaito na yi aure a lokacin ba, domin dukkan sisters dinmu ba a aurar da su ba sai da suka kammala digiri. Ga Yaya Munira ma bata yi a aure ba sai ni?"
Da rawar murya na ce "Aure yanzu?'
Ga mamakina sai kawai ya katse wayar gabadaya. Ba tare da ya ce uffan ba.
Na rike wayar ina kallonta tamkar wacce zata fahimtar da ni dalilin sauyin da nake ga ni a tare da Sahal.
Gabadaya na sake rikicewa, na kasa gane mai yake yi mini dadi a duniyata. Kwanakin biyun da suka biyo baya masu tsauri ne domin gabadaya Sahal ya yi watsi da ni. Na kasa tattauna halin da nake cikin da kowa. Abida ce abokiyar hirar, sai dai ban isa na tunkareta da maganarsa ba. To ban fada mata matsalata da shi ba kullum a cikin yi mini habaci da shaguben son da nake yi masa ya zarce wanda yake yi mini take. Bare yanzu da take mini fushi akan ban so brothers dinta ba.
To ina kuma ga na bude baki na tabbtar mata damuwar da nake kwana na yini a cikinta Sahal ne sababinta.
Cikin rashin karsashi nake hada kayana na komawa makaranta tunda a sati mai zuwa hutunmu zai kare.
Kwanaki biyu ke nan da nutsuwa ta yi mini tutsu sosai a dalilin kullum lamarina da Sahal na sake cakalkalewa. Na gama tunanina nasan ban yi masa komai ba. Haka kuma nasan bamu samu sabanin ra'ayi ba.
Haka siddan matsalakan ya dauki zazzafan fushi da ni, dan kawai yasan zuciyata ta shaku da shi, ta kuma kambaba sha'aninsa.
*Lame.Ng Skin Beauty and wellness*
*Duk masu son sanin mayukan da azsu dace da skin dinsu to A lame skin Beauty and wellness zaku samu.*
*07036662633*
Ranar talata da daddare bayan Abida ta yi barci. Na lallaba na kira wayarsa domin na kai matukar gajiya wajen takura da yanayin da ya jefamu.
Bugu biyu ya dauka murya babu amo ya yi sallama.
Na amsa sai kuma na yi shiru. Na kasa ce wa kanzil.
Murya a dashen ya ce "Me ya hana ki barci Bili?"
Maimakon na amsa sai na jefa masa tambaya na ce "Ni kam mai yake faruwa ne. Tun zuwan da ka yi last gabadaya ka canja mini, na gama iya nazarina ban hango inda muka samu sabani ko na bata maka ba. Amma ina ta ganin changes masu yawa a tare da kai. Tun ina yi maka uzzirin ko yanayin rayuwa ne har na fahimci kawai dan ka ga na damu da kai ne shiyasa zaka yi amfani da hakan wajen gigita nutsuwata!
Na kammala maganata cikin yanayin damuwa ainun.
Ya numfasa ya kaurara murya ya ce *Bilkisu".*
Na kasa amsawa domin ban saba jin ya kama cikakken sunana ba, yafi ce wa Bilki ko Bily.
Ya zarce da fadin "Gaskiyar maganar ban ji dadin wulakanta ni da yayanku ya yi a gidanku ba!
Gabana ya takarkara ya tsinke. Na kasa hakaito wanne a cikin yayan nawa yake batu a kansa?
Ban kai ga ganowa ba ya ce " Bilki tuni na fahimci mafi yawa y'anuwanki basu sona tare da ke. Na gama tunanina ban samu gamshasshen dalilin da zai sa su washe ni irin haka ba. Amma daga ranar da muka yi ido hudu da Asad Funtua na gane shi suke marawa baya, haka nan muzanta ni da ya yi a gabanki ya tabbatar mini da ce wa sonki yake yi, an kuma shirya yaudarata ne shi ya sanya aka karbi iyayena da hannu bibbiyu."
Raina ya baci sosai. Da rawar murya na ce "Wa ya shirya yaudarar naka ni ko iyayena Sahal?"
Jin na harzuka da yawa sai ya yi maza ya sassauta ya ce "Ai idan muna magana a tsakaninmu iya ni da ke ta shafa, babu maganar iyayenmu a ciki don kuwa ba abokan wasanmu bane. Ke kike mini wasa da hankali. Domin yadda kika manta da ni daga isowar yayanki wajen da muke zaune ya tabbatar mini da cewar kema kina sonsa, kinsan kuwa duk yadda iyayenku zasu so ni ba kamar dansu ba ko?"
Na sauke nannauyar ajiyar zuciya na ce "Ba a mini dole akan lamarinka ba, da yawuna ka turo aka tambayar maka izinin neman aurena, menene zai tayar maka hankali akan Yaya Asad?"
Da azama ya ce "Soyayyarki da na ga ni cikin idanuwansa da gangar jikinsa ce ta dame ni".
A tausashe na ce "Indai ba a nawa idanuwan ka ga soyayyarsa ba, ban ga abin damuwa ba, domin kuwa na riga na zabe ka".
Maimakon ya ji dadin kalamaina ya gasgata ni, ya huce. Sai ya numfasa ya ce "Indai nine zabinki to zan turo a yi maganar aurenmu idan ba haka ba, to kuwa sai dai idan hakan ya zama lisisin korata. Ni ba zan iya jure zullumin da nake ciki akan wannan tafkeken dansandan ba".
Na murmusa na ce "Me yasa ka karaya haka? Me yasa ka rasa jarumtar gwarazan maza?"
Murya babu amo ya ce "saboda Baba babba ne ubansa. Kin sani, na sa ni kuma still baba babban ne mai bada aurenki, idan kuwa haka ne ko ban ce komai kin san ína da hujjoji da zasu karya dukkan confidence dina."
Na numfasa na ce "Dukkan sisters dina da aka aurar sai da suka kammala jamia, ni fa yanzu ne na gama shekarar farko ma, ka yarda kai ne zabina".
Ina rufe baki ya ce " Allah ya bamu alheri! Cikin fishi ya furta hakan, sannan ya katse kiran.
Na daure ban kira shi ba . Kwanaki biyu Muna cikin takaddama. Kan dole na hakura na bi ra'ayinsa na amince mu yi auren tunda shine samun masalaaha a tsakaninmu.
Domin gabadaya ya fittitke akan ko dai mu yi auren ko kuma na ya yi gaba ba zai yarda na cigaba da yaudararsa ba.
Bamu koma makaranta ba sai da ya turo aka yi maganar aure tare da kawo dukkan abubuwan da ake yi ja al'ada. A sanya aure watanni hudu masu zuwa wanda ya yi daidai da kammala zangon farko na aji biyu.
Mahaifana duka biyu basu wani so lamarin ba, domin kowa da dalilin da ya hana shi zumudi.
Baba karami so ya yi ace a cikin yayan Baba babba ne zai aure ni, yayin da mami take kuncin ga Munira nan da kammala digiri ba a yi mata aure ba sai ni dan bakar mugunta irin ta Baba babba.
Ni dai na kame bakina ban ce mata komai ba, amma nasan koma menene nice da alhakin komai tunda sai da baba babban ya tambaye ni, na amince Sannan ya basu damar zuwa da maganar aure.
Ansar na zugata, yayin da Yaya Sulaiman ya ce "Mami huce ki daina damuwa dan ta riga Munira da Abida aure ai ba wani abin bane. Kowa da yadda aka tsara masa rayuwarsa, kawai yi hakuri ki bita da addu'ar dacewa". A lokacin ya zo hutu.
Kan dole ta hakura amma ba dan ta so ba.
Murna da zumudi da Sahal ke cikinsu ba zai yiwu na iya hakaitosu ba. Domin gabadaya ya ninka kulawar da yake yi mini, yayin da ni kuma na takura gabadaya na kasa samun nutsuwa a zuciyata. Haka siddan nake jin tamkar na yiwa kaina garaje. Na rasa da wa zan tattauna, na rasa wa zan tunkara ko na samu na fita daga takura da na samu kaina a ciki.
Ana jibi zamu koma makaranta. Da hantsi na ji ana ta kiciniya a harabar gidanmu. Da yake dakinmu na sashen baba babba muna ganin harabar ta taga. Da yake bana iya barci a dalilin nauyin da zuciyata ta yi mini a kwanakin nan. Ya sanya na sauka daga gadona na isa jikin tagar na yaye labulen kadan dan kada haske ya isa ga fuskar Abida ta tashi ta rufar mini da bala'i. Tunda aka saka ranar aurena ta sake botsare mini fiye da kwanakin baya. Ba gaba take yi da ni ba, a a kawai ta sake kamewa daga shiga dukkan shirgina, yana wahalar gaske ta yi mini magana a karan kanta, amma idan na yi mata zata amsa ko da a takaice ne. Haka nan shekaranjiya bayan an kawo kudin aurena.
Ta kalle ni jikinta a sanayaye ta ce "Ina miki fatan alheri a cikin hukuncin da kika yankewa kanki. Ina miki fatan kada ki yi kuka a hannun Sahalu"
Daga haka ta bude littafin Jiki magayi ta hau bitarsa da haka Har barci ya sure ta.