← Book details Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 68

Sashe 68

Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

"Istimna'i abu ne mai hatsari ga lafiyar mutum, sannan ƙololuwar zunubi a wurin Allah da addininmu na Musulunci. Saboda ko babu laifi a cikinsa yana haifar da matsalolin da za su zamo barazana ga lafiyar mai yin sa. Bayan ɓangaren wasu cututtukan, da kan iya zama barazanar da za ta shafi lafiyarsa da imaninsa, domin yana rage ƙarfin gani, kuma yana haifar da ƙuncin zuciya da yawan bugun ƙirji da na zuciya. Idan abin ya kama jikin mutum sosai yana haifar masa da taɓin ƙwaƙwalwa. Taɓin ƙwaƙwalwar kuma ba irin ta hauka ko doke-doke ba. A tsaye za a dinga ganin mutum lafiyayyensa amma ba ya aiki irin na masu cikakken hankali. Sannan an yi ittifaƙi a kan duk mai aikata irin wannan ɗabi'ar ta biya wa kai buƙata, musamman namiji; ba zai taɓa zaman aure da matarsa ba. Saboda zai rasa kuzarinsa na mazakutar ɗa namiji gabaɗaya, kuma zai iya komawa tamkar wani mata-maza ba tare da ya sani ba. Domin zai dinga abubuwa irin na mata, wanda idan aka yi rashin sa'a wata macen ma sai ta fi shi kuzari. Saboda ba zai iya ɗaukar lokaci yana saduwa da iyalinsa yadda ake so ba. Dalilin kuwa ya saba wasa da al'aurarsa, mintuna kaɗan ya zubar da ruwansa ya huta. Kuma shi kenan buƙatarsa ta gama biya daga hakan, saɓanin saduwar aure wadda ko ga mai kuzarin gaske sai ya yi da gaske. Domin a lokacin da maniyinsa yake gangar fita, ita kuma macen a lokacin sha'awarta take fara tashi. Shi ya sa masu dabara sai sun tabbatar da gamsuwar matansu; sannan suke zubar da ruwansu saboda gudun cutar da su, ba tare da sun sauke musu nauyin da ke rataye a kawunansu ba."

Shiru na ji Alƙalin ya yi kaina a duƙe, kunya kamar ta kashe ni. Saboda bayanin da yake yi cikin raina; ina jin ina ma ƙasa ta tsage na shige cikinta na ɓoye, saboda muguwar kunyar da ta lulluɓe ni.
Shirun da ya yi, ya bai wa kowa damar tagumi da nazartar maganganunsa. Duba da yanayin fuskokinsu da na saci kallo a fakaice É—aya bayan É—aya.

"Mukhtar ba za ka iya zaman aure da wannan baiwar Allah ba, idan ma kun ci gaba da zama; to kai ma za ka ci gaba da cutar da ita ne kamar yadda ka yi a baya. Don haka kotu za ta sauwaƙe mata, domin gudun ta faɗa halaka ta sanadin wannan ɗabi'ar da ta auri jikinka. Kai ma akwai damar gyara gare ka har yanzu tun da kana da sauran numfashi, saboda duk mai irin wannan halin, daidai yake da masu ɗabi'ar neman jinsi. Ma'ana mace ta nemi 'yar'uwarta mace ko namiji ya nemi ɗan'uwansa namiji, domin su biya wa juna buƙatunsu kuma su kawar wa da juna sha'awa. Kuma Allah da kansa ya tsine wa mai irin wannan halin har sau uku, inda masana sun ce babu wani laifi da bawa yake aikatawa na saɓo a nan doron duniya; wanda Ubangiji ya tsinewa mutum har sau uku jere da juna, sai masu aikata irin wannan ɗabi'ar. Kuma hukuncin neman jinsi ya yi kamanceceniya da biya wa kai buƙata. Wanda ake ɗaukar hannu ko wani abun da za a dinga wasa da azzakari ko farji, domin a biya wa kai buƙata ko kuma a gusar wa da juna sha'awa, ta wannan haramtacciyar hanya abin ƙyama. Saboda ɗabi'a ce irin ta dabbobi, shi kuma ɗan'adam Allah ya bambanta shi da dabba don ya mallaka masa hankalin da bai bai wa dabbobin ba."

Sai da ya numfasa, sannan ya sauke ajiyar zuciya ya sake cewa,
"Abin da kowa ya sani zina saɓon Allah ce, ya saka haramci a cikinta kuma ya ce mu nisance ta. Amma tana da sauƙi a kan wannan mummunar ɗabi'ar ta maɗigo, luwaɗi da biya wa kai buƙata. Kuma duk masu irin wannan halin, suna cikin tsinuwar Allah da mala'ikunsa koyaushe. Sannan muddin suka mutu a cikin wannan halin ba tare da sun tuba ba, to tabbas za su dawwama a cikin wutar jahanna da azaba marar yankewa."

Ƙirjina ya shiga bugawa da sauri da sauri, saboda ni ma wa'azin da tunatarwar da Alƙalin yake yi sun shafe Ni. Domin ɗabi'ar Mukhtar tuni ta yi naso a jikina, duk da ba ta zamar mini jiki kamar shi ba; amma dai Ina aikatawa lokaci bayan lokaci. Idan kuma har haka ne, ni ma ina cikin tsinuwar Allah da mala'ikunsa kamar yadda ya faɗa. Babu shiri hawaye suka dinga fareti a kan fuskata, tare da da-na-sani a kan biye wa ruɗin zuciya da kururuwar shaiɗan. Domin sun saka ni aikata abin da Allah zai yi fushi da ni, bayan kuma ya tsine mini.

Muryar Mukhtar na tsinkayo yana faÉ—in,

"Na gamsu da bayananka duka ranka ya daɗe! Kuma in Sha Allah zan gyara kuskuren da na aikata daga yau. Amma a yi mini haƙuri a yafe mini a janye zancen sakin nan, in Sha Allah daga yanzun nan zan shiga fafutukar neman magani domin na zamo kamar yadda take so!"

Alƙalin ya girgiza kai ya ce,
"Hukuncinku rubuce yake a cikin littafan addinin Musulunci irinsu; Minhajil Muslim, Muwaɗɗa Malik da sauran littafan da suka zo da bayani a kan matsalarku. Saboda Allah ya fi kowa sanin kalolin halittarmu 'yan Adam, dalilin da ya sa kenan aka bai wa mata damar neman wanda ya yi daidai da buƙatarsu. Saboda gudun su faɗa halaka ta sanadin wannan matsala. Saɓanin kai da kake namiji kana da damar auren mace fiye da biyu zuwa uku har huɗu ma. Ita kuma kai kaɗai ne take da shi, idan ba ka cire mata kwaɗayin wasu mazan ba; za ta iya fita waje nemansu ido rufe domin su yi mata abin da take buƙata, Wanda kai ka kasa sauke mata nauyinsa a cikin gidanka. Don haka an bai wa mata damar muddin mijinsu ba ya gamsar da su yadda suke so, ko kuma ba ya iya ɗauke ragamar buƙatuwarsu a duk lokacin da suka nema a wurinsa; su kai kotu a raba auren, domin su je su auri wanda ya yi daidai da halinsu da kuma ra'ayinsu. Saboda tsoron su faɗa halaka a ɓoye ba tare da an sani ba."

"Don Allah ranka ya daÉ—e kada a raba ni da matata wallahi ina son zama da ita!"

Alƙalin ya miƙa hannu tare da nuni a kan a ba shi takarda. Bayan an miƙa masa ya fara rubutu a jikin wata takardar yana cewa,

"Ka yi haƙuri! Idan da rabon za ku sake zama a gaba sai ku daidaita kanku. Saboda ka ci sa'a ba ka yi rantsuwar da na umurce ka da ita ba tun farko, don da a ce ka rantse tana zina ita ma ta rantse a kan ba ta yi; da ko ku kaɗai ne kuka rage a cikin duniyar nan ba za ku sake auren juna ba har abada. Amma yanzu idan har kuna da buƙatar sake zama, za ku iya sasanta kanku daga baya ku daidaita tsakaninku!"

Mukhtar ya fara roƙonsa cikin magiya cikin rawar murya, a kan kada a sake ni yana son zama da ni. Amma Alƙalin bai fasa ɗaga takardar da ya gama rubutawa ba yana faɗin,

_"A yau jumu'a uku ga watan biyar, shekara ta dubu biyu da goma Sha biyar 3/5/2015. Babbar Kotun jaha, ta aminta da miƙa saki ɗaya ga Zaituna Aliyu! Wadda ta zamo mata a wurin Mukhtar Mai Shadda, saboda tauye haƙƙin auratayya a tsakaninsu tsawon shekara huɗu."_

_"Ɗaga sa hannun Alƙali Muhammadu Jaɓɓi Falgore."_

Wani sanyin daɗi ya kwarara tun daga kaina har zuwa tafin ƙafata. Kafin na daidaita natsuwata na ji Alƙali ya kira sunana tare da ba ni umurnin na saka hannu a jikin takardar kotun. Na miƙe jikina yana rawa ina ji tamkar na kifa na karɓi takardar, hannuna yana kyarma na saka hannun a inda ya nuna mini. Sannan ya kira sunan Mukhtar a kan ya zo ya saka nasa hannun, ban juyo ba har sai da na zauna inda na tashi. Sannan na kai kallona inda yake ko gezau bai yi ba balle ya saka hannun kamar yadda aka umurce shi.
Sai da ya maimaita masa maganar sannan ya miƙa takardar ga magatardarsa, shi ya kai masa ita har inda yake sai da ya saka hannun sannan ya mayar wa Alƙalin takardar. Umma da Baba Ali ma duk sai da suka saka hannu sannan aka linke takardar bayan an buga stamp aka ba ni.

Murna har tsakiyar zuciyata, duk da wani gefen zuciyar ina jin kamar ba a kyautawa Mukhtar ɗin ba. Muryarsa na ji tana sarƙewa tamkar mai jinyar da numfashinsa ya yi ƙasa.

"Na yarda da hukuncin Kotu, Amma ina da buƙatar a ba ni yarana duka su dawo hannuna. Zan ci gaba da ɗawainiya da su don daman can ni Allah ya ɗora wa hidimarsu."

Kai-tsaye Alƙalin ya ce,
"An karɓi uzurinka, kuma Kotu ta mayar maka da yaranka a hannunka. Domin ka ci gaba da hidimta musu kamar yadda Musulunci ya shimfiɗa wa kowane uba."

"Ban aminta ba ranka ya daÉ—e!"

Zancen da na yi kenan jikina yana ɓari saboda tsabar tashin hankalin da na shiga. Bayan kaɗuwar da nake ciki a kan zancen Mukhtar ɗin da na Alƙalin duka. Domin sanin da gangan Mukhtar ya yi hakan don ya ƙumsa mini baƙinciki kamar yadda aka yi masa.

"Ki yi haƙuri ya fi ki iko a kan yaransa, duk da ke Musulunci ya bai wa damar riƙon su. Ko da ba kya duniya idan Mahaifiyarki tana raye ita ce a madadinki, a wani ƙaulin ma an ce har sai danginki sun ƙare kaf, sannan za a ba da yaran gare shi ko ga ahalinsa. Amma idan aka yi masa hakan a wannan lokaci an cutar da shi da yawa, duba da yadda aka raba auren yana da kyau a bar shi da yaransa. Domin su dinga ɗebe masa kewar rashin ganin ki a kusa da shi."

Idona a rufe na ce, "To idan har wannan sakin shi zai janyo a raba ni da yarana. Na aminta na yi ta zama a gidansa da aurensa har duniya ta ƙare a haka. Saboda yarana su ne rayuwata kuma su ne komai nawa a cikin duniya, ba zan iya rayuwa babu su ba!"

Yau ake yin ta🤭 uwa da ɗa sai Allah😢

Ƙarshen littafi na ɗaya kenan, idan Allah ya kai mu bayan sallah kuma ya ara mana lokacin. Za mu dawo bakin aiki kamar yadda muka dakata yanzu, in Sha Allah za mu ɗora labarin a inda muka tsaya. D. Auta taku ce kuma tana yi muku son so gabaɗaya😘

Masu neman lambata ga ta; 08022014771 fatan alheri gare ku duka. Bye😍

D.AUTA CE✍🏼
Chapter 68 · 0% Book details