Sashe 28
Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Subhanallah! Abin duka bai yi daÉ—i ba. Gaskiya da bai biye shirmen su ba. Saboda suna yi ne duka don haushin korar da ya yi wa Basirun. Da ya bar su don ko ba komai shi sama yake da su, kuma ya fi su mutunci a idon mutane, bai dace ya biye su girmansa ya zube a banza ba saboda hakan."
"Ni ko sai na ga ya kyauta, saboda sun yi ne kawai don su ci zarafin shi. Amma nuna musu da ya yi ya fi su hauka, hakan zai rage wa iskancinsu kaifi. Don na tabbatar da ba su da kuɗin ɗaukar lauyan da zai ƙaryata abin da Sara ta faɗa a idon mutane."
Sai da na sauke ajiyar zuciya sannan na ce, "Ba za ki gane ba Amina. Wani abin fa kana da ikon ɗaukar mataki kake haƙura, saboda illar da abin zai haifar maka ya fi amfanin shi ya yawa. Domin fallasuwar wannan abin zai taɓa ƙimar MD sosai wallahi, kuma ba zai gano hakan ba har sai an gama shari'ar tsegumi zai fara tashi a tsakanin mutanensa da bai yi tsammani ba. Amma idan ya haƙura ya ƙyale shi kenan komai zai wuce waɗanda suka sani ma za su manta. Saɓanin fallasar da za ta janyo labarin ya fantsama ta yadda goge tarihin zai yi wahala a zukatan mutane."
"Lalle kin fi ni gaskiya Maman Haidar. Don haka ya dace ki yi wannan gudunmawar domin ki datakar da shi ko za a dace ya haƙura ya janye."
Shiru na yi ina nazarin maganar, saboda duk abin da zai haÉ—a ni magana da shi personally ba na so, amma idan aiki ya haÉ—a ko É—ar ba zan ji ba saboda babu yadda zan yi.
"Ba na son duk wani abu da zai haÉ—a ni da shi Amina."
"To ki tura masa saƙo!"
Shiru na yi na ɗan lokaci, sannan na janyo wayata ba don ina so ba na tura masa saƙo kamar haka;
'Ka yi haƙuri ka janye ƙarar da na ji ka saka. Saboda babu alfanu idan sirrin ya fallasu a idon waɗanda ba su san da shi ba. Maimakon kankare laifin, sai ka ƙara ɓanɓaro mana yamaɗiɗin mutane, garin neman gira za a rasa ido. Ba na jin kaina, amma ina jin takaicin ƙimarka ta taɓu ta sanadina.'
Amina na bai wa ta karanta, sannan ta dawo mini da wayar tana faÉ—in.
"Sannu gwanar hikima da azanci. Allah ya ba ki iya tsara magana da hangen nesa. Ina ma kaso mafi rinjaye na mutanen duniya haka suke. Da an samu rangwamen cakwalkwalin cakwakiyar da ya baibaye mutane a wannan lokacin da muke ciki. Ubangiji ya kawo miki mafita a cikin rayuwarki."
Amin Amina. Tare da sauran masu Matsala irin taku da ma wadda ta fi.ðŸ‘ðŸ»
D. AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*ASHIRIN DA ÆŠAYA.*
Mun tattauna sosai da Amina, tana sanar da ni matsalar Basiru mijin Sara. Da irin tataɓurzar da aka yi da su a lokacin da suke ganiyar rashin mutuncinsu. Bayan an tashi muka fito bakin ma'aikatar muka tsaya, da niyyar neman adaidaita amma muka buge da hira.
Amina ta kalli agogon da ke hannunta ta ce da ni, "Yau dai na yi missing ba a tsakura mini komai daga cikin labarin ba. Ga shi na matsu na ji yadda ta kaya a lokacin da kika shiga É—akin, domin ina so na ji me ya ba ki tsoro wanda ya sa kika yi salatin da, har yanzu ban daina jin sautinsa cikin kunnuwana ba."
Baki kawai na riƙe cike da mamakin sharotan da take ƙoƙarin yi, domin kawai ta yi mini daɗin bakin da zai sa na ɗora mata labarin, daga inda na tsaya ban shirya ba. Cike da zolaya na ce da ita,
"To ko za mu tsaya ki ji sauran kanun labarin ne?"
Cikin sauri ta dawo daga bakin titin da ta nufa tana ƙoƙarin tare wani ɗan adaidaitan da zai wuce. "Wallahi in dai za ki ƙarasa mini labarin yanzu, to na yarda mu kai wata safiya a nan ba tare da na ƙosa ba."
"Rufa mini asiri kada ki sa Mama ta zo har wurin nan ta ci ubanmu."
Dariya muka fashe da ita dukanmu, kafin na shammace ta na shige adaidaitan. Da hanzari ta matso inda nake tana faÉ—in, "Ji nake kamar na biyo ki mu je tare wallahi. Domin har ga Allah matse nake da jin labarin nan, kamar na yi tsuntsuwa na dira tsakiyar É—akin domin na ga komai ba sai na jira an sanar da ni ba."
"Ai kuwa dole ki jira har lokacin da za a sanar da ke, don haka mu haÉ—u goben kawai Hajiya ko shi idan da rabon ki. Domin haka kawai ba za ki janyo mini fushin Mama ba. Tsautsayi ya sa a binciko mata inda nake ta ci kwakwata, ni kin ga tafiya ta mu kwana lafiya ki gaishe da my boy."
Daga haka muka tafi muka bar ta a tsaye tana aika mini harara har da ƙwafa. Hakan ya sa ko da muka yi nisa ban rufe bakina daga dariyar da ta ba ni ba, sosai nake tsintar kaina cikin farincikin a duk lokacin da muna tare, domin tana ɗebe mini kewar 'yar uwa macen da na rasa kuma ƙawa makusanciya.
***
Mamaki fal raina a lokacin da na shiga gidan na yi tozali da kayansu Ummu Salma tsibe , na bi kayan da kallo cike da tunanin me ya kawo jakunkunan su a ƙofar ɗakina. Duk da oyoyon da suke mini bai sa na ɗauke kallona daga kan kayan ba.
Da sassarfa na isa bakin ƙofar ɗakinsu ina murɗa handle idona ƙur a kansu, tare neman ba'asin dalilin da ya janyo hakan, tambayar da tun kafin na furta ta fito da kanta cikin ƙwayar idona.
"Mu ma ko da muka dawo mun taras da kayan a wurin. Kuma har yanzu Abbanmu bai dawo ba balle mu ji ko shi ne ya fito mana da su."
Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi sannan na ce, "Ku ɗauko kayan mu je ɗakina, idan ya dawo mu ji me yake nufi."
Da ƙyar na yi maganar saboda hadarin baƙincikin da ya taso ya rufe idona. Guguwar takaici ta sa ban iya ɗaukar komai daga cikin kayan ba. Domin har da katifunsu biyu tasu ita da Iman da ta Haidar.
Sun shigar da kayan duka a lokacin da na kammala sallah, a kan kayan na ɗora idona saboda tunanin abin da yake nufi da abin da ya aikata. A take zuciyata ta hasko mini zallar manufar shi duk da bai faɗa mini ba, duba da kalaman barazanar da ya yi mini a ranar da ya tuna da haƙƙinsa da ke kaina.
'Wallahi duk abin da ya biyo baya kada ki ga laifina. Ba dai kin hana ni haƙƙina ba? To ke kuma ki jira me zai faru cikin kwanan..'
Maganar shi kenan da ta faÉ—o mini rai, kuma ta shiga kunnena tamkar a lokacin yake furta mini ita.
"Waton aure zai yi?"
Tambayar da na jefi kaina da ita kenan a fili, sannan wani murmushi mai sauti ya suɓuce mini ba tare da na shirya ba, saboda tabbacin da zuciyata ta ba ni a kan hasashen da nake yi. Nan take wani sabon kuzari ya ziyarce ni, wanda ya kore rabin damuwar da ya haifar mini a lokacin.
Ummu Salma na ƙwala wa kira, ta shigo ido tsakar ka bayan ta amsa kiran, sallayata na shiga naɗewa ina cewa, "Zo mu saita kayan nan. Kafin lokacin makaranta ya yi."
Da Mamaki ta bi ni da kallo wanda ya nuna tambayar da take son yi mini, ina mata 'yar dariya na ce, "A nan za ku dawo da zama dukanku. Don daman can ina ta so ku dawo nan mu dinga kwana tare. Kafin lokacin da Haidar zai ƙara girman da za a ware masa makwancinsa daban."
Farinciki mayalwaci ya ziyarci fuskarta, ta fara murna tana ƙwala wa su Haidar kira bakinta har kunne, ko da suka shigo ta fesa musu labari suka hau ihu, domin alamunsu ya bayyana jin daɗinsu a kan sabon tsarin da nake ƙoƙarin zartarwa.
Tare da su duka muka gyara ɗakin tsaf komai muka tanadar masa a muhallinsa, duk da katifar Haidar ba ta samu wuri ba dole jingine ta muka yi. Saboda an laƙume ɗan filin ɗakin da katifar su Ummu Salma, sannan da jakunkunan kayansu. Don ma na cire wasu na saka a wardrobe domin a rage tarkacen kayan.
Saboda suna da sutura sosai domin ba na ɗaukar lokaci ban yi musu ba, musamman Haidar da ko kan hanya na zo wucewa na hango yadin da ya burge ni, sai na saka an yanka masa ko da iya kuɗin jakata kenan. Wani kuma idan ban da kuɗin, cewa nake yi a yanka a ajiye mini. Daga baya na dawo na karɓa tun a lokacin da yake cin yadi ɗaya, har yanzu da yake shekara bakwai ya fara laƙume yadi ɗaya da rabi.
Su ma atamfa É—aya nake saya a É—inka musu su biyu, saboda Ummu Salma shekararta goma sha biyu, Iman ce mai shekara tara. Domin tsakaninta da Haidar babu tazara mai yawa, kuma yana da jikin girma, don ya kusa kamo tsawon Iman.
"Ni ko sai na ga ya kyauta, saboda sun yi ne kawai don su ci zarafin shi. Amma nuna musu da ya yi ya fi su hauka, hakan zai rage wa iskancinsu kaifi. Don na tabbatar da ba su da kuɗin ɗaukar lauyan da zai ƙaryata abin da Sara ta faɗa a idon mutane."
Sai da na sauke ajiyar zuciya sannan na ce, "Ba za ki gane ba Amina. Wani abin fa kana da ikon ɗaukar mataki kake haƙura, saboda illar da abin zai haifar maka ya fi amfanin shi ya yawa. Domin fallasuwar wannan abin zai taɓa ƙimar MD sosai wallahi, kuma ba zai gano hakan ba har sai an gama shari'ar tsegumi zai fara tashi a tsakanin mutanensa da bai yi tsammani ba. Amma idan ya haƙura ya ƙyale shi kenan komai zai wuce waɗanda suka sani ma za su manta. Saɓanin fallasar da za ta janyo labarin ya fantsama ta yadda goge tarihin zai yi wahala a zukatan mutane."
"Lalle kin fi ni gaskiya Maman Haidar. Don haka ya dace ki yi wannan gudunmawar domin ki datakar da shi ko za a dace ya haƙura ya janye."
Shiru na yi ina nazarin maganar, saboda duk abin da zai haÉ—a ni magana da shi personally ba na so, amma idan aiki ya haÉ—a ko É—ar ba zan ji ba saboda babu yadda zan yi.
"Ba na son duk wani abu da zai haÉ—a ni da shi Amina."
"To ki tura masa saƙo!"
Shiru na yi na ɗan lokaci, sannan na janyo wayata ba don ina so ba na tura masa saƙo kamar haka;
'Ka yi haƙuri ka janye ƙarar da na ji ka saka. Saboda babu alfanu idan sirrin ya fallasu a idon waɗanda ba su san da shi ba. Maimakon kankare laifin, sai ka ƙara ɓanɓaro mana yamaɗiɗin mutane, garin neman gira za a rasa ido. Ba na jin kaina, amma ina jin takaicin ƙimarka ta taɓu ta sanadina.'
Amina na bai wa ta karanta, sannan ta dawo mini da wayar tana faÉ—in.
"Sannu gwanar hikima da azanci. Allah ya ba ki iya tsara magana da hangen nesa. Ina ma kaso mafi rinjaye na mutanen duniya haka suke. Da an samu rangwamen cakwalkwalin cakwakiyar da ya baibaye mutane a wannan lokacin da muke ciki. Ubangiji ya kawo miki mafita a cikin rayuwarki."
Amin Amina. Tare da sauran masu Matsala irin taku da ma wadda ta fi.ðŸ‘ðŸ»
D. AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*ASHIRIN DA ÆŠAYA.*
Mun tattauna sosai da Amina, tana sanar da ni matsalar Basiru mijin Sara. Da irin tataɓurzar da aka yi da su a lokacin da suke ganiyar rashin mutuncinsu. Bayan an tashi muka fito bakin ma'aikatar muka tsaya, da niyyar neman adaidaita amma muka buge da hira.
Amina ta kalli agogon da ke hannunta ta ce da ni, "Yau dai na yi missing ba a tsakura mini komai daga cikin labarin ba. Ga shi na matsu na ji yadda ta kaya a lokacin da kika shiga É—akin, domin ina so na ji me ya ba ki tsoro wanda ya sa kika yi salatin da, har yanzu ban daina jin sautinsa cikin kunnuwana ba."
Baki kawai na riƙe cike da mamakin sharotan da take ƙoƙarin yi, domin kawai ta yi mini daɗin bakin da zai sa na ɗora mata labarin, daga inda na tsaya ban shirya ba. Cike da zolaya na ce da ita,
"To ko za mu tsaya ki ji sauran kanun labarin ne?"
Cikin sauri ta dawo daga bakin titin da ta nufa tana ƙoƙarin tare wani ɗan adaidaitan da zai wuce. "Wallahi in dai za ki ƙarasa mini labarin yanzu, to na yarda mu kai wata safiya a nan ba tare da na ƙosa ba."
"Rufa mini asiri kada ki sa Mama ta zo har wurin nan ta ci ubanmu."
Dariya muka fashe da ita dukanmu, kafin na shammace ta na shige adaidaitan. Da hanzari ta matso inda nake tana faÉ—in, "Ji nake kamar na biyo ki mu je tare wallahi. Domin har ga Allah matse nake da jin labarin nan, kamar na yi tsuntsuwa na dira tsakiyar É—akin domin na ga komai ba sai na jira an sanar da ni ba."
"Ai kuwa dole ki jira har lokacin da za a sanar da ke, don haka mu haÉ—u goben kawai Hajiya ko shi idan da rabon ki. Domin haka kawai ba za ki janyo mini fushin Mama ba. Tsautsayi ya sa a binciko mata inda nake ta ci kwakwata, ni kin ga tafiya ta mu kwana lafiya ki gaishe da my boy."
Daga haka muka tafi muka bar ta a tsaye tana aika mini harara har da ƙwafa. Hakan ya sa ko da muka yi nisa ban rufe bakina daga dariyar da ta ba ni ba, sosai nake tsintar kaina cikin farincikin a duk lokacin da muna tare, domin tana ɗebe mini kewar 'yar uwa macen da na rasa kuma ƙawa makusanciya.
***
Mamaki fal raina a lokacin da na shiga gidan na yi tozali da kayansu Ummu Salma tsibe , na bi kayan da kallo cike da tunanin me ya kawo jakunkunan su a ƙofar ɗakina. Duk da oyoyon da suke mini bai sa na ɗauke kallona daga kan kayan ba.
Da sassarfa na isa bakin ƙofar ɗakinsu ina murɗa handle idona ƙur a kansu, tare neman ba'asin dalilin da ya janyo hakan, tambayar da tun kafin na furta ta fito da kanta cikin ƙwayar idona.
"Mu ma ko da muka dawo mun taras da kayan a wurin. Kuma har yanzu Abbanmu bai dawo ba balle mu ji ko shi ne ya fito mana da su."
Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi sannan na ce, "Ku ɗauko kayan mu je ɗakina, idan ya dawo mu ji me yake nufi."
Da ƙyar na yi maganar saboda hadarin baƙincikin da ya taso ya rufe idona. Guguwar takaici ta sa ban iya ɗaukar komai daga cikin kayan ba. Domin har da katifunsu biyu tasu ita da Iman da ta Haidar.
Sun shigar da kayan duka a lokacin da na kammala sallah, a kan kayan na ɗora idona saboda tunanin abin da yake nufi da abin da ya aikata. A take zuciyata ta hasko mini zallar manufar shi duk da bai faɗa mini ba, duba da kalaman barazanar da ya yi mini a ranar da ya tuna da haƙƙinsa da ke kaina.
'Wallahi duk abin da ya biyo baya kada ki ga laifina. Ba dai kin hana ni haƙƙina ba? To ke kuma ki jira me zai faru cikin kwanan..'
Maganar shi kenan da ta faÉ—o mini rai, kuma ta shiga kunnena tamkar a lokacin yake furta mini ita.
"Waton aure zai yi?"
Tambayar da na jefi kaina da ita kenan a fili, sannan wani murmushi mai sauti ya suɓuce mini ba tare da na shirya ba, saboda tabbacin da zuciyata ta ba ni a kan hasashen da nake yi. Nan take wani sabon kuzari ya ziyarce ni, wanda ya kore rabin damuwar da ya haifar mini a lokacin.
Ummu Salma na ƙwala wa kira, ta shigo ido tsakar ka bayan ta amsa kiran, sallayata na shiga naɗewa ina cewa, "Zo mu saita kayan nan. Kafin lokacin makaranta ya yi."
Da Mamaki ta bi ni da kallo wanda ya nuna tambayar da take son yi mini, ina mata 'yar dariya na ce, "A nan za ku dawo da zama dukanku. Don daman can ina ta so ku dawo nan mu dinga kwana tare. Kafin lokacin da Haidar zai ƙara girman da za a ware masa makwancinsa daban."
Farinciki mayalwaci ya ziyarci fuskarta, ta fara murna tana ƙwala wa su Haidar kira bakinta har kunne, ko da suka shigo ta fesa musu labari suka hau ihu, domin alamunsu ya bayyana jin daɗinsu a kan sabon tsarin da nake ƙoƙarin zartarwa.
Tare da su duka muka gyara ɗakin tsaf komai muka tanadar masa a muhallinsa, duk da katifar Haidar ba ta samu wuri ba dole jingine ta muka yi. Saboda an laƙume ɗan filin ɗakin da katifar su Ummu Salma, sannan da jakunkunan kayansu. Don ma na cire wasu na saka a wardrobe domin a rage tarkacen kayan.
Saboda suna da sutura sosai domin ba na ɗaukar lokaci ban yi musu ba, musamman Haidar da ko kan hanya na zo wucewa na hango yadin da ya burge ni, sai na saka an yanka masa ko da iya kuɗin jakata kenan. Wani kuma idan ban da kuɗin, cewa nake yi a yanka a ajiye mini. Daga baya na dawo na karɓa tun a lokacin da yake cin yadi ɗaya, har yanzu da yake shekara bakwai ya fara laƙume yadi ɗaya da rabi.
Su ma atamfa É—aya nake saya a É—inka musu su biyu, saboda Ummu Salma shekararta goma sha biyu, Iman ce mai shekara tara. Domin tsakaninta da Haidar babu tazara mai yawa, kuma yana da jikin girma, don ya kusa kamo tsawon Iman.