Sashe 49
Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ok!" Ita ce iya maganar da na yi ya fice na miƙe ina kakkaɓe ƙurar da ta ƙi sakin jikina, sannan na nufi ofishin fuskata a haɗe ƙirjina yana bugawa.
Sallama na yi cikin siririyar murya ya amsa mini a gadarance tamkar ba ya so. Takardu na gani a gansa tsibi guda da hannu ya yi mini nuni da su a kan na É—auka. Harara na wurga wa kwantaccen gashin kansa da ya sha gyara, saboda haushin izzar da yake ji da ita a lokacin.
ÆŠauka na yi kawai ba tare da na ce da shi komai ba na nufi hanyar fita.
"Ya hidimar bikin? Fatan Allah ya ba da zaman lafiya."
"Amin" Kawai na faɗa na fice, tunanin ƙara yi masa godiya ya faɗo mini a rai na koma. Bakin ƙofar na tsaya ina faɗin,
"Na gode sosai a kan kyautar da ka yi mini. Allah ya ƙara rufa asiri."
Bai ce da ni komai ba, har sai da na juya na ji ya ce, "Amin" can cikin maƙoshinsa. Raina a haɗe na fito ina gungunin da ban san me nake ta faɗa ba.
Saboda sauyin da ya yi mini sosai yake taɓa mini zuciya, saɓanin baya da yake faram-faram da ni, duk da ba ya sakewa sosai ina yabon kirkinsa da Amina. Amma tun daga kan abin da Mukhtar ya yi masa ya daina sake mini fuska, musamman lokacin rikici na da su Ummita har tsawa yake daka mini tamkar ya dake ni.
Ban ɓata lokaci ba na fara aikina gadan-gadan, Amina ta shigo muna hira ina aikin har lokacin tashi ya yi. Tare muka miƙa wa MD takardun muka fito tana cewa,
"Wai ina amarya? Na manta ban tambaye ki ba."
"Amarya tana gidan mijinta. Sauri nake yi ma na koma saboda ba na so yaran su yi mata ba daidai ba. Don na fahimci ita ma rawar kanta ya fi ta yawa."
Dariya Amina ta yi sannan ta ce, "Ganin take yi karanta ya kai tsaiko. Tun da ta haÉ—a kishi da mace mai halin kirki da nagarta irin taki. Don wallahi ba don ke ta samu ba; da sai ta gane barno gabas take a yadda na gan ta wata jagwal tamkar sandar makafi."
Ajiyar zuciya na yi ina tare wata adaidaita na ce, "Ki bari kawai! Nan da kike ganin ta ba ba ƙaramar 'yar hannu ba ce."
"A hakan?"
"Tabbas! Ke dai kin ga mutum!"
Da haka na tafi muna ɗaga wa juna hannu. Zuciyata cike da tunanin su Ummu Salma har aka ajiye ni ƙofar gidan. Tun da na jefa ƙafafuwana cikin gidan na fara jin sautin kukan Ummu Salma. Da sassarfa na shiga falon idona a kan Ummu Salmar da ke rakuɓe jikin gini tana cisgar kuka har da shessheka.
'Me nake shirin gani?'
Wata sabuwa🤔 wa ya taɓa mana Ummu Salma ne haka?😢
D. AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*TALATIN DA BIYAR .*
"Lafiya!? Me ya same ki!?"
Abin da na fara faÉ—a kenan a hargitse tun kafin na isa inda take. Tana gani na da ta tarye ni da gudu ta faÉ—a jikina, tare da rushewa da wani sabon kukan ya sa jikina kyarma.
Domin ko ni rabon da na saka hannu na dake ta har na manta, saboda tana ƙoƙarin barin abin da duk ta san ba na so, balle ta yin abin da zan dake ta a kansa. Haidar ne kawai yake shan duka a wurina, don ko Iman miskilancinta kawai yake sa na dake ta idan na saka ta aiki tana jan jiki.
Jikina na ɓanɓare ta ina faɗin, "Faɗa mini me ya faru?" Cikin shesshekar kuka ta ce, "Abbanmu ya dake ni"
"Me kika yi masa?"
Ƙirjina yana bugawa na yi maganar saboda sabon ɓacin ran da ya ziyarci zuciyata.
"Girki na zo zan É—ora amarya ta ce ba zan É—ora shi ba, ni kuma ganin kin ce na yi kafin ki dawo ya sa na ci gaba da yi. Ban san ya aka yi ba ina tsaka da kwasar abincin na ji muryar Abbanmu yana ta zagi na. Shi ne ya same ni a kitchen É—in yana ta dukana, kuma ya É—auke abincin duka ya ce ba za mu ci ba tun da amarya ta yi girki shi kowa zai ci."
"To fa! Abin har ya kai can?"
"Har ya wuce ma! Kuma wallahi matuƙar kika sa ta raina Barcy sai na ci uwarta a cikin gidan nan."
Zancen Mukhtar kenan a sama yana ba ni amsar tambayar da na yi wa kaina cike da mamaki. Na saki hannun Ummu Salma na tarye shi gaba da gaba na ce,
"Sai dai ka ci ubansu waton kai kenan! Don wallahi daga kai har wannan ƙanjamammar amaryar holoƙon da kake tinƙaho da ita; kun yi kaɗan ku ci zarafin yarana ba bisa haƙƙinsu ba. Abinci da ta dafa kuma ni na ba ta umurnin dafawa, saboda ba zan sake zama wata ballagaza tana hora mu da yunwa ba."
"Ke kika ba ta umurni Barcy kuma ta hana ta, saboda tun kafin su dawo gidan ta yi girki. Kuma shi za a ci dole don tuni na kyautar da wanda ta dafa."
Baki a sake nake bin fuskarsa da kallo saboda mamakin zancensa na 'ke kika saka ta Barcy ta hana'.
"Waton ita Barcyn ce za ta dinga ba mu umurnin abin da za mu yi a gidan da wanda za mu bari?"
"E! Saboda ni ce amarya kuma har yanzu ina cikin kwanakin girkina. Ki bari idan girkin ya dawo hannunki ki yi duk abin da kike so babu ruwana. Amma yanzu kam babu wanda zai É—ora girki a cikin gidan nan bayan wanda na dafa."
Martanin Barira kenan tana girgizar jiki tare da riƙe ƙugu. Ta so ba ni dariya amma na fuske na ce,
"Sannu shafaffiya da mai jikar sarauniyar Ingila 'yar gidan Sarki Macciɗo. To na rantse da Allah zan yi bikin watan cin ubanki a cikin gidan nan. Ko ki fita sabga ta da yarana; ko na nuna miki na fi ki sanin makamar iskanci da rashin mutunci. Abincinki kuma wallahi daga ni har yaran ba za mu sake jiransa ba, ke da cin abinci ya kawo gidan ki buɗe ciki ki yi ta zubawa, nawa kaso da na yarana duka mun bar miki. idan kin ƙoshi ki miƙa saura gidanku don na san suna da buƙata."
Baki a sake take kallona tare da cizon yatsa tana faÉ—in,
"Kai kai kai!"
Kansa na juya ina faÉ—in,
"Kai kuma mijin ta ce! Namijin ho-ti-ho! Ɗankwali ya ja hula! To ka sanar da ita babu kwanakin girkin kowa a kaina. Idan ma akwai duka na bar mata don haka ku sake wa 'ya'yana mara su ji daɗin fitsari. Kuma daga yau abincinmu daban za mu dinga girkawa, idan ka ji tsoron Allah ka ba mu namu haƙƙin. Domin ka rage wa kanka guzurin mugun bugun da Mala'iku za su yi maka a ranar lahira. Idan kuma ka bijire kamar yadda ka yi a baya, ina maka albishir za ka girbi duk abin da ka shuka khairan ko sharran. Na zare hannuna a cikin sha'anin girkin matarka, ni ma daga yau babu ruwanta da duk abin da za mu ci ko mu sha, a cikin gidan nan ni da yarana. Saboda ba za mu zauna tana gasa mana aya a hannu ba saboda abinci."
" Ina ƙare faɗar hakan na yi gaba zan shige ɗakina, sannan na yi saurin juyowa ina faɗin,
"Gass nawa ne, ni na saya da kuɗina, repelling ma ni nake yi ba wani yake yi mini ba. Daga yau kada a sake taɓa mini kaya ko da ɗora ruwan zafi ne!"
"Wallahi ni kuma ba zan yi girki da itace ba!"
Abin da Barira ta yi hanzarin faɗi kenan tana murguɗa baki. Saboda Ummu Salma ta faɗa mini ita ce ta nuna mata yadda ake amfani da shi. Lokacin da take girkin tana 'yan waƙe-waƙen farinciki, lokacin da wata ta kira ta a waya baki a sake take faɗin,
'Ke yarinya na wuce nan! Sabod Allah ya kawo ni gidan arziƙi, inda ba zan sha wahalar hura wutar ice ba. Gass cooker Hajiya shi nake girki da shi yanzu haka har na kusa gamawa... Ja can yarinya! Allah dai ya ba ku irin tawa kawai, don ni na tako arziƙi na wuce da sanin ku ƙananun ƙwari.'
Tuno labarin na yi murmushi mai sauti sannan na ce da ita, "Wannan kuma mijinki za ki faÉ—awa ba ni ba!"
"To ni ko idan dai da ice zan dinga girki, sai dai kada kowa ya ci abinci a gidan nan, daga ni har shi wallahi."
"Kanku ake ji!"
Sallama na yi cikin siririyar murya ya amsa mini a gadarance tamkar ba ya so. Takardu na gani a gansa tsibi guda da hannu ya yi mini nuni da su a kan na É—auka. Harara na wurga wa kwantaccen gashin kansa da ya sha gyara, saboda haushin izzar da yake ji da ita a lokacin.
ÆŠauka na yi kawai ba tare da na ce da shi komai ba na nufi hanyar fita.
"Ya hidimar bikin? Fatan Allah ya ba da zaman lafiya."
"Amin" Kawai na faɗa na fice, tunanin ƙara yi masa godiya ya faɗo mini a rai na koma. Bakin ƙofar na tsaya ina faɗin,
"Na gode sosai a kan kyautar da ka yi mini. Allah ya ƙara rufa asiri."
Bai ce da ni komai ba, har sai da na juya na ji ya ce, "Amin" can cikin maƙoshinsa. Raina a haɗe na fito ina gungunin da ban san me nake ta faɗa ba.
Saboda sauyin da ya yi mini sosai yake taɓa mini zuciya, saɓanin baya da yake faram-faram da ni, duk da ba ya sakewa sosai ina yabon kirkinsa da Amina. Amma tun daga kan abin da Mukhtar ya yi masa ya daina sake mini fuska, musamman lokacin rikici na da su Ummita har tsawa yake daka mini tamkar ya dake ni.
Ban ɓata lokaci ba na fara aikina gadan-gadan, Amina ta shigo muna hira ina aikin har lokacin tashi ya yi. Tare muka miƙa wa MD takardun muka fito tana cewa,
"Wai ina amarya? Na manta ban tambaye ki ba."
"Amarya tana gidan mijinta. Sauri nake yi ma na koma saboda ba na so yaran su yi mata ba daidai ba. Don na fahimci ita ma rawar kanta ya fi ta yawa."
Dariya Amina ta yi sannan ta ce, "Ganin take yi karanta ya kai tsaiko. Tun da ta haÉ—a kishi da mace mai halin kirki da nagarta irin taki. Don wallahi ba don ke ta samu ba; da sai ta gane barno gabas take a yadda na gan ta wata jagwal tamkar sandar makafi."
Ajiyar zuciya na yi ina tare wata adaidaita na ce, "Ki bari kawai! Nan da kike ganin ta ba ba ƙaramar 'yar hannu ba ce."
"A hakan?"
"Tabbas! Ke dai kin ga mutum!"
Da haka na tafi muna ɗaga wa juna hannu. Zuciyata cike da tunanin su Ummu Salma har aka ajiye ni ƙofar gidan. Tun da na jefa ƙafafuwana cikin gidan na fara jin sautin kukan Ummu Salma. Da sassarfa na shiga falon idona a kan Ummu Salmar da ke rakuɓe jikin gini tana cisgar kuka har da shessheka.
'Me nake shirin gani?'
Wata sabuwa🤔 wa ya taɓa mana Ummu Salma ne haka?😢
D. AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*TALATIN DA BIYAR .*
"Lafiya!? Me ya same ki!?"
Abin da na fara faÉ—a kenan a hargitse tun kafin na isa inda take. Tana gani na da ta tarye ni da gudu ta faÉ—a jikina, tare da rushewa da wani sabon kukan ya sa jikina kyarma.
Domin ko ni rabon da na saka hannu na dake ta har na manta, saboda tana ƙoƙarin barin abin da duk ta san ba na so, balle ta yin abin da zan dake ta a kansa. Haidar ne kawai yake shan duka a wurina, don ko Iman miskilancinta kawai yake sa na dake ta idan na saka ta aiki tana jan jiki.
Jikina na ɓanɓare ta ina faɗin, "Faɗa mini me ya faru?" Cikin shesshekar kuka ta ce, "Abbanmu ya dake ni"
"Me kika yi masa?"
Ƙirjina yana bugawa na yi maganar saboda sabon ɓacin ran da ya ziyarci zuciyata.
"Girki na zo zan É—ora amarya ta ce ba zan É—ora shi ba, ni kuma ganin kin ce na yi kafin ki dawo ya sa na ci gaba da yi. Ban san ya aka yi ba ina tsaka da kwasar abincin na ji muryar Abbanmu yana ta zagi na. Shi ne ya same ni a kitchen É—in yana ta dukana, kuma ya É—auke abincin duka ya ce ba za mu ci ba tun da amarya ta yi girki shi kowa zai ci."
"To fa! Abin har ya kai can?"
"Har ya wuce ma! Kuma wallahi matuƙar kika sa ta raina Barcy sai na ci uwarta a cikin gidan nan."
Zancen Mukhtar kenan a sama yana ba ni amsar tambayar da na yi wa kaina cike da mamaki. Na saki hannun Ummu Salma na tarye shi gaba da gaba na ce,
"Sai dai ka ci ubansu waton kai kenan! Don wallahi daga kai har wannan ƙanjamammar amaryar holoƙon da kake tinƙaho da ita; kun yi kaɗan ku ci zarafin yarana ba bisa haƙƙinsu ba. Abinci da ta dafa kuma ni na ba ta umurnin dafawa, saboda ba zan sake zama wata ballagaza tana hora mu da yunwa ba."
"Ke kika ba ta umurni Barcy kuma ta hana ta, saboda tun kafin su dawo gidan ta yi girki. Kuma shi za a ci dole don tuni na kyautar da wanda ta dafa."
Baki a sake nake bin fuskarsa da kallo saboda mamakin zancensa na 'ke kika saka ta Barcy ta hana'.
"Waton ita Barcyn ce za ta dinga ba mu umurnin abin da za mu yi a gidan da wanda za mu bari?"
"E! Saboda ni ce amarya kuma har yanzu ina cikin kwanakin girkina. Ki bari idan girkin ya dawo hannunki ki yi duk abin da kike so babu ruwana. Amma yanzu kam babu wanda zai É—ora girki a cikin gidan nan bayan wanda na dafa."
Martanin Barira kenan tana girgizar jiki tare da riƙe ƙugu. Ta so ba ni dariya amma na fuske na ce,
"Sannu shafaffiya da mai jikar sarauniyar Ingila 'yar gidan Sarki Macciɗo. To na rantse da Allah zan yi bikin watan cin ubanki a cikin gidan nan. Ko ki fita sabga ta da yarana; ko na nuna miki na fi ki sanin makamar iskanci da rashin mutunci. Abincinki kuma wallahi daga ni har yaran ba za mu sake jiransa ba, ke da cin abinci ya kawo gidan ki buɗe ciki ki yi ta zubawa, nawa kaso da na yarana duka mun bar miki. idan kin ƙoshi ki miƙa saura gidanku don na san suna da buƙata."
Baki a sake take kallona tare da cizon yatsa tana faÉ—in,
"Kai kai kai!"
Kansa na juya ina faÉ—in,
"Kai kuma mijin ta ce! Namijin ho-ti-ho! Ɗankwali ya ja hula! To ka sanar da ita babu kwanakin girkin kowa a kaina. Idan ma akwai duka na bar mata don haka ku sake wa 'ya'yana mara su ji daɗin fitsari. Kuma daga yau abincinmu daban za mu dinga girkawa, idan ka ji tsoron Allah ka ba mu namu haƙƙin. Domin ka rage wa kanka guzurin mugun bugun da Mala'iku za su yi maka a ranar lahira. Idan kuma ka bijire kamar yadda ka yi a baya, ina maka albishir za ka girbi duk abin da ka shuka khairan ko sharran. Na zare hannuna a cikin sha'anin girkin matarka, ni ma daga yau babu ruwanta da duk abin da za mu ci ko mu sha, a cikin gidan nan ni da yarana. Saboda ba za mu zauna tana gasa mana aya a hannu ba saboda abinci."
" Ina ƙare faɗar hakan na yi gaba zan shige ɗakina, sannan na yi saurin juyowa ina faɗin,
"Gass nawa ne, ni na saya da kuɗina, repelling ma ni nake yi ba wani yake yi mini ba. Daga yau kada a sake taɓa mini kaya ko da ɗora ruwan zafi ne!"
"Wallahi ni kuma ba zan yi girki da itace ba!"
Abin da Barira ta yi hanzarin faɗi kenan tana murguɗa baki. Saboda Ummu Salma ta faɗa mini ita ce ta nuna mata yadda ake amfani da shi. Lokacin da take girkin tana 'yan waƙe-waƙen farinciki, lokacin da wata ta kira ta a waya baki a sake take faɗin,
'Ke yarinya na wuce nan! Sabod Allah ya kawo ni gidan arziƙi, inda ba zan sha wahalar hura wutar ice ba. Gass cooker Hajiya shi nake girki da shi yanzu haka har na kusa gamawa... Ja can yarinya! Allah dai ya ba ku irin tawa kawai, don ni na tako arziƙi na wuce da sanin ku ƙananun ƙwari.'
Tuno labarin na yi murmushi mai sauti sannan na ce da ita, "Wannan kuma mijinki za ki faÉ—awa ba ni ba!"
"To ni ko idan dai da ice zan dinga girki, sai dai kada kowa ya ci abinci a gidan nan, daga ni har shi wallahi."
"Kanku ake ji!"