Sashe 37
Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da gudu suka taso suna ihun murnar gani na, idona a kansu na ce da su,
"A nan kuke shirin yau kuma?"
Haidar ya yi saurin faɗin, "Abbanmu ya ce mu ɗauko duk abin da muke so mu tsaya nan, kada mu ɓata masa fenti."
"Ah! Tabbas ya kyauta, ko ba komai kayanku za su huta da kwasar fentin da za a sha wuyar fitar da shi idan an zo wanki."
Ummu Salma ta ɓata fuska tana faɗin, "Har fa dukan Haidar ya yi, don ya taɓa fentin bai sani ba ya goge wurin."
"Da bai taɓa ba ai ba zai dake shi ba! Ni dai ku yi sauri ku shirya ku tafi makarantar. Kun ci abinci dai ko?"
"Bai bari Aunty Ummu ta dafa mana ba, wai kada a ɓata masa fenti a bari sai gobe idan ya ƙame."
"To me kuka ci?"
Tambayar da na jefo wa Iman kenan saboda ita ce ta ba ni amsar.
"Gari da suga ya siyo mana muka sha. Kuma wallahi ni ban ma ƙoshi ba." Haidar ya faɗa yana turo baki a ƙoƙarin shi na nuna mini haushin da ya ji a kan hakan.
"Oya ku gama shirin kafin na dafa muku Indomie yanzu shaf-shaf!"
Ban jira cewarsu ba na yi ciki da sauri don raina ya yi ƙololuwar ɓaci. Kallo na bi falon da shi saboda ganin yadda aka mayar da kayan cikinsa duka gefe, an shafe falon tas da fenti mai kala biyu sai ƙyalƙyali yake yi. Sannan ƙofofin ɗakunan duka sun sha fenti har maiƙo suke yi.
Ƙofar ɗakina na tura na shiga, shi kam yana nan yadda yake ba a taɓa mini komai ba. Jakata na ajiye tare da cire hijabin da ke jikina na fice zuwa kitchen. A nan ma ya Sha fentin ko'ina fes-fes duk da an hargitsa mini kayan cikinsa.
Cikin mintuna ƙalilan na gama dafa Indomien, na wanko tire na juye duka sannan na fito tsakar gidan. A kan tabarmar da suke kai muka baje, sai da suka ci suka ƙoshi har suka bar mini saura. Sannan na yi musu addu'a kamar yadda na saba suka fice suna faɗin "Mama sai mun dawo."
Da sauri na miƙe saboda alamun zuwan period da na ji a jikina. Wanka na faɗa a gurguje na fito, a nan na ga toilet ɗin ma ya sha fenti har da ƙyauren ƙofar.
Murmushi na yi a raina na ce, 'An zo wurin' Domin har cikin zuciyata ina farincikin auren duk da bai fito ya sanar da ni ba.
Bayan na kimtsa na dawo kitchen na ɗora mana girki dare, saboda time ya tafi biyar har ta wuce. Kasancewar ina da sauran garin semo tuwon shi na yi mana shaf-shaf da miya yauɗi. Na jefa mata ƙwarorin busasshen kifin da ya rage mana nan take ƙamshi ya karaɗe gidan.
Ina tsaka da kaÉ—a miyar Mukhtar ya shigo kitchen É—in, hannuwansa a aljihu ya tsaya bayana bai ce da ni komai ba. Tun kallon farkon da na yi masa ban sake bi ta kan shi ba har sai da ya yi gyaran murya ya ce,
"Girki kike yi?"
"Idonka ya ganar maka ai!"
Amsar da na ba shi kenan, ba tare da na daina abin da nake yi ba.
"Ban so aka yi girki a gidan nan yau ba, saboda fentin nan ba na so a lalace shi tun kafin ya gama ƙamewa."
"Idan kai ka iya hora Yaranka saboda fenti, ni kam ba zan iya barin su da yunwa ba a kan ka yi sabon fentin."
"To shi kenan a bar zancen kawai, daman ina so na sanar da ke auren da zan yi a cikin satin nan mai zuwa. Saboda ba na so ki ji a wani wuri gara ki ji komai a bakina."
Dariya na yi mai sauti sannan na saukar da miyar ina goge wurin da na ɓata na ce, "Wannan ai abin farinciki ne ba kaɗan ba. Da ka faɗa mini da wuri ma ɗakina zan bar wa amaryar na koma ɗakin su Ummu Salma. Saboda sai ta fi jin daɗinsa fiye da ɗakinsu don ya fi shi girma. Amma tun da a can ka fi so ta zauna shi kenan babu damuwa, ina taya ka murna Allah ya kawo ta lafiya, kuma ya ba da zuri'a ɗayyiba a tsakaninku."
Shiru ya yi kawai yana kallo na, ni kam abincina kawai na zuba a plate na raɓa gefen shi na fice. Jikina ya ba ni kallon mamaki ya ni da shi a lokacin da zan bar kitchen ɗin, shigowar su Ummu Salma ya sa na fice tsakar gidan ina cewa da su su je ɗakinmj su cire kayan makarantarsu, su yi shirin sallah.
Kujerar roba na janyo na zauna a tsakar gidan ina ta cin abincin ina 'yan waƙe-waƙena. Tsayuwar shi kawai na ji a gabana yana huci ya ce,
"Ko ba ki yi hakan ba, na san yanzu ba kya so na, to ki sha kuruminki in dai ni ne sai na nuna miki na fi ki rashin mutunci. Kuma ki sani ban ji zafin kin daina kishina ba, tun da zan auro mai sona tsakani da Allah kuma wadda ta san zafina. Ki je ki ci gaba da ƙuncinki ni ko a jikina wallahi, don ba ke kaɗai Allah ya ba ni damar aure ba balle ki nemi wulaƙanta ni a banza."
"Bazar kowa bazar kowa."
"Da bazarka ce nake taka rawa."
"Haƙiƙa ya habibina"
"Ƙaunarka ce ta sa ni zumuɗi."
"Yau sai ka zo mu É—an taka rawa. Yau sai ka zo mu É—an taka rawaaaa!"
Waƙar da na fara rerawa kenan, da abin ya yi mini daɗi na ajiye plate ɗin tuwona na fara tiƙar rawa, gaban shi na zo ina laƙamo wuyansa tare da goga fuskata jikin tashi musamman da na zo ƙarshen baitin ina faɗin "Taka rawaaaa!"
Cire hannuna ya yi daga wuyan shi ya wurgar cikin fushi, tare da nuna ni da hannu yana faÉ—in,
"Sai kin san ni kika wulaƙanta!"
Yana ƙare faɗar haka ya juya zai fice gidan, na bi shi da waƙar,
"Ku yi ta kanku"
"Mu ma mu yi ta kanmu"
"Dariyaa ba fa so ba"
"Ya raye daÉ—in dariyalle"
"Mai hali bai bari ba"
Har ya fita ya dawo buguzum ya shiga ciki kamar ya kifa, na koma na zauna tare da É—aukar plate É—in tuwona ina ci. Lokacin da na ji zai fito na sake É—auko wani sabon baiti na É—ora.
"Bana an gama komai"
"Bori ya kashe boka"
"In dai taro ne in babu ai suna ne"
"Allah ya yi sarkin daka shi ne turmi ahayye"
"Takun ya yi wasu sun saki reshe sun kama ganye."
Babu zato na ji ya shaƙo wuyana, cikin azama saki plate ɗin na rarumi jarumar shi na matse iya ƙarfina. Ya yi hanzarin saki na ya dafe gaban shi hannu biyu yana faɗin,
"Wallahi sai kin gane kuskuren tozarcin da kike ƙoƙarin yi mini a gidan nan."
Daga haka ya fice gidan dafe da gaban shi yana nuna ni da hannu yana ƙwafa.
Na bi ƙofar da harara kafin murmushin mugunta ya suɓuce mini ba tare da na shirya ba. Haka kawai na tsinci kaina cikin nishaɗi, ko babu komai ban bari ya gano dakan luguden da zancen auren shi ya yi mini a zuciya ba.
Saboda ban yi zaton zan ji kishin shi a raina ba, kamar yadda na ji zafin zancen auren da ya yi mini ba a zuciya.
Daren ranar kwana na yi cikin yarana cike da jin daɗi da farinciki, duk da wani gefen zuciyata yana hasko mini kalar matar da Mukhtar zai aura. Tsaki na yi ya fi a ƙirga saboda tunanin kowace ce wataƙila ta fi ni komai, shi ya sa ta yi nasarar kama masa wuya har ya amince zai aure ta.
'To ina ruwanki idan ma ta fi ki? Ke da ba ki son shi kishin me za ki yi na shi?'
Tambayar da zuciyata ta kitsa mini kenan, wadda na kasa bai wa kaina amsa. Saboda ni na sani ba Mukhtar ne ba na so ba, halinsa ne ya janyo ya sire mini na juya wa son shi baya. Kuma ba na ji zai iya yi mini abin da zai ya goge tabon baƙincikin da ya bar wa zuciyata iya rayuwa.
Warr💃ðŸ»
Na yi nan kada Mukhtar ya ci ufana🤣ðŸƒðŸ»â€â™€ï¸ðŸƒðŸ»â€â™€ï¸
D.AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*ASHIRIN DA BAKWAI.*
Da safe ban fita aiki ba har sai da na gyara zaman kujeruna, kasancewar falon babba ne na yi gefen É—akina da su duka. Sannan na sa aka kafa mini plasma TV ta a bango, daidai tsakiyar kujeruna. Saboda ba na son a zo yi wa amarya jere a nemi kawo mini rainin hankali, ko kuma shi ya faÉ—a mini abin da ba zan ji daÉ—i ba a samu matsala.
Ranar sai ƙarfe sha ɗaya na je ma'aikatarmu, na duƙufa aiki sosai ba tare da na biye surutun Amina ba. Lokacin da aka tashi ma ban yi jinkirin komai ba na nufo gida, saboda tunanin yaran da ke raina. Domin fargabar da nake ciki a kan kada ya hana su yin girki kamar yadda ya yi jiya, cikin sa'a na taradda Ummu Salma kitchen tana aikin abincin.
Sannu da zuwan da suke yi mini kawai na amsa, sannan na yi wanka a gurguje na fito. Iman na ce ta zo ta raka ni mu je gidan Maman TaufiÆ™. Haidar ya fara rigimar sai ya bi ni na ce da su kowa ya yi zamansa na fasa ba zan je ba.
Abincin Ummu Salma ta kawo mana muka baje a tsakiyar kujerun muka fara ci muna hira. Mukhtar ya shigo da manyan ledodi a hannunsa ya yi ɗakin shi yana muƙu-muƙu, sai da ya fito sannan ya fara faɗin ina abincin shi.
Kallo ma bai ishe ni ba balle na tanka masa, Ummu Salma ce ta miƙe ta ɗauko masa kular abincin ta miƙa masa. Karɓa kawai ya yi ya nufi ɗakinsa, na bi bayansa da harara saboda haushin auren da ya jajiibo wa kansa nake ji.
"A nan kuke shirin yau kuma?"
Haidar ya yi saurin faɗin, "Abbanmu ya ce mu ɗauko duk abin da muke so mu tsaya nan, kada mu ɓata masa fenti."
"Ah! Tabbas ya kyauta, ko ba komai kayanku za su huta da kwasar fentin da za a sha wuyar fitar da shi idan an zo wanki."
Ummu Salma ta ɓata fuska tana faɗin, "Har fa dukan Haidar ya yi, don ya taɓa fentin bai sani ba ya goge wurin."
"Da bai taɓa ba ai ba zai dake shi ba! Ni dai ku yi sauri ku shirya ku tafi makarantar. Kun ci abinci dai ko?"
"Bai bari Aunty Ummu ta dafa mana ba, wai kada a ɓata masa fenti a bari sai gobe idan ya ƙame."
"To me kuka ci?"
Tambayar da na jefo wa Iman kenan saboda ita ce ta ba ni amsar.
"Gari da suga ya siyo mana muka sha. Kuma wallahi ni ban ma ƙoshi ba." Haidar ya faɗa yana turo baki a ƙoƙarin shi na nuna mini haushin da ya ji a kan hakan.
"Oya ku gama shirin kafin na dafa muku Indomie yanzu shaf-shaf!"
Ban jira cewarsu ba na yi ciki da sauri don raina ya yi ƙololuwar ɓaci. Kallo na bi falon da shi saboda ganin yadda aka mayar da kayan cikinsa duka gefe, an shafe falon tas da fenti mai kala biyu sai ƙyalƙyali yake yi. Sannan ƙofofin ɗakunan duka sun sha fenti har maiƙo suke yi.
Ƙofar ɗakina na tura na shiga, shi kam yana nan yadda yake ba a taɓa mini komai ba. Jakata na ajiye tare da cire hijabin da ke jikina na fice zuwa kitchen. A nan ma ya Sha fentin ko'ina fes-fes duk da an hargitsa mini kayan cikinsa.
Cikin mintuna ƙalilan na gama dafa Indomien, na wanko tire na juye duka sannan na fito tsakar gidan. A kan tabarmar da suke kai muka baje, sai da suka ci suka ƙoshi har suka bar mini saura. Sannan na yi musu addu'a kamar yadda na saba suka fice suna faɗin "Mama sai mun dawo."
Da sauri na miƙe saboda alamun zuwan period da na ji a jikina. Wanka na faɗa a gurguje na fito, a nan na ga toilet ɗin ma ya sha fenti har da ƙyauren ƙofar.
Murmushi na yi a raina na ce, 'An zo wurin' Domin har cikin zuciyata ina farincikin auren duk da bai fito ya sanar da ni ba.
Bayan na kimtsa na dawo kitchen na ɗora mana girki dare, saboda time ya tafi biyar har ta wuce. Kasancewar ina da sauran garin semo tuwon shi na yi mana shaf-shaf da miya yauɗi. Na jefa mata ƙwarorin busasshen kifin da ya rage mana nan take ƙamshi ya karaɗe gidan.
Ina tsaka da kaÉ—a miyar Mukhtar ya shigo kitchen É—in, hannuwansa a aljihu ya tsaya bayana bai ce da ni komai ba. Tun kallon farkon da na yi masa ban sake bi ta kan shi ba har sai da ya yi gyaran murya ya ce,
"Girki kike yi?"
"Idonka ya ganar maka ai!"
Amsar da na ba shi kenan, ba tare da na daina abin da nake yi ba.
"Ban so aka yi girki a gidan nan yau ba, saboda fentin nan ba na so a lalace shi tun kafin ya gama ƙamewa."
"Idan kai ka iya hora Yaranka saboda fenti, ni kam ba zan iya barin su da yunwa ba a kan ka yi sabon fentin."
"To shi kenan a bar zancen kawai, daman ina so na sanar da ke auren da zan yi a cikin satin nan mai zuwa. Saboda ba na so ki ji a wani wuri gara ki ji komai a bakina."
Dariya na yi mai sauti sannan na saukar da miyar ina goge wurin da na ɓata na ce, "Wannan ai abin farinciki ne ba kaɗan ba. Da ka faɗa mini da wuri ma ɗakina zan bar wa amaryar na koma ɗakin su Ummu Salma. Saboda sai ta fi jin daɗinsa fiye da ɗakinsu don ya fi shi girma. Amma tun da a can ka fi so ta zauna shi kenan babu damuwa, ina taya ka murna Allah ya kawo ta lafiya, kuma ya ba da zuri'a ɗayyiba a tsakaninku."
Shiru ya yi kawai yana kallo na, ni kam abincina kawai na zuba a plate na raɓa gefen shi na fice. Jikina ya ba ni kallon mamaki ya ni da shi a lokacin da zan bar kitchen ɗin, shigowar su Ummu Salma ya sa na fice tsakar gidan ina cewa da su su je ɗakinmj su cire kayan makarantarsu, su yi shirin sallah.
Kujerar roba na janyo na zauna a tsakar gidan ina ta cin abincin ina 'yan waƙe-waƙena. Tsayuwar shi kawai na ji a gabana yana huci ya ce,
"Ko ba ki yi hakan ba, na san yanzu ba kya so na, to ki sha kuruminki in dai ni ne sai na nuna miki na fi ki rashin mutunci. Kuma ki sani ban ji zafin kin daina kishina ba, tun da zan auro mai sona tsakani da Allah kuma wadda ta san zafina. Ki je ki ci gaba da ƙuncinki ni ko a jikina wallahi, don ba ke kaɗai Allah ya ba ni damar aure ba balle ki nemi wulaƙanta ni a banza."
"Bazar kowa bazar kowa."
"Da bazarka ce nake taka rawa."
"Haƙiƙa ya habibina"
"Ƙaunarka ce ta sa ni zumuɗi."
"Yau sai ka zo mu É—an taka rawa. Yau sai ka zo mu É—an taka rawaaaa!"
Waƙar da na fara rerawa kenan, da abin ya yi mini daɗi na ajiye plate ɗin tuwona na fara tiƙar rawa, gaban shi na zo ina laƙamo wuyansa tare da goga fuskata jikin tashi musamman da na zo ƙarshen baitin ina faɗin "Taka rawaaaa!"
Cire hannuna ya yi daga wuyan shi ya wurgar cikin fushi, tare da nuna ni da hannu yana faÉ—in,
"Sai kin san ni kika wulaƙanta!"
Yana ƙare faɗar haka ya juya zai fice gidan, na bi shi da waƙar,
"Ku yi ta kanku"
"Mu ma mu yi ta kanmu"
"Dariyaa ba fa so ba"
"Ya raye daÉ—in dariyalle"
"Mai hali bai bari ba"
Har ya fita ya dawo buguzum ya shiga ciki kamar ya kifa, na koma na zauna tare da É—aukar plate É—in tuwona ina ci. Lokacin da na ji zai fito na sake É—auko wani sabon baiti na É—ora.
"Bana an gama komai"
"Bori ya kashe boka"
"In dai taro ne in babu ai suna ne"
"Allah ya yi sarkin daka shi ne turmi ahayye"
"Takun ya yi wasu sun saki reshe sun kama ganye."
Babu zato na ji ya shaƙo wuyana, cikin azama saki plate ɗin na rarumi jarumar shi na matse iya ƙarfina. Ya yi hanzarin saki na ya dafe gaban shi hannu biyu yana faɗin,
"Wallahi sai kin gane kuskuren tozarcin da kike ƙoƙarin yi mini a gidan nan."
Daga haka ya fice gidan dafe da gaban shi yana nuna ni da hannu yana ƙwafa.
Na bi ƙofar da harara kafin murmushin mugunta ya suɓuce mini ba tare da na shirya ba. Haka kawai na tsinci kaina cikin nishaɗi, ko babu komai ban bari ya gano dakan luguden da zancen auren shi ya yi mini a zuciya ba.
Saboda ban yi zaton zan ji kishin shi a raina ba, kamar yadda na ji zafin zancen auren da ya yi mini ba a zuciya.
Daren ranar kwana na yi cikin yarana cike da jin daɗi da farinciki, duk da wani gefen zuciyata yana hasko mini kalar matar da Mukhtar zai aura. Tsaki na yi ya fi a ƙirga saboda tunanin kowace ce wataƙila ta fi ni komai, shi ya sa ta yi nasarar kama masa wuya har ya amince zai aure ta.
'To ina ruwanki idan ma ta fi ki? Ke da ba ki son shi kishin me za ki yi na shi?'
Tambayar da zuciyata ta kitsa mini kenan, wadda na kasa bai wa kaina amsa. Saboda ni na sani ba Mukhtar ne ba na so ba, halinsa ne ya janyo ya sire mini na juya wa son shi baya. Kuma ba na ji zai iya yi mini abin da zai ya goge tabon baƙincikin da ya bar wa zuciyata iya rayuwa.
Warr💃ðŸ»
Na yi nan kada Mukhtar ya ci ufana🤣ðŸƒðŸ»â€â™€ï¸ðŸƒðŸ»â€â™€ï¸
D.AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*ASHIRIN DA BAKWAI.*
Da safe ban fita aiki ba har sai da na gyara zaman kujeruna, kasancewar falon babba ne na yi gefen É—akina da su duka. Sannan na sa aka kafa mini plasma TV ta a bango, daidai tsakiyar kujeruna. Saboda ba na son a zo yi wa amarya jere a nemi kawo mini rainin hankali, ko kuma shi ya faÉ—a mini abin da ba zan ji daÉ—i ba a samu matsala.
Ranar sai ƙarfe sha ɗaya na je ma'aikatarmu, na duƙufa aiki sosai ba tare da na biye surutun Amina ba. Lokacin da aka tashi ma ban yi jinkirin komai ba na nufo gida, saboda tunanin yaran da ke raina. Domin fargabar da nake ciki a kan kada ya hana su yin girki kamar yadda ya yi jiya, cikin sa'a na taradda Ummu Salma kitchen tana aikin abincin.
Sannu da zuwan da suke yi mini kawai na amsa, sannan na yi wanka a gurguje na fito. Iman na ce ta zo ta raka ni mu je gidan Maman TaufiÆ™. Haidar ya fara rigimar sai ya bi ni na ce da su kowa ya yi zamansa na fasa ba zan je ba.
Abincin Ummu Salma ta kawo mana muka baje a tsakiyar kujerun muka fara ci muna hira. Mukhtar ya shigo da manyan ledodi a hannunsa ya yi ɗakin shi yana muƙu-muƙu, sai da ya fito sannan ya fara faɗin ina abincin shi.
Kallo ma bai ishe ni ba balle na tanka masa, Ummu Salma ce ta miƙe ta ɗauko masa kular abincin ta miƙa masa. Karɓa kawai ya yi ya nufi ɗakinsa, na bi bayansa da harara saboda haushin auren da ya jajiibo wa kansa nake ji.