← Book details Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 68

Sashe 52

Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ba zai kashe ki ba, amma za ki raina kanki."

"Don Allah Aunty kada ki biye ta, wallahi ba na so Romiyo ya ji maganar nan. In Sha Allah daga yau ko gidan nan ba za ta sake zuwa ba."
"Ke kam kina da abin takaici Barira! Har yaushe za ki dinga kwantar da kai ga kishiya irin haka tamkar za ki yi mata sujada. Abin da take tunanin an yi kuma shi aka aikata, idan akwai wani abu da za ta yi kafin soloɓiyon mijin ya zo ta fara yi kafin shi. Ni wallahi da na auri irin wannan ragon mazan ƙara na lalace a kan titi."

Dariya ta so ba ni, amma kuma na mazge na ce,
"Oh ita Barirar ce ta faɗa miki soloɓiyo ne?"
"Ko ma dai mene ne hakan yake."

Bubbugar ƙofar da ake yi ya sa na je na buɗe kwaɗon na ja gefe, saboda ganin Yaya Maimuna fuskarta a haɗe. Tana ƙoƙarin yin magana Barira ta iso wurinta da gudu tana kuka tare da kai mata ƙara ta.
"Kin ga Aunty nan ta saka Aunty Suby gaba tana ƙoƙarin manna mata sharri. Don Allah ki ce ta bar ta ta tafi tun da ba gaskiya ba ne abin da take zargi."

"Yi shiru! FaÉ—a mini me ya faru?"

Zancen Yaya Maimuna kenan tana ƙoƙarin rarrashin Barira, ta hanyar bubbuga bayanta tana share mata hawaye.
Suby ta fara magana tana cewa,
"Wai daga ta dawo ta gan ni cikin gidan, shi kenan take neman haÉ—a ni da sharri. To wallahi ni daidai nake da zamaninta don na ci dubu sai ce..."
Marin da na kai mata a haukace ya sa ta haɗiye sauran maganar da ke bakinta. Ban jira komai ba, na yi cikinta da duka cikin sa'a na jefar da ita ƙasa na haye. Yaya Maimuna da Barira suna ƙoƙarin ture ni kanta na yi wata zabura na watsar da su ƙasa warwas suka faɗi.
Sannan na ci gaba da kai wa Suby naushi a baki su ma suka rufe ni da duka. Hargowar Mukhtar ta sa dukanmu muka shiga hankalin kanmu. Gefen bakin Suby ya kumbure tamkar zunɓutun kaza, amma a hakan ta dinga aika mini zagi ta uwa ta uba.
Mukhtar ya dakatar da ita, sannan ya tambayi dalilin faɗan. Na yi masa bayanin komai Barira ta fashe da kuka tana faɗin ƙarya nake yi mata. Suby ma ta tuɓure a kan sharri ne na yi musu ba gaskiya ba ne.
Yaya Maimuna ta dinga jifa ta da miyagun maganganun da suke nuni; da fatar abin da nake yi wa Barira ƙazafi da shi ya hau kaina ko 'ya'yana.
Raina a ɓace na ce, "Bakinki ya sari ƙaton dutse, don har abada ni ko yarana ba za mu yi irin wannan halin tumakai ba."
Mukhtar ya taso mini da masifa kamar ya dake ni, wai na yi wa Barira da Subyn ƙazafi kuma idan na sake duk abin da na janyo wa kaina babu ruwan shi. Haushi ya sa na dinga mayar masa da raddi bakina yana kumfa tamkar na kai masa duka.
Sanin halina ya sa bai taɓa ni ba, ya dawo kan Suby yana ba ta haƙuri tare da lallaɓa ta har ta fice gidan. Yaya Maimuna kuma ta dawo da faɗan sabo don daman can shi ya kawo ta.

"Daman wurinki na zo! Zugar da kike yi wa Sajida ta yi aiki. Amma ki sani wallahi muddin kika ga ba a yi auren nan ba; to sai idan ba na numfashi a cikin duniya. Amma wajibi ne sai Sajida ta auri Aminu ko kina so ko ba kya so."

"Wane Aminun!!?"

Zancen Maman TaufiÆ™ kenan cikin muryar tashin hankali, a lokacin da take shigowa gidan idonta a kan Yaya Maimuna.

"Aminu na ji kina faÉ—a!"

"Ko ma dai wane ne ba ku isa ku hana abin da Allah ya ƙaddara ba"

Tambaya Maman TaufiÆ™ kenan da amsar Yaya Maimuna a lokaci É—aya. Jikina yana rawa na ja Maman TaufiÆ™ muka shige ciki ina faÉ—in,
"Ba da ke suke ba ni aka zo yi wa takakkiya. Ni kuma a yanzu daidai nake da kowa tun da abin nasu babu mutunci balle kawaici."
"Wai har na ji sanyi wallahi. Ba ki ji yadda ƙirjina ya buga ba a lokacin da na ji ta kira sunan Amini.."
Zama muka yi a kan kujera tana faÉ—in, "Ita Sajida aure za ta yi ne?"

"E, kuma ba ta son mutumin."

"Kuma shi ne za a zo wurinki takakkiya miye naki a ciki?"

"Su dai suka sani."

"Hayaniya na ji shi ya sa na zo na gani lafiya? Ashe Mamarta ce take abin da ta saba. Ni na rasa laifin me kika yi wa wannan matar da ta saka ki gaba irin haka."

"Mijinki ake so a manna wa Sajida ba ki da labari."
Maganar Barira kenan da muka jiyo daga ni har Maman Taufiƙa saman kanmu.

"Mijina kuma?"

"E, shi! Kuma babu mai son ta ga auren nan ya ƙullu face wadda kuke zaune da ita yanzu. Don a gabana take saka Sajida ta manne wa mijinki, domin kawai ta ga ƙarshen kishinki."

"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun!"

Ita ce kalmar da muka haɗa baki wurin faɗa ni da Maman Taufiƙ, tare da miƙewa tsaye dukanmu muna kallon Barira.

"To wasa ce nake yi! Ku yi haƙuri don Allah kada ku cinye ni da raina."

Barcy lamarinki sai ke 🤔😂

D. AUTA CE✍🏼

*ABOKIN AIKINA*

*@HADIZA D. AUTA*

*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*

*TALATIN DA BAKWAI.*

Ban san ya aka yi ba, sai hango Maman Taufiƙ na yi maƙare da wuyan Barira tana kakarin mutuwa. Cikin wani sabon tashin hankali na yi kansu ina ƙoƙarin ɓanɓare hannun Maman Taufiƙ, daga muguwar shaƙar da ta yi wa Barira. Wadda azaba ta sa ta gwalalo ido waje gulu-gulu tamkar idanun mota.
Ganin ba zan iya ni kaÉ—ai ba na fasa ihu saboda gabaÉ—aya sun fita hayyacinsu, tamkar wasu sababbin halitta. Mukhtar ya iso wurin a É—ari yana faÉ—in,

"Innalillahi wa inna ilaihirraji'un!"

Ya ja Barira na samu na ƙwace hannun Mama Taufiƙ, sai dai hakan bai yi mata ba ta koma ta cafko ta iya ƙarfinta. Mukhtar ya yi hanzarin ture ta gefe ta faɗi sannan ya rungume Barira yana ƙwala mata kira a haukace, saboda alamunsa ya nuna tsantsar kiɗima da ruɗewar da ya shiga. Ganin halin da Barira take ciki riƙe da wuyanta tana juye-juye tare da kakari a lokaci ɗaya.
Domin a kallo ɗaya za a kira shi da kakarin mutuwa saboda shure-shuren da take yi. Maman Taufiƙ kuma ta baje ƙasa tana gumza tamkar wata raƙuma. Bayan furzar da yawun da take yi yana baltsi a kan fuskarta.
Ruwa na ɗebo da gudu na dawo a firgice saboda na gama kai wa ƙololuwar ruɗewa. Sai dai tun kafin na iso na hango ta zabura tamkar wata zakanya ta yi kan Mukhtar da ke rungume da Barira.
Cakumo shi ta yi ta wurgar gefe tamkar a cikin shirin horror, sannan ta fisgo tsorayen Barira sai ga ta da su a hannu ta jefar ƙasa.
Kukan kura na yi tamkar wata ifirituwa na kai wa Maman Taufiƙ raruma ta baya. Saboda ƙoƙarin fisgo wasu tsorayen da take yi ta sauke su ƙasa kamar yadda ta yi wa na farkon. Kokawa muka shiga da ita tsakiyar falon tana so na sake ta ina damƙe ta iya ƙarfina. Tun muna faɗawa kujeru har muka faɗi ƙasa a tare muna mulmula tamkar wasu macizai.
Addu'a na dinga karanta mata a bakina cikin sauti tun tana fisge-fisgen har ta yi luf! Na ci gaba da karanta mata surorin tsari da kore shaiɗanun aljanu. Saboda na gamsu da cewa ba ta cikin hayyacinta balle hankalin kanta, shi ya sa take ƙoƙarin aikata aika-aikar da dukanmu sai mun yi da-na-sani.

Ganin ta lafa na hango Mukhtar ya nufi inda Barira da jini ya gama wanke mata jiki kaca-kaca. Ihu ya yi tare da kinkimarta tamkar 'yar tsana ya fice da gudu yana faman kiran sunanta.
Fitar su da ɗan lokaci na saki Maman Taufiƙ na miƙe ina kiran sunanta tare bubbuga jikinta. Firgigit ta miƙe idonta a zare sun yi jawur tana ƙare wa falon kallo, tamkar wadda aka bai wa aikin ƙididdige abin da ke cikin falon duka.

Hannunta na riƙa ta miƙe tana kakkaɓe kayan jikinta ta ce,
"Me ya kawo ni gidan nan?"
Fuskata ɗauke da mamaki na ce, "Kina nufin ba ki ma san kin zo gidan ba?" Na ƙare maganar tare da zuba mata idanuwa domin na tantance ita ce ko sarakan aljanunta masu neman ɗaukar rai.
"Wallahi Maman Haidar ban san na zo gidan nan ba! Iya abin da kawai zan ƙaras tuƙin tuwon da nake yi a kitchen.

"Cabɗijam! To mu je na raka ki gida kada ya ƙone a yi biyu babu"

Hijabinta na mayar mata sannan takalminta na ja nawa hijabin muka nufi gidanta. Abin mamaki tun a ƙofar gidan na fara jiyo ƙaurin ƙonewar shinkafa. Da sauri na sake ta na yi kitchen ɗinta da gudu na saukar da tukunyar tuwon. Wadda ta turnuƙe Kitchen ɗin da hayaƙi ko gabana da ƙyar na gani, har na samu sararin sauke tukunyar a kan gawayin da take girkin da shi.
Na fito ina tari tamkar na shiɗe, saboda ulcer ta ko kaɗan ba ta buƙatar hayaƙi. Dalilin da ya sa na daina aiki da komai sai gass, duk da a lokacin da na saye shi ba ƙaramar rigima muka yi da Mukhtar ba. Saboda ya buga kansa a ƙasa shi ba zai iya wahalar shi ba, na ce masa na ji na ɗauka ni zan ɗauki nauyin komai ko don lafiyata.

Gida na koma na rufe, sannan na dawo na kankare tuwon da fiye da rabinsa ya gama ƙonewa. A gurguje na canza tukunya na ɗora mata wani sabon tuwon, ganin garin semo a buhu ya sa na fara talga tuwon na rufe. Sannan na fito na nufi ƙofar gidan saboda sallamar da na ji Mukhtar yana bugawa.
Hankalina a tashe na isa ina tambayar shi Barira da halin da take ciki, harara ya kwaÉ—a mini tamkar idonsa su faÉ—o ya ce,
"Ba ni makulli!"
Chapter 52 · 0% Book details