Sashe 40
Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A fusace ya yi kaina zai kai mini duka, na yi hanzarin ja baya tare da nuna shi da hannu ina cewa,
"Kul! Kada ka yi gangancin taɓa ni ka janyo na yi maka aika-aika yanzun nan. Na fi so na je gidan kaso da na bari ka dake ni ka hana ni kokawa, domin mari da tsinka jakar da kake yi mini kullum ba don ba na iya ramawa ba ne nake ƙyalewa. Idan ka kai ni bango kuma zan nuna maka na fi ka zama 'yar tarawi."
"Idan ma kin ce za ki rama ai ke ce a wahale, domin aurena ne ba kya so kuma ba zan taɓa sakinki ba."
Yana ƙare faɗar hakan a fusace ya bar wurin zai fice falon, na biyo shi a zafafe ina faɗin, "In dai wannan baƙin auren kake taƙama da shi ka faɗo. Don tuni ya lalace babu komai a cikinsa face kwasar zunubai."
"A hakan kuma za ki zauna ko kina so ko ba kya so!"
Abin da ya faɗa kenan ya fice gidan, tare da bugo ƙofar da ƙarfi har sai da ƙirjina ya buga sanadin sautin ƙarar ƙofar,
'Garam!!!'
Dawowa na yi na zauna, zuciyata sai hawa da sauka take yi ina fisgar numfashina da ƙarfi. Na ɗauki lokaci a haka sannan na fara jin sallamar wasu mata a bakin ƙofar falon.
Na fito ina amsa sallamar idona a kansu, tunanin inda na san su a raina na yi amma na kasa.
"Dangin amarya ne, mun zo duba É—aki."
"Allah Sarki to ku shigo mana!"
Na ƙare maganar cikin sakin fuska da murmushin yaƙe na yi gaba, suka bi ni a baya na ja na tsaya a bakin ƙofar ɗakin. Da fara'ata a kan fuska na ce da su,
"Ku jira na karɓo muku makullin ɗakin a wurinsa."
"Ai shi ya ce mu shigo, ga makullin a nan ya ba mu."
"FaÉ—uwa ta zo daidai da zama, yanzu yake sanar da ni zai ba ni na ajiye muku kafin ya fita."
Maganar da na yi kenan ina 'yar dariya, a ƙoƙarin kore damuwar da ke kan fuskata.
"An hutar da ke ai tun da ya ba mu!"
Wata matashiya daga cikinsu ta faɗa cikin haɗe rai tana ƙoƙarin buɗe ɗakin, ɗakina na nufa zuciyata tana tafasa saboda duka biyun da yake ƙoƙarin hawa kaina. Tsakanin rashin mutuncin da Mukhtar ya yi mini da rainin hankalin da dangin amaryarsa suke ƙoƙarin kawo mini.
Wanka na faÉ—a shaf-shaf na dirje jikina, cike da jin haushin bai sanar da ni zuwansu ba. Da ban bari suka same ni a yadda nake ban cancanÉ—a kwalliya ba.
Ƙwafa na yi kawai tare da cije leɓen ƙasa a lokacin da na gama shafa hoda sama-sama. Wata doguwar rigar atamfata na saka fited gawn, kuma mai fitting ɗina sosai a duk lokacin da na saka. Turaruka nake fesawa ina jiyo sautin muryoyinsu suna yaba tsarin falon.
A daidai lokacin da suka shiga kitchen na fito na kunna tv sannan na zauna kan kujera ina kallo. Duk da ba na gane komai amma ban É—auke idona daga kan tv'n ba jefi-jefi na latsa wayata.
Sun É—auki minti sha biyar a kitchen É—in, suna ta maganganun da ba na tantance abin da suke faÉ—a. Sannan suka fito daga Kitchen É—in suna faÉ—in,
"Ma sha Allah wuri ya yi kyau! Sai fatan Allah ya ba da zaman lafiya da ƙazantar ɗaki."
Kaina na É—ago daga latsar wayar da nake yi na ce da su, "Amin, har kun gama?"
Wasu biyu suka wuce suna faÉ—in
"E, mu za mu tafi."
Yayin da wasu masu hankalin cikinsu uku suka ce, "Mun kammala, gobe idan Allah ya kai mu za mu zo a yi jere. Allah ya ba ku zaman lafiya da haƙuri da juna."
Da murmushi a kan fuskata na ce da su, "Amin-amin." Suka nufi hanyar fita na rako su ina yi musu godiya da Allah ya tsare.
Sai da suka fice gidan sannan na rufo ƙofar na juyo zuciyata a cunkushe da takaicin Mukhtar. Don da ya faɗa mini za su zo, dole ne a tanadar musu wani abu, saboda babu daɗi su tafi hannu rabbana ba a ba su komai ba.
Ko zama ban yi ba Maman TaufiÆ™ ta shigo na tarbe ta da fara'a muka zauna. Kallon tsarin falon ta shiga yi da kujeruna da muke kai, fuskarta a sake ta ce da ni,
"Kujerun nan sun yi mini kyau Maman Haidar!"
"Na gode" Na faÉ—a cike da murmushin da ya kasa barin fuskata. Zamanta ta gyara tana faÉ—in,
"Wasu mata na gani sun fito daga gidan nan suna ta yabonki. Kuma jikina ya ba ni kamar dangin amaryarsu ne?"
"E, su ne. Sun zo duba É—akin amarya da tsarin gidan."
"CabÉ—ijam! Lalle kin fara aika musu makaman nuclear. Domin kuwa da kunnena na ji wata yarinya daga cikinsu tana faÉ—in"
'Ni fa haushi ya hana ni tsayawa na fito gidan. Don wannan haÉ—aÉ—É—iyar mata ko ni aka haÉ—a kishi da ita an cuce ni balle Barira. CabÉ—i! Na tausaya wa mata gaskiya, don ta kawo kanta inda za a ga kasawarta'
'Idan ban da ma hali irin na maza da ba a iya musu; mai irin wannan zankaÉ—eÉ—iyar macen ne zai auri Barira?'
'Shi aure ai nufi ne na Allah! Ita ce matarsa shi ya sa ya nemo ta. Don haka ku zo mu je mu bi su da addu'ar zaman lafiya, saboda alamu ya nuna a fili ta yi sa'ar kishiyar da babu ruwanta'
Sanyin daɗi na ji ya tsirga mini, domin labarin da Maman Taufiƙ ta faɗa mini ba ƙaramin faranta zuciyata ya yi ba. Shiru kawai na yi ina ta murmushi, sai da ta yi 'yar kuwwar jin daɗi sannan ta sake cewa,
"A gaskiya Maman Haidar ke ƙwaro ce! A tashi guda kin hargitsa musu lissafi sun fita da ke a bakinsu."
Murmushi na yi mai sauti sannan na ce, "Ai shi yaƙi ɗan zamba ne, idan ba ka iya shi ba za ka sha wahalar kashe abokan gaba, kuma za a yi saurin gano maɓoyarka domin a kawo maka farmaki. Don haka ta wannan hanyar kaɗai zan iya rama abin da ake ƙoƙarin yi mini a fakaice. Saboda faɗa da tashin hankali ba zai kawo gyara ba, kuma ba zai sa a fasa abin da aka yi niyya ba. A ƙarshe ma biyu babu ake yi a rasa mutunci kuma a ɓarar da ƙima."
"Kai jama'a! Maman Haidar ke ta daban ce a cikin dubban mutane. Ban taɓa cin karo da macen da za a yi wa kishiya ta yi juriya irin taki ba. Wai don Allah da gaske ba kya jin komai a cikin ranki? Ni fa na kasa gasgata wannan lamari naki mai kama da almara."
Tambayar da ta yi mini ba ƙaramar dariya ta saka ni ba, saboda yanayin da ta yi maganar tamkar wata zautacciya. Sai da na gama dariyar sannan na ce da ita,
"Kowace mace tana da kalar nata kishin Maman Taufiƙ! Amma da a ce za a yi koyi da kalar kishin da magabata suka yi; Da mata da yawa ba su ɓarar da damar da Allah ya mallaka musu ba. Don sau da yawa namiji ba don ba ya son matarsa yake ƙara aure ba, ke wani lokaci ma ba ya ƙara ƙaunarki; har sai ya jera ki da wata ya gano akwai tazara a tsakaninki da sauran mata. Saboda haka da a ce za mu gane mu daina zafafa kishin maza idan za su ƙaro aure, da mun taimaki kanmu mun rage nauyin wahalar da muke ɗaukar wa kanmu a kan ɗa namiji. Ni kin ga ma a ranar da ya zo mini da zancen auren..."
Na kwashe duk yadda muka yi da Mukhtar na faɗa mata, dariya ta shiga sheƙawa har da riƙe ciki. Sai da ta gaji don kanta tana goge ƙwallar dariyar ta ce da ni,
"Wallahi ba ki da kirki Maman Haidar! Wannan tura haushin har ina saboda Allah?"
"Da a ce ban yi masa hakan ba, hauka zai siyo kasuwa ya manna mini ban ji ban gani ba. Saboda duk wani tashin hankalin da zan yi a lokacin; kai-tsaye zai ɗora shi a mizanin taɓin hankali. A ƙarshen ma zagina mutane za su dinga yi ba tare da sun yi duba da ƙunar da zuciyata ke yi, su tausaya mini ba."
"Wallahi zancenki gaskiya ne Maman Haidar! Amma kin san me? Ni ba zan iya wannan dauriyar ba. Allah kada ka jarrabe ni da irin wannan musibar mai wuyar shanyewa, don na san duk ranar da Amini ya sanar da ni zai yi aure; ba zan É—aga daga inda nake ba zan mutu."
😱cab!🤠Na yi nanðŸƒðŸ»â€â™€ï¸
D.AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*ASHIRIN DA TARA.*
"Kul! Kada ka yi gangancin taɓa ni ka janyo na yi maka aika-aika yanzun nan. Na fi so na je gidan kaso da na bari ka dake ni ka hana ni kokawa, domin mari da tsinka jakar da kake yi mini kullum ba don ba na iya ramawa ba ne nake ƙyalewa. Idan ka kai ni bango kuma zan nuna maka na fi ka zama 'yar tarawi."
"Idan ma kin ce za ki rama ai ke ce a wahale, domin aurena ne ba kya so kuma ba zan taɓa sakinki ba."
Yana ƙare faɗar hakan a fusace ya bar wurin zai fice falon, na biyo shi a zafafe ina faɗin, "In dai wannan baƙin auren kake taƙama da shi ka faɗo. Don tuni ya lalace babu komai a cikinsa face kwasar zunubai."
"A hakan kuma za ki zauna ko kina so ko ba kya so!"
Abin da ya faɗa kenan ya fice gidan, tare da bugo ƙofar da ƙarfi har sai da ƙirjina ya buga sanadin sautin ƙarar ƙofar,
'Garam!!!'
Dawowa na yi na zauna, zuciyata sai hawa da sauka take yi ina fisgar numfashina da ƙarfi. Na ɗauki lokaci a haka sannan na fara jin sallamar wasu mata a bakin ƙofar falon.
Na fito ina amsa sallamar idona a kansu, tunanin inda na san su a raina na yi amma na kasa.
"Dangin amarya ne, mun zo duba É—aki."
"Allah Sarki to ku shigo mana!"
Na ƙare maganar cikin sakin fuska da murmushin yaƙe na yi gaba, suka bi ni a baya na ja na tsaya a bakin ƙofar ɗakin. Da fara'ata a kan fuska na ce da su,
"Ku jira na karɓo muku makullin ɗakin a wurinsa."
"Ai shi ya ce mu shigo, ga makullin a nan ya ba mu."
"FaÉ—uwa ta zo daidai da zama, yanzu yake sanar da ni zai ba ni na ajiye muku kafin ya fita."
Maganar da na yi kenan ina 'yar dariya, a ƙoƙarin kore damuwar da ke kan fuskata.
"An hutar da ke ai tun da ya ba mu!"
Wata matashiya daga cikinsu ta faɗa cikin haɗe rai tana ƙoƙarin buɗe ɗakin, ɗakina na nufa zuciyata tana tafasa saboda duka biyun da yake ƙoƙarin hawa kaina. Tsakanin rashin mutuncin da Mukhtar ya yi mini da rainin hankalin da dangin amaryarsa suke ƙoƙarin kawo mini.
Wanka na faÉ—a shaf-shaf na dirje jikina, cike da jin haushin bai sanar da ni zuwansu ba. Da ban bari suka same ni a yadda nake ban cancanÉ—a kwalliya ba.
Ƙwafa na yi kawai tare da cije leɓen ƙasa a lokacin da na gama shafa hoda sama-sama. Wata doguwar rigar atamfata na saka fited gawn, kuma mai fitting ɗina sosai a duk lokacin da na saka. Turaruka nake fesawa ina jiyo sautin muryoyinsu suna yaba tsarin falon.
A daidai lokacin da suka shiga kitchen na fito na kunna tv sannan na zauna kan kujera ina kallo. Duk da ba na gane komai amma ban É—auke idona daga kan tv'n ba jefi-jefi na latsa wayata.
Sun É—auki minti sha biyar a kitchen É—in, suna ta maganganun da ba na tantance abin da suke faÉ—a. Sannan suka fito daga Kitchen É—in suna faÉ—in,
"Ma sha Allah wuri ya yi kyau! Sai fatan Allah ya ba da zaman lafiya da ƙazantar ɗaki."
Kaina na É—ago daga latsar wayar da nake yi na ce da su, "Amin, har kun gama?"
Wasu biyu suka wuce suna faÉ—in
"E, mu za mu tafi."
Yayin da wasu masu hankalin cikinsu uku suka ce, "Mun kammala, gobe idan Allah ya kai mu za mu zo a yi jere. Allah ya ba ku zaman lafiya da haƙuri da juna."
Da murmushi a kan fuskata na ce da su, "Amin-amin." Suka nufi hanyar fita na rako su ina yi musu godiya da Allah ya tsare.
Sai da suka fice gidan sannan na rufo ƙofar na juyo zuciyata a cunkushe da takaicin Mukhtar. Don da ya faɗa mini za su zo, dole ne a tanadar musu wani abu, saboda babu daɗi su tafi hannu rabbana ba a ba su komai ba.
Ko zama ban yi ba Maman TaufiÆ™ ta shigo na tarbe ta da fara'a muka zauna. Kallon tsarin falon ta shiga yi da kujeruna da muke kai, fuskarta a sake ta ce da ni,
"Kujerun nan sun yi mini kyau Maman Haidar!"
"Na gode" Na faÉ—a cike da murmushin da ya kasa barin fuskata. Zamanta ta gyara tana faÉ—in,
"Wasu mata na gani sun fito daga gidan nan suna ta yabonki. Kuma jikina ya ba ni kamar dangin amaryarsu ne?"
"E, su ne. Sun zo duba É—akin amarya da tsarin gidan."
"CabÉ—ijam! Lalle kin fara aika musu makaman nuclear. Domin kuwa da kunnena na ji wata yarinya daga cikinsu tana faÉ—in"
'Ni fa haushi ya hana ni tsayawa na fito gidan. Don wannan haÉ—aÉ—É—iyar mata ko ni aka haÉ—a kishi da ita an cuce ni balle Barira. CabÉ—i! Na tausaya wa mata gaskiya, don ta kawo kanta inda za a ga kasawarta'
'Idan ban da ma hali irin na maza da ba a iya musu; mai irin wannan zankaÉ—eÉ—iyar macen ne zai auri Barira?'
'Shi aure ai nufi ne na Allah! Ita ce matarsa shi ya sa ya nemo ta. Don haka ku zo mu je mu bi su da addu'ar zaman lafiya, saboda alamu ya nuna a fili ta yi sa'ar kishiyar da babu ruwanta'
Sanyin daɗi na ji ya tsirga mini, domin labarin da Maman Taufiƙ ta faɗa mini ba ƙaramin faranta zuciyata ya yi ba. Shiru kawai na yi ina ta murmushi, sai da ta yi 'yar kuwwar jin daɗi sannan ta sake cewa,
"A gaskiya Maman Haidar ke ƙwaro ce! A tashi guda kin hargitsa musu lissafi sun fita da ke a bakinsu."
Murmushi na yi mai sauti sannan na ce, "Ai shi yaƙi ɗan zamba ne, idan ba ka iya shi ba za ka sha wahalar kashe abokan gaba, kuma za a yi saurin gano maɓoyarka domin a kawo maka farmaki. Don haka ta wannan hanyar kaɗai zan iya rama abin da ake ƙoƙarin yi mini a fakaice. Saboda faɗa da tashin hankali ba zai kawo gyara ba, kuma ba zai sa a fasa abin da aka yi niyya ba. A ƙarshe ma biyu babu ake yi a rasa mutunci kuma a ɓarar da ƙima."
"Kai jama'a! Maman Haidar ke ta daban ce a cikin dubban mutane. Ban taɓa cin karo da macen da za a yi wa kishiya ta yi juriya irin taki ba. Wai don Allah da gaske ba kya jin komai a cikin ranki? Ni fa na kasa gasgata wannan lamari naki mai kama da almara."
Tambayar da ta yi mini ba ƙaramar dariya ta saka ni ba, saboda yanayin da ta yi maganar tamkar wata zautacciya. Sai da na gama dariyar sannan na ce da ita,
"Kowace mace tana da kalar nata kishin Maman Taufiƙ! Amma da a ce za a yi koyi da kalar kishin da magabata suka yi; Da mata da yawa ba su ɓarar da damar da Allah ya mallaka musu ba. Don sau da yawa namiji ba don ba ya son matarsa yake ƙara aure ba, ke wani lokaci ma ba ya ƙara ƙaunarki; har sai ya jera ki da wata ya gano akwai tazara a tsakaninki da sauran mata. Saboda haka da a ce za mu gane mu daina zafafa kishin maza idan za su ƙaro aure, da mun taimaki kanmu mun rage nauyin wahalar da muke ɗaukar wa kanmu a kan ɗa namiji. Ni kin ga ma a ranar da ya zo mini da zancen auren..."
Na kwashe duk yadda muka yi da Mukhtar na faɗa mata, dariya ta shiga sheƙawa har da riƙe ciki. Sai da ta gaji don kanta tana goge ƙwallar dariyar ta ce da ni,
"Wallahi ba ki da kirki Maman Haidar! Wannan tura haushin har ina saboda Allah?"
"Da a ce ban yi masa hakan ba, hauka zai siyo kasuwa ya manna mini ban ji ban gani ba. Saboda duk wani tashin hankalin da zan yi a lokacin; kai-tsaye zai ɗora shi a mizanin taɓin hankali. A ƙarshen ma zagina mutane za su dinga yi ba tare da sun yi duba da ƙunar da zuciyata ke yi, su tausaya mini ba."
"Wallahi zancenki gaskiya ne Maman Haidar! Amma kin san me? Ni ba zan iya wannan dauriyar ba. Allah kada ka jarrabe ni da irin wannan musibar mai wuyar shanyewa, don na san duk ranar da Amini ya sanar da ni zai yi aure; ba zan É—aga daga inda nake ba zan mutu."
😱cab!🤠Na yi nanðŸƒðŸ»â€â™€ï¸
D.AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*ASHIRIN DA TARA.*