Sashe 2
Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita ce ta fara jarumtar tsayar da ruwan hawayen da take yi ta shiga fyace majinar kukan da ta sha, ta janyo ƙafafuwanta ta zauna a bakin gado cikin sigar rarrashi ta ce "Idan ban da tausayin yaran nan da nake yi, me zai sa mu fuskanci baƙincikin rayuwa irin wannan? Ki yi haƙuri Zaituna na san ina sara miki ko babu gaɓa. Amma ki sani ni na san abin da ya sa ba na fatan ki kashe aurenki. Kuma ina roƙon Allah ya hana ki zama bazawara, domin ni kaɗai na san duhun baƙincikin da ke damfare cikin hakan. Ubangiji ya yi miki albarka, yadda kike yi mini biyayya ke ma Allah ya sa 'ya'yanki su yi miki fiye da hakan". Tana ƙare faɗar maganar ta miƙe tana ƙoƙarin ficewa daga ɗakin, na bi bayanta da kallo ina goge hawayen da suka kasa tsayawa cikin kwarmin idona. Kiciɓis suka yi da Mukhtar wanda yake ƙoƙarin shigowa ɗakin fuskarsa a haɗe tamkar bai taɓa dariya ba. Ganin ta ya sa shi sakin fuskar shi kaɗan ya rusuna har ƙasa yana sosa ƙeya cike da girmama ya ce "Umma daman magana nake so mu yi dangane da aikin nan da take zuwa. Ni dai gaskiya ban lamunta da shi ba, idan akwai yiyuwar ta daina zuwa duka a duba mini. Saboda zuwa aikin ne yanzu duk wata matsala take kunno kai tsakanina da ita, amma idan aka jingine shi kamar an yi maganin rabin matsalolin da ke faruwa daga wannan sai wannan". Shiru ya ratsa tsakani idona a kanta ina jiran amsar da za ta ba shi kafin na yi magana, domin na fuskanci nazarin maganganun shi da amsar da za ta bayar take yi. "A gaskiya Mukhtar sai dai ka yi haƙuri da zancen aikin nan, domin ka sani ban da wani iko a kan hana mata zuwa aikin nan. Amma tun da ba ka so kana da ikon da ya fi na kowa a kanta. Ka je ka samu Alhaji Ali domin ka sanar da shi a kai ƙarshen maganar, saboda shigar da kaina cikin maganar yanzu zai sake janyo wata sabuwar rigima tsakanina da shi. Wanda ba na fatar hakan an yi na baya ina fatar kuma ba za a yi maimaici ba". ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi ina aika masa harara da jajayen idanuwana tamkar su fito su manne jikin shi. Saboda tsabar takaicin da yake ba ni ji nake kamar na taso na rufe shi da duka. "Ba sai na je ba, a bar zancen kawai. Umma amma a sanar da ita babu ita babu wannan mayaudarin mutumin. Domin wallahi yanzu haka mutane har sun fara zunɗena a kan na zama mijin ho-ti-ho, saboda ganin yadda na kasa raba ta da mutumin da yake ƙoƙarin keta mata haddin aure..." "Wane aure kake zance? Kai har kana da bakin faɗar kana aurena? Na rantse da Allah darajar Umma kake ci, da tuni na watsa maka fetur na ƙone ka..."
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun!" Ita ce kalmar da Ummata ta furta cikin kiɗimewa da tashin hankalin da ya bayyana kan shi cikin fuskarta. "Gara da ta yi gabanki kika gani Umma, haka take yi mini ko a gaban su Haidar. Ba ta jin kunyar faɗa mini magana domin ta wulaƙanta ni a gabansu. Ban san wace irin tsana ce take yi mini ba da ba ta iya ɓoyewa ko a gaban waye..." "Ban ji daɗin maganar nan ba Zaituna, ki san me za ki faɗa wa mijinki saboda gudun shiga matsala da fushin Ubangiji". Nasiha ta shiga yi mini ina sharar hawaye, shi ma tana yi masa faɗan so-kanka a fakaice. Saboda har kullum tana jin nauyin shi da kunyar surukuntakar da ke tsakaninta da shi. Wadda ya dace a ce tuni ta watsar da ita ta huta, ko don kalolin cin amanar da yake yi mini. A gabana suka yi sallama ta fice ya dawo kaina yana ƙare mini kallon wulaƙanci sama da ƙasa, sannan ya yi ƙwafa ya fice tare da buga mini ƙofar ɗakin da ƙarfi kamar zai ɓalla ta.
Shin ya wannan rikicin yake ne? Kun hasko wani abu cikin labarin ko sai mun ƙara nutso a cikin tafiyar?.
D AUTA CE🚶
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA TA UKU.*
Ajiyar zuciya na sauke, sannan na yunƙura cikin rashin kuzari na sauko daga gadon. Ina layi na fice ɗakin saboda yunwar da ke ƙwaƙular cikina, kitchen na nufa kai-tsaye don jirin da nake ji ya tabbatar mini da ban samu waraka daga ciwon da ke damuna kwana biyu ba, wanda yake hana ni sukuni a duk lokacin da babu komai a cikina. Turus na yi na ja na tsaya gaban kayan shayinmu. Domin a take na gano Mukhtar ya yi abin da ya saba, saboda kofin da ya yi amfani da shi ma a nan ya bar shi bai ɗauke ba, kamar yadda ya bar gwangwanin madarar a buɗe bai rufe ba, bayan milon da ya barbazar a ƙasan tiles har ya yi danƙo, domin ba na tamtama a kan lokacin da zai zuba ya sha shayin ne ya zubar da shi, saboda halin shi da sani na sakankance komai ba ya yin sa a nutse sai ya yi hargitsi. Sau tari idan zai ci tuwo kafin ya tashi daga cin tuwon nan sai ya zubar da miyar. Idan fura ce kuma da wuya ya gama sha a kofi bai zubar da rabi ba.
Numfashi na ja tare da sauke ajiyar zuciya cikin ƙunar rai, a gurguje na ɗan gyara wurin sannan na ɗora ruwan zafi na haɗa tea. Saboda a yadda nake ji ba zan iya cin komai ba idan ba shi ba. Fitowa ta daga kitchen kenan ina ƙoƙarin komawa ɗaki, na ji muryar maƙociyata tana sallama, hakan ya tabbatar mini da Mukhtar ba ya cikin unguwar, domin a bin da na sani ne ba ta shigowa gidan sai ta tabbatar da ba ya nan, saboda tana cikin mutanen da yake zargin suna kawo mini tsegumin da yake haɗa mu rikici da shi a wasu lokutan. Na amsa mata sallama da disasshiyar muryata irin ta marasa lafiya. Tare muka nemi wurin zama a kan kujerun falon muka zauna, ina kurɓar shayin muka fara gaisawa babu yabo babu fallasa. Yanayin kallon da naga tana yi mini ya tabbatar min da akwai dalilin da ya kawo ta wurina, wanda ba na raba ɗaya biyu a kan rikicin da ya auku ne jiya. Wanda nake da tabbacin zuwa lokacin ya karaɗe ko'ina cikin unguwar da kewaye. Nan take na ji hawaye ya cika idanuwana, na ajiye ɗan sauran shayin da rage kan tebur, saboda zuciyata ta yi duhun da ba zan iya shanye shi ba.
"Ban samu wayarki ba, shi ya sa na kasa haƙuri sai da na yi wanann tattakin. Saboda ba na so Mukhtar ya gan ni ya yi mini abin da raina zai ɓaci a banza..." "Me ke tafe da ke?" Ita ce tambayar da na jefo mata tun kafin ta dire zancenta. Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce "Ban ji daɗin abin da ya faru ba, kuma ban ji daɗin irin zantukan da ake yi a kanki cikin unguwar nan ba" Ta ƙare maganar fuskarta ɗauke da damuwa, shiru na yi na ɗan lokaci sannan cikin muryar kuka na ce "Ban ga laifin duk wanda ya zage ni ba, domin abin zagin ya ji ko kuma ya gani shi ya sa ya zage ni. Idan akwai mai alhakin laifin hakan to ni ce nan. Domin da ban yi biyayyar da nake yi a yanzu ba, da duk hakan bai faru ba. Na sani babu biyayya wurin saɓa wa mahalicci, amma na zaɓi tauye kaina na ci amanar kaina saboda farincikin mahaifiyata. Na sani kuma Allah ma ya sani babu wani abu na assha tsakanina da MD illa gaisuwar mutuncin da muke yi. Amma ban san miye a cikin zuciyar shi dangane da ni ba, domin da ban ji abin da ya faɗa ba kai-tsaye zan ce da kowa sharri Mukhtar yake ƙoƙarin yi masa, sai dai kuma idan na yi duba da sanin darajar ɗan'adam irin na shi. Zan daki ƙirji na ce sai Allah ya isar masa a kan duk wanda ya zarge shi a kaina. Ban ji daɗin kashin kajin da ya shafa wa kansa ta dalilina, duba da mutumtakar shi ta fi ƙarfin kwatar ɗan sauran mutuncin da ya rage, wanda Mukhtar bai gama watsar mini ba. Ban taɓa ganin aure irin nawa ba a duniya, ina ma ban rayu ba har zuwa wannan lokacin da nake wannan maganar. Na tsani kaina kuma na tsani kowa ma a duniyar nan..."
Kuka na fashe da shi mai ƙarfi saboda ƙololon baƙincikin da ya tsaya mini a ƙahon zuci. Haƙuri ta fara ba ni, tana goge hawayen da na kula suna fareti saman fuskarta tun lokacin da na fara magana, sannan ta ce, "Idan ɓera da sata daddawa ma da warinta. Me ya kai ki shiga motarsa har ki bari ya kawo ki gida? A gaskiya dole Mukhtar ya ji haushin hakan, don ko ke ce kika gan shi da wata a mota za ki ji babu daɗi, shi ma da Allah ya halassta wa ya yi huɗu. Me ya sa ba ki hana kanki shiga motar ba tun a farkon tayin da ya yi miki? Ina da tabbacin da kin kauce wa wannan alfarma ta shi da kin tsira daga yamaɗiɗin da ake yi da ke. Yanzu wa gari ya waya? Ko fita kika yi za a nuna ki a ce ke ce, shin kin manta abin da ya faru baya kafin wannan? Haka za ki yi ta maimata laifi iri ɗaya wane kallo kike ganin mutane za su yi miki? Idan wancan gaskiyarki ta wanke ki, wannan kuma fa?"
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun!" Ita ce kalmar da Ummata ta furta cikin kiɗimewa da tashin hankalin da ya bayyana kan shi cikin fuskarta. "Gara da ta yi gabanki kika gani Umma, haka take yi mini ko a gaban su Haidar. Ba ta jin kunyar faɗa mini magana domin ta wulaƙanta ni a gabansu. Ban san wace irin tsana ce take yi mini ba da ba ta iya ɓoyewa ko a gaban waye..." "Ban ji daɗin maganar nan ba Zaituna, ki san me za ki faɗa wa mijinki saboda gudun shiga matsala da fushin Ubangiji". Nasiha ta shiga yi mini ina sharar hawaye, shi ma tana yi masa faɗan so-kanka a fakaice. Saboda har kullum tana jin nauyin shi da kunyar surukuntakar da ke tsakaninta da shi. Wadda ya dace a ce tuni ta watsar da ita ta huta, ko don kalolin cin amanar da yake yi mini. A gabana suka yi sallama ta fice ya dawo kaina yana ƙare mini kallon wulaƙanci sama da ƙasa, sannan ya yi ƙwafa ya fice tare da buga mini ƙofar ɗakin da ƙarfi kamar zai ɓalla ta.
Shin ya wannan rikicin yake ne? Kun hasko wani abu cikin labarin ko sai mun ƙara nutso a cikin tafiyar?.
D AUTA CE🚶
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA TA UKU.*
Ajiyar zuciya na sauke, sannan na yunƙura cikin rashin kuzari na sauko daga gadon. Ina layi na fice ɗakin saboda yunwar da ke ƙwaƙular cikina, kitchen na nufa kai-tsaye don jirin da nake ji ya tabbatar mini da ban samu waraka daga ciwon da ke damuna kwana biyu ba, wanda yake hana ni sukuni a duk lokacin da babu komai a cikina. Turus na yi na ja na tsaya gaban kayan shayinmu. Domin a take na gano Mukhtar ya yi abin da ya saba, saboda kofin da ya yi amfani da shi ma a nan ya bar shi bai ɗauke ba, kamar yadda ya bar gwangwanin madarar a buɗe bai rufe ba, bayan milon da ya barbazar a ƙasan tiles har ya yi danƙo, domin ba na tamtama a kan lokacin da zai zuba ya sha shayin ne ya zubar da shi, saboda halin shi da sani na sakankance komai ba ya yin sa a nutse sai ya yi hargitsi. Sau tari idan zai ci tuwo kafin ya tashi daga cin tuwon nan sai ya zubar da miyar. Idan fura ce kuma da wuya ya gama sha a kofi bai zubar da rabi ba.
Numfashi na ja tare da sauke ajiyar zuciya cikin ƙunar rai, a gurguje na ɗan gyara wurin sannan na ɗora ruwan zafi na haɗa tea. Saboda a yadda nake ji ba zan iya cin komai ba idan ba shi ba. Fitowa ta daga kitchen kenan ina ƙoƙarin komawa ɗaki, na ji muryar maƙociyata tana sallama, hakan ya tabbatar mini da Mukhtar ba ya cikin unguwar, domin a bin da na sani ne ba ta shigowa gidan sai ta tabbatar da ba ya nan, saboda tana cikin mutanen da yake zargin suna kawo mini tsegumin da yake haɗa mu rikici da shi a wasu lokutan. Na amsa mata sallama da disasshiyar muryata irin ta marasa lafiya. Tare muka nemi wurin zama a kan kujerun falon muka zauna, ina kurɓar shayin muka fara gaisawa babu yabo babu fallasa. Yanayin kallon da naga tana yi mini ya tabbatar min da akwai dalilin da ya kawo ta wurina, wanda ba na raba ɗaya biyu a kan rikicin da ya auku ne jiya. Wanda nake da tabbacin zuwa lokacin ya karaɗe ko'ina cikin unguwar da kewaye. Nan take na ji hawaye ya cika idanuwana, na ajiye ɗan sauran shayin da rage kan tebur, saboda zuciyata ta yi duhun da ba zan iya shanye shi ba.
"Ban samu wayarki ba, shi ya sa na kasa haƙuri sai da na yi wanann tattakin. Saboda ba na so Mukhtar ya gan ni ya yi mini abin da raina zai ɓaci a banza..." "Me ke tafe da ke?" Ita ce tambayar da na jefo mata tun kafin ta dire zancenta. Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce "Ban ji daɗin abin da ya faru ba, kuma ban ji daɗin irin zantukan da ake yi a kanki cikin unguwar nan ba" Ta ƙare maganar fuskarta ɗauke da damuwa, shiru na yi na ɗan lokaci sannan cikin muryar kuka na ce "Ban ga laifin duk wanda ya zage ni ba, domin abin zagin ya ji ko kuma ya gani shi ya sa ya zage ni. Idan akwai mai alhakin laifin hakan to ni ce nan. Domin da ban yi biyayyar da nake yi a yanzu ba, da duk hakan bai faru ba. Na sani babu biyayya wurin saɓa wa mahalicci, amma na zaɓi tauye kaina na ci amanar kaina saboda farincikin mahaifiyata. Na sani kuma Allah ma ya sani babu wani abu na assha tsakanina da MD illa gaisuwar mutuncin da muke yi. Amma ban san miye a cikin zuciyar shi dangane da ni ba, domin da ban ji abin da ya faɗa ba kai-tsaye zan ce da kowa sharri Mukhtar yake ƙoƙarin yi masa, sai dai kuma idan na yi duba da sanin darajar ɗan'adam irin na shi. Zan daki ƙirji na ce sai Allah ya isar masa a kan duk wanda ya zarge shi a kaina. Ban ji daɗin kashin kajin da ya shafa wa kansa ta dalilina, duba da mutumtakar shi ta fi ƙarfin kwatar ɗan sauran mutuncin da ya rage, wanda Mukhtar bai gama watsar mini ba. Ban taɓa ganin aure irin nawa ba a duniya, ina ma ban rayu ba har zuwa wannan lokacin da nake wannan maganar. Na tsani kaina kuma na tsani kowa ma a duniyar nan..."
Kuka na fashe da shi mai ƙarfi saboda ƙololon baƙincikin da ya tsaya mini a ƙahon zuci. Haƙuri ta fara ba ni, tana goge hawayen da na kula suna fareti saman fuskarta tun lokacin da na fara magana, sannan ta ce, "Idan ɓera da sata daddawa ma da warinta. Me ya kai ki shiga motarsa har ki bari ya kawo ki gida? A gaskiya dole Mukhtar ya ji haushin hakan, don ko ke ce kika gan shi da wata a mota za ki ji babu daɗi, shi ma da Allah ya halassta wa ya yi huɗu. Me ya sa ba ki hana kanki shiga motar ba tun a farkon tayin da ya yi miki? Ina da tabbacin da kin kauce wa wannan alfarma ta shi da kin tsira daga yamaɗiɗin da ake yi da ke. Yanzu wa gari ya waya? Ko fita kika yi za a nuna ki a ce ke ce, shin kin manta abin da ya faru baya kafin wannan? Haka za ki yi ta maimata laifi iri ɗaya wane kallo kike ganin mutane za su yi miki? Idan wancan gaskiyarki ta wanke ki, wannan kuma fa?"