Sashe 63
Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun da muka doshi ƙofar gidan na ji ƙirjina yana dakan luguden uku-uku, saboda har raina ba na farinciki da kwashe kayan da muke ƙoƙarin yi. In da ta ni za a bi sai an jira idan ya sake ni sannan a kwashe kayan, duk da ba na zaton zan sake zama gidan amma kuma ba na so mu yi wahala a banza.
Kasancewar ina da makullin gidan a jikin na ɗakina, da na ƙofar falo tare da wadrobe ɗin da nake ajiyar wasu kayana a kitchen. Hakan ya sa ba mu sha wuyar shiga gidan ba duk da yake ƙargame, alamun masu gidan ba su ciki.
Da mamaki muka isa tsakiyar gidan, saboda ganin komai kaca-kaca tamkar an yi yaƙi. Ko'ina kwanoni da kofuna warwatse bayan tukunyoyin da aka jera kowace an yi girki da ita an ƙi wankewa.
Ganin murhu da itace ajiye tsakar a gidan, hakan ya sa na gano da shi Barira take girki. Falon muka kutsa kai babu shiri na zaro ido waje, saboda ganin an dawo da kujeruna inda aka ajiye na Barira. Sannan babu nata ko É—aya a falon sai nawa da aka maye gurbin nata da su.
Kasancewar mai motar tare yake da waÉ—anda za su taimaka masa, na ba su umurnin su fitar da kujerun waje su saka mota. Sannan na buÉ—e É—akina Inna Kulu tana faÉ—in,
"Ita wannan amarya halan ɗiyar wane hamshaƙi ce a garin nan?"
"Me kika gani?"
Tambayar da na yi mata kenan ina tura ƙofar ɗakina da na buɗe ina 'yar dariya.
"Na ga gidan kamar ba ta san miye shara ba balle wanke-wanke!"
Ɗakin muka shiga ina faɗin, "Matar so ai ba za a auro ta don wahala ba. Da dai a ce shi ɗin ba son jiki ne da shi ba, da sai ya dingà gyara mata komai su huta da ƙazanta."
"Ikon Allà h!"
Inna Kulu ta faɗa tana ƙoƙarin cire labulen ɗakin, na yi 'yar dariya sannan na ce,
"To wallahi in dai Mukhtar ne har tsutsotsi sai kayanta sun yi ba tare da ya ɗaga su daga inda suke ba, balle ya kawar da su a ji daɗi. Saboda duk lokacin da na je Kebbi, na sha dawowa garin nan na tarar da kwanonina ko wata kulata da tsutsotsi suna gwazarniya. Saboda ba ya iya ɗauke kwano a inda ya ci abinci, haka ma ba ya iya wankewa sai dai ya nemo wani ya ƙara ɓatawa. Gidan nan kuma tamkar an yi yaƙi a cikinsa don komai sai na gani, tsakanin kwalayen tabar da yake Sha, gwangwanin maltina da ledodin ruwan pure water. Wasu ma an sha rabi an ajiye, wasu kuma ajiya ta sa sun fashe da kansu, sai tarin takardu da mujallun da yake bita tamkar wani furofesa."
"Cabɗijam!" Inna Kulu ta faɗa tana riƙe da gemunta, fuskarta cike da mamakin maganganun da na faɗa. Umma tana fito da kayan wadrobe ɗita ta ce,
"Ai duk wanda ya zauna da Mukhtar dole ne a yi masa sannu, kamar yadda ake yi wa mara lafiya idan an je ganin sa. Don zama da shi babban ciwo ne mai zaman kansa, wanda babu maganinsa matuƙar ba rabuwa aka yi da shi ba!"
Ina dariya na ce, "Wallahi ko kashi ya yi ba ya flooshing Umma, haka zai cika masai abinsa ya wanke jikinsa ya fito. Tun ina zuba ruwa cikin mutunci ba na damuwa har na fara jin haushinsa ina masa ƙorafi. Amma wallahi bai daina ba, don sai ya gama wankansa ya fita idan na shiga toilet ɗin na taras da kashin zanƙare cikin kwalbar masan. Dole ba don na so ba nake zuba ruwa na wanke toilet ɗin ina gunguni. Allah bai raba ni da matsalarsa ba har sai da muka dawo gidan nan."
"Wannan ai ƙazanta ce wallahi! Amma idan kika gan shi fes-fes da shi kamar bai san wani abu ƙazanta ba." Cewar Inna Kulu kenan suna ƙoƙarin ɓalle gado bayan an fitar da katifu. Dariya na fashe da ita ina faɗin,
"To wallahi Inna har da majina yake kaftawa ƙasan toilet ɗin sai na zo takawa na ji santsinta ya kwashe ni. Sannan ko a gidan nan haka yake duk da ɗakinsa daban nawa daban, amma warin da toilet ɗinsa yake yi wani lokaci har cikin falon nan gabaɗaya gamewa yake. Saboda ba ya flooshing tsawon kwanaki, warin kashin ya haɗe da warin tabarsa wuri ɗaya, ana tura kai ɗakinsa dole sai an fito ana toshe hanci. Da ƙyar na samu ya daina rashin zuba ruwa ko shi sai da na fara yi masa gorin; a gan shi a hanya tsaf-tsaf! Ɗakinsa kamar shekar ɓeraye. A haka nake ta jifar sa da maganganun da zai suke sa yana jin haushi har ya gyara dolensa. Saboda na yi iya ƙoƙarina wurin ci gaba da wanke masa toilet ɗin amma na kasa, Ummu Salma ma da nake sakawa tana wanke masa, duk ranar da ta yi aikin ƙyanƙyaminta nake yi ko kusa da ni hana ta zuwa nake yi."
"Tsakani da Allah ko nawa za a ba ni ba zan iya zama da Mukhtar ba!" Umma ta faɗa tana buɗe window ta furzar da yawu tana yatsina fuska. Dariya ta suɓuce mini na ce,
"Ai yanzu ya daina, yana wanke kayansa amma fa wallahi ba koyaushe yake flooshing ba. Saboda ɗabi'ar ta bi jikinsa ba ya iya aikin komai sai ci da kwanciya. Amma shara ma idan ba an yi sa'a ya bar ɗakinsa a buɗe mun share masa ba; sai ya fi ƙarfin wata ɗaya har biyu bai nemi a gyara masa ko ya gyara da kansa ba. Amma babu laifi sharar ma yanzu yana yi da kansa idan ya gaji da zama cikin datti."
"Wannan kuma kin fi shi laifi gaskiya! Don ke ya dace a ce kullum kina share masa É—akin, ko da ba za ki yi hidimar kashinsa ba!" Umma ta faÉ—a tana haÉ—e fuska, sannan ta fitar da hanjin gadon waje ta dawo. Cikin sanyin jiki na ce da ita,
"Ai ke Umma a baya yana barin É—akin buÉ—e ya tafiyarsa, amma yanzu kullum rufewa yake yi sai an ci sa'a yake barin shi buÉ—e ya fita. Ko na ce ya ba da makulli a buÉ—e É—akin a share masa, sai ya ce a bar masa kayansa haka nan sai ya tashi."
"To wannan kam daga ke har shi kuna da laifi! Tun da ba makulli ɗaya ba ne sai ki zari wani ki ɓoye. Duk lokacin da ya fita sai ki buɗe ki share masa ɗakin ki mayar ki rufe. Saboda irin Mukhtar ko haƙƙin kansa ma ba ya iya saukewa balle na abokin zamansa. Don wallahi a yadda yaken nan ko dabba aka ba shi kiwo sai ta mutu bai san ta mutu na, saboda rashin kulawa balle ɗan mutum mai buƙatu da yawa. Allah dai ya sauya miki da alheri, amma shi kam ba mijin aure ba ne ga duk macen da ta san ciwon kanta."
Ta ƙare maganar tana goge gumin fuskarta, Inna Kulu ta yi tsaki sannan ta ce, "Ni fa tun inda lamarinsa ya fara ba ni tsoro; da na ji ta ce duk inda za ta je a faɗin garin nan don ta daɗe ba zai neme ta ba. Haka ma idan ta dawo ba zai tambaya ya ji lafiya ba, wannan ai ba aure ba ne kuma rashin sanin ciwon kai ne kawai wallahi. Na ga ni nan tsohuwa ce ba yarinya ba, amma idan fita ta kama ni Sale ya dingà shimfiɗa mini dokoki kenan. Idan ma na yi fitar waya bisa waya a kan na dawo, hankalinsa ba zai kwanta ba har sai ya ga na dawo gidan nan na zauna."
Umma ta riga ni faɗar maganar da nake ƙoƙarin fitarwa a bakina, ta yi hanzarin cewa da ita,
"To ai shi Salenmu na daban ne kowa ma ya sani wallahi."
Inna Kulu tana dariya ta ce,
"Daman can aikinku kenan kuri da nuna kun fi kowa iya zaman aure!"
"Kin dai ga zahiri don ke ma kin san ba kowane namiji ne irin Salenmu ba!"
Umma ta faɗa kanta tsaye, Inna Kulu ta riƙe baki tana kallon ta murmushi a kan fuskarta bakinta ya ƙi rufuwa, saboda ta san gaskiya ce Umma ta faɗa. Don ni kaina rayuwar Kawu Sale tana burge ni matuƙa, musamman da bai haɗa komai da Inna Kulu ba. A gaban kowa yana iya nuna mata ƙauna da kulawa babu ruwansa da sun tsufa, ko 'ya'ya da jikoki ba za su saka shi jin nauyin ɗaura mata ɗankwali ba, ko kuma ya kakkaɓe mata ƙurar hayaƙi a saman kai idan ya ga ta ɓata mata jiki. Nama ma idan ya siyo wani lokaci idan ya ɗauki yanka ɗaya kafin a raba ya ci, to ita ma sai ya ɗauki ɗaya ya kai mata a baki, mu yi ta dariya.
Zancen Inna Kulun ne ya katse mini tunanin rayuwar aurensu mai É—auke da kulawa tare da fahimtar juna.
"Tabbas! Sale mutum ne, don ko ina zan iya bugun ƙirji na ce na yi sa'ar aure. Don duk macen da mijinta bai damu da yawan fitar da take yi ba; gaskiya yana da rangwamen ƙaunarta. Saboda ke kanki macen da kike tambayar fitar kullum yana barin ki babu musu, wallahi watarana sai kin ji wani iri, matuƙar kin san kanki."
Dariya na fashe da ita ina faɗin, "Zancenki haka yake Inna! Saboda ni kaina haushi nake ji a lokacin da nake tambayarsa fita. Wani lokaci ma ba ya bari na kai ƙarshen zancen balle na faɗi abin da zai kai ni; yake cewa da ni sai kin dawo. Watarana ma idan na ji haushi na ce, wai kai ba za ka ce da ni ban zuwa ba, kullum da na faɗa ko bakina ba na rufewa kake cewa sai na dawo. Sai ya ce idan tafiyar ce ba na so na yi zamana kawai, ya fita ya bar ni cike da mamakin murɗaɗɗen halinsa."
"Ai duk macen da ke tambayar fita koyaushe a ce mata tafi, ba ta yi sa'a ba. Gara a dingà nuna miki iko da isa a wasu lokutan. Ta hakan kike gane an damu da ke, kuma ana kishinki."
Kasancewar ina da makullin gidan a jikin na ɗakina, da na ƙofar falo tare da wadrobe ɗin da nake ajiyar wasu kayana a kitchen. Hakan ya sa ba mu sha wuyar shiga gidan ba duk da yake ƙargame, alamun masu gidan ba su ciki.
Da mamaki muka isa tsakiyar gidan, saboda ganin komai kaca-kaca tamkar an yi yaƙi. Ko'ina kwanoni da kofuna warwatse bayan tukunyoyin da aka jera kowace an yi girki da ita an ƙi wankewa.
Ganin murhu da itace ajiye tsakar a gidan, hakan ya sa na gano da shi Barira take girki. Falon muka kutsa kai babu shiri na zaro ido waje, saboda ganin an dawo da kujeruna inda aka ajiye na Barira. Sannan babu nata ko É—aya a falon sai nawa da aka maye gurbin nata da su.
Kasancewar mai motar tare yake da waÉ—anda za su taimaka masa, na ba su umurnin su fitar da kujerun waje su saka mota. Sannan na buÉ—e É—akina Inna Kulu tana faÉ—in,
"Ita wannan amarya halan ɗiyar wane hamshaƙi ce a garin nan?"
"Me kika gani?"
Tambayar da na yi mata kenan ina tura ƙofar ɗakina da na buɗe ina 'yar dariya.
"Na ga gidan kamar ba ta san miye shara ba balle wanke-wanke!"
Ɗakin muka shiga ina faɗin, "Matar so ai ba za a auro ta don wahala ba. Da dai a ce shi ɗin ba son jiki ne da shi ba, da sai ya dingà gyara mata komai su huta da ƙazanta."
"Ikon Allà h!"
Inna Kulu ta faɗa tana ƙoƙarin cire labulen ɗakin, na yi 'yar dariya sannan na ce,
"To wallahi in dai Mukhtar ne har tsutsotsi sai kayanta sun yi ba tare da ya ɗaga su daga inda suke ba, balle ya kawar da su a ji daɗi. Saboda duk lokacin da na je Kebbi, na sha dawowa garin nan na tarar da kwanonina ko wata kulata da tsutsotsi suna gwazarniya. Saboda ba ya iya ɗauke kwano a inda ya ci abinci, haka ma ba ya iya wankewa sai dai ya nemo wani ya ƙara ɓatawa. Gidan nan kuma tamkar an yi yaƙi a cikinsa don komai sai na gani, tsakanin kwalayen tabar da yake Sha, gwangwanin maltina da ledodin ruwan pure water. Wasu ma an sha rabi an ajiye, wasu kuma ajiya ta sa sun fashe da kansu, sai tarin takardu da mujallun da yake bita tamkar wani furofesa."
"Cabɗijam!" Inna Kulu ta faɗa tana riƙe da gemunta, fuskarta cike da mamakin maganganun da na faɗa. Umma tana fito da kayan wadrobe ɗita ta ce,
"Ai duk wanda ya zauna da Mukhtar dole ne a yi masa sannu, kamar yadda ake yi wa mara lafiya idan an je ganin sa. Don zama da shi babban ciwo ne mai zaman kansa, wanda babu maganinsa matuƙar ba rabuwa aka yi da shi ba!"
Ina dariya na ce, "Wallahi ko kashi ya yi ba ya flooshing Umma, haka zai cika masai abinsa ya wanke jikinsa ya fito. Tun ina zuba ruwa cikin mutunci ba na damuwa har na fara jin haushinsa ina masa ƙorafi. Amma wallahi bai daina ba, don sai ya gama wankansa ya fita idan na shiga toilet ɗin na taras da kashin zanƙare cikin kwalbar masan. Dole ba don na so ba nake zuba ruwa na wanke toilet ɗin ina gunguni. Allah bai raba ni da matsalarsa ba har sai da muka dawo gidan nan."
"Wannan ai ƙazanta ce wallahi! Amma idan kika gan shi fes-fes da shi kamar bai san wani abu ƙazanta ba." Cewar Inna Kulu kenan suna ƙoƙarin ɓalle gado bayan an fitar da katifu. Dariya na fashe da ita ina faɗin,
"To wallahi Inna har da majina yake kaftawa ƙasan toilet ɗin sai na zo takawa na ji santsinta ya kwashe ni. Sannan ko a gidan nan haka yake duk da ɗakinsa daban nawa daban, amma warin da toilet ɗinsa yake yi wani lokaci har cikin falon nan gabaɗaya gamewa yake. Saboda ba ya flooshing tsawon kwanaki, warin kashin ya haɗe da warin tabarsa wuri ɗaya, ana tura kai ɗakinsa dole sai an fito ana toshe hanci. Da ƙyar na samu ya daina rashin zuba ruwa ko shi sai da na fara yi masa gorin; a gan shi a hanya tsaf-tsaf! Ɗakinsa kamar shekar ɓeraye. A haka nake ta jifar sa da maganganun da zai suke sa yana jin haushi har ya gyara dolensa. Saboda na yi iya ƙoƙarina wurin ci gaba da wanke masa toilet ɗin amma na kasa, Ummu Salma ma da nake sakawa tana wanke masa, duk ranar da ta yi aikin ƙyanƙyaminta nake yi ko kusa da ni hana ta zuwa nake yi."
"Tsakani da Allah ko nawa za a ba ni ba zan iya zama da Mukhtar ba!" Umma ta faɗa tana buɗe window ta furzar da yawu tana yatsina fuska. Dariya ta suɓuce mini na ce,
"Ai yanzu ya daina, yana wanke kayansa amma fa wallahi ba koyaushe yake flooshing ba. Saboda ɗabi'ar ta bi jikinsa ba ya iya aikin komai sai ci da kwanciya. Amma shara ma idan ba an yi sa'a ya bar ɗakinsa a buɗe mun share masa ba; sai ya fi ƙarfin wata ɗaya har biyu bai nemi a gyara masa ko ya gyara da kansa ba. Amma babu laifi sharar ma yanzu yana yi da kansa idan ya gaji da zama cikin datti."
"Wannan kuma kin fi shi laifi gaskiya! Don ke ya dace a ce kullum kina share masa É—akin, ko da ba za ki yi hidimar kashinsa ba!" Umma ta faÉ—a tana haÉ—e fuska, sannan ta fitar da hanjin gadon waje ta dawo. Cikin sanyin jiki na ce da ita,
"Ai ke Umma a baya yana barin É—akin buÉ—e ya tafiyarsa, amma yanzu kullum rufewa yake yi sai an ci sa'a yake barin shi buÉ—e ya fita. Ko na ce ya ba da makulli a buÉ—e É—akin a share masa, sai ya ce a bar masa kayansa haka nan sai ya tashi."
"To wannan kam daga ke har shi kuna da laifi! Tun da ba makulli ɗaya ba ne sai ki zari wani ki ɓoye. Duk lokacin da ya fita sai ki buɗe ki share masa ɗakin ki mayar ki rufe. Saboda irin Mukhtar ko haƙƙin kansa ma ba ya iya saukewa balle na abokin zamansa. Don wallahi a yadda yaken nan ko dabba aka ba shi kiwo sai ta mutu bai san ta mutu na, saboda rashin kulawa balle ɗan mutum mai buƙatu da yawa. Allah dai ya sauya miki da alheri, amma shi kam ba mijin aure ba ne ga duk macen da ta san ciwon kanta."
Ta ƙare maganar tana goge gumin fuskarta, Inna Kulu ta yi tsaki sannan ta ce, "Ni fa tun inda lamarinsa ya fara ba ni tsoro; da na ji ta ce duk inda za ta je a faɗin garin nan don ta daɗe ba zai neme ta ba. Haka ma idan ta dawo ba zai tambaya ya ji lafiya ba, wannan ai ba aure ba ne kuma rashin sanin ciwon kai ne kawai wallahi. Na ga ni nan tsohuwa ce ba yarinya ba, amma idan fita ta kama ni Sale ya dingà shimfiɗa mini dokoki kenan. Idan ma na yi fitar waya bisa waya a kan na dawo, hankalinsa ba zai kwanta ba har sai ya ga na dawo gidan nan na zauna."
Umma ta riga ni faɗar maganar da nake ƙoƙarin fitarwa a bakina, ta yi hanzarin cewa da ita,
"To ai shi Salenmu na daban ne kowa ma ya sani wallahi."
Inna Kulu tana dariya ta ce,
"Daman can aikinku kenan kuri da nuna kun fi kowa iya zaman aure!"
"Kin dai ga zahiri don ke ma kin san ba kowane namiji ne irin Salenmu ba!"
Umma ta faɗa kanta tsaye, Inna Kulu ta riƙe baki tana kallon ta murmushi a kan fuskarta bakinta ya ƙi rufuwa, saboda ta san gaskiya ce Umma ta faɗa. Don ni kaina rayuwar Kawu Sale tana burge ni matuƙa, musamman da bai haɗa komai da Inna Kulu ba. A gaban kowa yana iya nuna mata ƙauna da kulawa babu ruwansa da sun tsufa, ko 'ya'ya da jikoki ba za su saka shi jin nauyin ɗaura mata ɗankwali ba, ko kuma ya kakkaɓe mata ƙurar hayaƙi a saman kai idan ya ga ta ɓata mata jiki. Nama ma idan ya siyo wani lokaci idan ya ɗauki yanka ɗaya kafin a raba ya ci, to ita ma sai ya ɗauki ɗaya ya kai mata a baki, mu yi ta dariya.
Zancen Inna Kulun ne ya katse mini tunanin rayuwar aurensu mai É—auke da kulawa tare da fahimtar juna.
"Tabbas! Sale mutum ne, don ko ina zan iya bugun ƙirji na ce na yi sa'ar aure. Don duk macen da mijinta bai damu da yawan fitar da take yi ba; gaskiya yana da rangwamen ƙaunarta. Saboda ke kanki macen da kike tambayar fitar kullum yana barin ki babu musu, wallahi watarana sai kin ji wani iri, matuƙar kin san kanki."
Dariya na fashe da ita ina faɗin, "Zancenki haka yake Inna! Saboda ni kaina haushi nake ji a lokacin da nake tambayarsa fita. Wani lokaci ma ba ya bari na kai ƙarshen zancen balle na faɗi abin da zai kai ni; yake cewa da ni sai kin dawo. Watarana ma idan na ji haushi na ce, wai kai ba za ka ce da ni ban zuwa ba, kullum da na faɗa ko bakina ba na rufewa kake cewa sai na dawo. Sai ya ce idan tafiyar ce ba na so na yi zamana kawai, ya fita ya bar ni cike da mamakin murɗaɗɗen halinsa."
"Ai duk macen da ke tambayar fita koyaushe a ce mata tafi, ba ta yi sa'a ba. Gara a dingà nuna miki iko da isa a wasu lokutan. Ta hakan kike gane an damu da ke, kuma ana kishinki."