Sashe 42
Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ina gamawa na share gidan fes sannan na wanke kayan da aka ɓata, na ɓoye wasu kayana. Wanka na faɗa na shirya cikin shigar da ni kaina na san na yi kyau. Sallamar su Sajida da na jiyo na fito daga ɗakin ina zuba ƙamshi da murmushi a kan fuskata. Sajida da Mamarta na hango, sai wasu yayun Mukhtar na 'yan'uwa tare da yaransu.
Gaisawa muka fara yi da su babu yabo babu fallasa sannan na zauna. Sajida ta fara koÉ—a ni bakinta a sake take ta yabon kwalliyata, ina hankalce da Mamarta tana aika mata harara ta gefen ido.
Ganin ba za ta daina rawar ƙafar da take yi da ni ba ta miƙe tana faɗin,
"Abincin masu jere za mu dafa. A fito mana da tukanen girkin mu je mu yi abin da ya kawo mu."
Na miƙe tare da kiran Sajida da wasu yaran da suka zo da su muka nufi kitchen. A nan muka fito da manyan tukanena da murhu biyu, tare da wasu kayan da za a buƙata duka muka fitar da su a tsakar gidan.
Ina ƙoƙarin shige falo na ji ihun yara suna faɗin ga motar kayan amarya nan ta iso. Dam-dam! Na ji dakan lugude a tsakiyar zuciyata, da murmushin yaƙe na zauna falo ina kiran lambar Firdausi.
Bayan ta É—auka nake sanar da ita Mukhtar zai yi aure yau ake gyaran É—aki,
"Ai na É—auka ba za ki faÉ—a mini ba har sai an kawo amaryar mu zo ganin ta."
"Kwantas Hajiya! Ni ma daga sama na tsinci zancen auren. Don haka gobe ki fito ku danne mini ƙirjina."
Na ƙare maganar a daidai lokacin da ake shigo da kayan gadon amarya ana shigar da su ɗakinta. Miƙewa na yi na koma ɗakina, mayafi na ɗauko mahaɗin kayan na saka, sannan na rufe ɗakin da key na yi wa matan da ke shigowa sannu da zuwa.
Na fice tsakar gidan bayan jikina ya ba ni shaidar kallon da dangin amaryar suke yi mini. Maman TaufiÆ™ na kira a waya na ce ta fito ga aikin an kawo mana har gida.
Hannu na saka ina taya su aikin ba tare da na damu da kallon mamakin da Yayunsa suke yi mini ba. Na dinga jan Sajida da hira muna dariyar da iyakacinta kan fuskata, saboda ina so na nuna wa kowa ba na baƙinciki da auren a zahiri.
Ko da Maman Taufiƙ ta shigo har mun fara cin ƙarfin aikin, tare da ita aka dafa jallop ɗin shinkafa. Sannan aka yi musu tuwon da za su je da shi gida bayan jinjer drink.
Najib mai adaidatana na kira a waya ya siyo mana ƙanƙara da nufin idan ya zo na ba shi kuɗin. Babu ɓata lokaci ya siyo mini ya kawo na biya shi, aka baza ta cikin jinjar da aka shaƙe kula biyu da ƙullinta.
Muna tsaka da haɗa kayan Mukhtar ya shigo gidan ya kira Mamar Sajida, wasu manyan ledodi biyu ya miƙa mata yana faɗin,
"Don Allah a saka musu yadda na bayar kada a bari a taɓa musu komai."
Ban bari na sake kallon inda yake ba ma balle abin da yake faɗin kada a taɓa. Sajida kawai ta kira tana faɗin ta samo wata kula a kitchen a saka musu naman kajin a ciki.
Shock na yi da jin maganar kajin, nan take raina ya ɓaci ta yadda har na kasa ɓoye damuwa a kan fuskata. Miƙewa na yi ina faɗin,
"Bari na kawo miki don kulolin suna É—akina kuma na rufe."
Ba ƙaramar jarumta na yi wurin haɗa kalmomin ba, saboda muryar kuka da ke ƙoƙarin tona asirin zuciyata. Toilet na shige na yi kukan rabin lokaci, sannan na wanke fuskata na fito na ƙara goga mai na bi da 'yar hoda sama.
Kulolin na ɗauko a cikin durowar Kitchen ɗina da na kulle da makulli. Sannan na rufe ina ƙoƙarin ɗagowa na ga Sajida a saman kaina, murmushi ta yi mini tana ƙoƙarin goge hawayen fuskarta ta ce,
"Ki yi haƙuri Aunty! Duk da na san ba a kyauta miki. Amma kuma hakan ba zai hana na ba ki haƙurin ba, don na fahimci ba ki ji daɗin abin da Baba Mukhtar ya ce ba."
"Kada ki damu! Na saba da halinsa ko kaɗan ban ji komai a kan zancensa ba. Kuma ai yana da gaskiya, idan ba mu ƙara ba ba zai yiyu mu rage musu ba."
Ina ƙare faɗar hakan muka fito kitchen ɗin muka koma tsakar gidan. A nan na ji Mamar Sajidar sun haɗa kai da wata 'yar'uwarsu, suna ta gulmar kayan ɗakin amarya.
"Ni fa ina ganin kamar ba sababbi ba ne fenti ne."
"Da gaskiyarki Maimuna! Don ko kujerun gyaransu aka yi ba sabon katako ba ne."
Murmushi na yi mai sauti sannan na matso kusa da su na ce,
"Kaya ba su ne aure ba Yaya Maimuna, ku yi musu fatan zaman lafiya sai ya fi yi da sun da kuke yi."
Kallon juna suka fara yi a muzance, kafin Yaya Maimunar ta ja kular da Sajida ta ajiye gefenta tana faÉ—in,
"Iyayi ne fa saka suruka makarantar boko. Tun da ya samu mai son sa tsakani da Allah ko yau ya mutu ya bar tarihi. Don ya ƙwaci wuyan hannunsa daga muguwar damƙar da aka yi masa."
Murmushi kawai na yi mata na bar wurin, saboda idon Sajida da ke kanmu. Kuma na tabbatar da duk abin da zan faɗa a wannan lokacin ba mai daɗi ba ne, kuma dole sai ta ji zafi domin ba zan yi ƙasa a gwiwa wurin rama daidai abin da ta faɗa mini ba, wataƙila ma na zarce awa wurin ƙoƙarin mayar da raddin na ci zarafinta a banza wofi."
Hmmmmm! Shiru ma ai magana ce Zaituna.😢
D.AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA TALATIN.*
Abincin Sajida ta zuba mana a ƙaton tire, ni da ita da Maman Taufik muka yi ɗakina. Yayin da muka bar Yaya Maimuna da sauran dangin Mukhtar a nan suna cin nasu.
Muna ɗakina muna ta hira bayan mun gama cin abincin. Ban san ya aka ƙare da 'yan jeren ba, har sai da suka zo ƙofar ɗakina suna yi mini godiya, tare da sallama a kan sun ƙare za su tafi.
Sauka lafiya na yi musu a bakin ƙofar ɗakin ban fita ba, a gabana suka fice ɗauke da kulolin abincin da aka ba su. Na dawo ɗakin inda su Maman Taufiƙ da Sajida suke ta hirar amaryar da kayan ɗakinta.
Zama na yi ina 'yar dariyar yaƙe na ce da su,
"Idan ba ku daina gulmar matar mutane ba, zan faÉ—a wa mijinta ya É—auki mataki kanku."
Maman TaufiÆ™ ta maka mini jar harara tana faÉ—in, "Gaskiya ce muke faÉ—a kuma ke ma kin sani, don duk wanda ya gan ki ya san zaman boranci kawai amaryar ta zo yi a gidan Abban su Haidar."
"Kin taɓa ganin inda namiji zai zuba kuɗinsa ya yi auren so don huce haushi; sannan a kira amaryar da boranci a gidansa?"
Na ƙare maganar tare da kafe ta da ido ina murmushi, Sajida ce ta yi hanzarin ba ni amsa da cewa,
"To ita dai wannan amarya Aunty; babu abin da zai tsinta a jikinta face kayan haushi da takaici. Ba ki gan ta ba fa! Yar firit da ita babu kumarin jiki balle gaba ko baya. Ta tafi 1 tamkar taɓaryar da ta shekara jingine cikin rana, ta bi duk ta ƙarmashe sai ɗan banzan son kuɗi ga surutun masifa."
Baki na rufe ina dariya saboda yadda Sajida take maganar tana yatsinar fuskar, tamkar ta hango wani abin ƙyama. Maman Taufiƙ kuma dariyar mugunta kawai take yi saboda an mata abin da take so.
Ina ƙoƙarin yin magana kiran Amina ya shigo wayata, da hanzari na ɗauka saboda tuno ban sanar da ita labarin auren ba. Ƙorafi ta fara yi mini a kan rashin zuwana ofis, sannan ta ƙare da tambayar lafiya ko jikina ne ya motsa. Ina murmushi kamar a gabanta na ce,
"Hidimar amaryar Mukhtar muke yi. Gobe za a yi walima jibi a kawo amarya, idan da hali ki zo mana bikin ko na rana É—aya ne."
'Aure!!!?'
Tambayar da ta yi kenan cikin É—aga murya, domin sautin da ta yi maganar da shi ya tabbatar mini; da mamakin auren da ta ji na ambata. Gaskiyar hasashena ya fito a cikin amsar da ta ba ni kai-tsaye muryarta tana rawa.
'CabÉ—ijam! Daman can kin san da batun auren ne? Ko kuwa yadda kika sanar da ni a sama haka ke ma kika ji shi?'
"Na san da batun auren tuni, kawai dai ke ce Allah ya mantar da ni ban faÉ—a miki ba."
Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi sannan ta ce, "Ba zan samu zuwa gobe ba sai ranar bikin. Allah ya ƙara miki haƙuri da juriya. Mutanen wurinmu suna ta tambayar lafiya ba ki fito aiki ba jiya da yau. Na faɗa musu abin da MD yake sanar musu cewar ba kya jin daɗin jikinki."
"Yawwa! Mutuniyata! Kin kyauta da yawa, ki gaishe da kowa don gobe ma da wuya na fito."
Na ƙare maganar ina rufe baki don na san sai ta yi wani ƙorafin bayan wanda ta yi.
"Gaskiya dai ki daure ki zo ko ba ki daÉ—e ba ki koma, saboda aikinki ya yi wa MD yawa ko yau sai da na rage masa wani a madadinki."
"Hmmm! A dai ba shi haƙuri iya gobe da jibi ne kawai hutun, ranar monday tun da sassafe zan shigo har sai na riga ki zuwa."
"To shi kenan! Amma dai..."
"Ke dai me? Plss! Ki ba shi haƙuri idan kin ga da matsala kuma ki sanar da shi bikin kishiyata na tsaya yi."
Ina ƙare maganar na datse kiran, don na san halinta da jan zance ya yi tsawon da sai ta sa na je aikin dole ko ba na so.
Gaisawa muka fara yi da su babu yabo babu fallasa sannan na zauna. Sajida ta fara koÉ—a ni bakinta a sake take ta yabon kwalliyata, ina hankalce da Mamarta tana aika mata harara ta gefen ido.
Ganin ba za ta daina rawar ƙafar da take yi da ni ba ta miƙe tana faɗin,
"Abincin masu jere za mu dafa. A fito mana da tukanen girkin mu je mu yi abin da ya kawo mu."
Na miƙe tare da kiran Sajida da wasu yaran da suka zo da su muka nufi kitchen. A nan muka fito da manyan tukanena da murhu biyu, tare da wasu kayan da za a buƙata duka muka fitar da su a tsakar gidan.
Ina ƙoƙarin shige falo na ji ihun yara suna faɗin ga motar kayan amarya nan ta iso. Dam-dam! Na ji dakan lugude a tsakiyar zuciyata, da murmushin yaƙe na zauna falo ina kiran lambar Firdausi.
Bayan ta É—auka nake sanar da ita Mukhtar zai yi aure yau ake gyaran É—aki,
"Ai na É—auka ba za ki faÉ—a mini ba har sai an kawo amaryar mu zo ganin ta."
"Kwantas Hajiya! Ni ma daga sama na tsinci zancen auren. Don haka gobe ki fito ku danne mini ƙirjina."
Na ƙare maganar a daidai lokacin da ake shigo da kayan gadon amarya ana shigar da su ɗakinta. Miƙewa na yi na koma ɗakina, mayafi na ɗauko mahaɗin kayan na saka, sannan na rufe ɗakin da key na yi wa matan da ke shigowa sannu da zuwa.
Na fice tsakar gidan bayan jikina ya ba ni shaidar kallon da dangin amaryar suke yi mini. Maman TaufiÆ™ na kira a waya na ce ta fito ga aikin an kawo mana har gida.
Hannu na saka ina taya su aikin ba tare da na damu da kallon mamakin da Yayunsa suke yi mini ba. Na dinga jan Sajida da hira muna dariyar da iyakacinta kan fuskata, saboda ina so na nuna wa kowa ba na baƙinciki da auren a zahiri.
Ko da Maman Taufiƙ ta shigo har mun fara cin ƙarfin aikin, tare da ita aka dafa jallop ɗin shinkafa. Sannan aka yi musu tuwon da za su je da shi gida bayan jinjer drink.
Najib mai adaidatana na kira a waya ya siyo mana ƙanƙara da nufin idan ya zo na ba shi kuɗin. Babu ɓata lokaci ya siyo mini ya kawo na biya shi, aka baza ta cikin jinjar da aka shaƙe kula biyu da ƙullinta.
Muna tsaka da haɗa kayan Mukhtar ya shigo gidan ya kira Mamar Sajida, wasu manyan ledodi biyu ya miƙa mata yana faɗin,
"Don Allah a saka musu yadda na bayar kada a bari a taɓa musu komai."
Ban bari na sake kallon inda yake ba ma balle abin da yake faɗin kada a taɓa. Sajida kawai ta kira tana faɗin ta samo wata kula a kitchen a saka musu naman kajin a ciki.
Shock na yi da jin maganar kajin, nan take raina ya ɓaci ta yadda har na kasa ɓoye damuwa a kan fuskata. Miƙewa na yi ina faɗin,
"Bari na kawo miki don kulolin suna É—akina kuma na rufe."
Ba ƙaramar jarumta na yi wurin haɗa kalmomin ba, saboda muryar kuka da ke ƙoƙarin tona asirin zuciyata. Toilet na shige na yi kukan rabin lokaci, sannan na wanke fuskata na fito na ƙara goga mai na bi da 'yar hoda sama.
Kulolin na ɗauko a cikin durowar Kitchen ɗina da na kulle da makulli. Sannan na rufe ina ƙoƙarin ɗagowa na ga Sajida a saman kaina, murmushi ta yi mini tana ƙoƙarin goge hawayen fuskarta ta ce,
"Ki yi haƙuri Aunty! Duk da na san ba a kyauta miki. Amma kuma hakan ba zai hana na ba ki haƙurin ba, don na fahimci ba ki ji daɗin abin da Baba Mukhtar ya ce ba."
"Kada ki damu! Na saba da halinsa ko kaɗan ban ji komai a kan zancensa ba. Kuma ai yana da gaskiya, idan ba mu ƙara ba ba zai yiyu mu rage musu ba."
Ina ƙare faɗar hakan muka fito kitchen ɗin muka koma tsakar gidan. A nan na ji Mamar Sajidar sun haɗa kai da wata 'yar'uwarsu, suna ta gulmar kayan ɗakin amarya.
"Ni fa ina ganin kamar ba sababbi ba ne fenti ne."
"Da gaskiyarki Maimuna! Don ko kujerun gyaransu aka yi ba sabon katako ba ne."
Murmushi na yi mai sauti sannan na matso kusa da su na ce,
"Kaya ba su ne aure ba Yaya Maimuna, ku yi musu fatan zaman lafiya sai ya fi yi da sun da kuke yi."
Kallon juna suka fara yi a muzance, kafin Yaya Maimunar ta ja kular da Sajida ta ajiye gefenta tana faÉ—in,
"Iyayi ne fa saka suruka makarantar boko. Tun da ya samu mai son sa tsakani da Allah ko yau ya mutu ya bar tarihi. Don ya ƙwaci wuyan hannunsa daga muguwar damƙar da aka yi masa."
Murmushi kawai na yi mata na bar wurin, saboda idon Sajida da ke kanmu. Kuma na tabbatar da duk abin da zan faɗa a wannan lokacin ba mai daɗi ba ne, kuma dole sai ta ji zafi domin ba zan yi ƙasa a gwiwa wurin rama daidai abin da ta faɗa mini ba, wataƙila ma na zarce awa wurin ƙoƙarin mayar da raddin na ci zarafinta a banza wofi."
Hmmmmm! Shiru ma ai magana ce Zaituna.😢
D.AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA TALATIN.*
Abincin Sajida ta zuba mana a ƙaton tire, ni da ita da Maman Taufik muka yi ɗakina. Yayin da muka bar Yaya Maimuna da sauran dangin Mukhtar a nan suna cin nasu.
Muna ɗakina muna ta hira bayan mun gama cin abincin. Ban san ya aka ƙare da 'yan jeren ba, har sai da suka zo ƙofar ɗakina suna yi mini godiya, tare da sallama a kan sun ƙare za su tafi.
Sauka lafiya na yi musu a bakin ƙofar ɗakin ban fita ba, a gabana suka fice ɗauke da kulolin abincin da aka ba su. Na dawo ɗakin inda su Maman Taufiƙ da Sajida suke ta hirar amaryar da kayan ɗakinta.
Zama na yi ina 'yar dariyar yaƙe na ce da su,
"Idan ba ku daina gulmar matar mutane ba, zan faÉ—a wa mijinta ya É—auki mataki kanku."
Maman TaufiÆ™ ta maka mini jar harara tana faÉ—in, "Gaskiya ce muke faÉ—a kuma ke ma kin sani, don duk wanda ya gan ki ya san zaman boranci kawai amaryar ta zo yi a gidan Abban su Haidar."
"Kin taɓa ganin inda namiji zai zuba kuɗinsa ya yi auren so don huce haushi; sannan a kira amaryar da boranci a gidansa?"
Na ƙare maganar tare da kafe ta da ido ina murmushi, Sajida ce ta yi hanzarin ba ni amsa da cewa,
"To ita dai wannan amarya Aunty; babu abin da zai tsinta a jikinta face kayan haushi da takaici. Ba ki gan ta ba fa! Yar firit da ita babu kumarin jiki balle gaba ko baya. Ta tafi 1 tamkar taɓaryar da ta shekara jingine cikin rana, ta bi duk ta ƙarmashe sai ɗan banzan son kuɗi ga surutun masifa."
Baki na rufe ina dariya saboda yadda Sajida take maganar tana yatsinar fuskar, tamkar ta hango wani abin ƙyama. Maman Taufiƙ kuma dariyar mugunta kawai take yi saboda an mata abin da take so.
Ina ƙoƙarin yin magana kiran Amina ya shigo wayata, da hanzari na ɗauka saboda tuno ban sanar da ita labarin auren ba. Ƙorafi ta fara yi mini a kan rashin zuwana ofis, sannan ta ƙare da tambayar lafiya ko jikina ne ya motsa. Ina murmushi kamar a gabanta na ce,
"Hidimar amaryar Mukhtar muke yi. Gobe za a yi walima jibi a kawo amarya, idan da hali ki zo mana bikin ko na rana É—aya ne."
'Aure!!!?'
Tambayar da ta yi kenan cikin É—aga murya, domin sautin da ta yi maganar da shi ya tabbatar mini; da mamakin auren da ta ji na ambata. Gaskiyar hasashena ya fito a cikin amsar da ta ba ni kai-tsaye muryarta tana rawa.
'CabÉ—ijam! Daman can kin san da batun auren ne? Ko kuwa yadda kika sanar da ni a sama haka ke ma kika ji shi?'
"Na san da batun auren tuni, kawai dai ke ce Allah ya mantar da ni ban faÉ—a miki ba."
Ajiyar zuciya ta sauke mai ƙarfi sannan ta ce, "Ba zan samu zuwa gobe ba sai ranar bikin. Allah ya ƙara miki haƙuri da juriya. Mutanen wurinmu suna ta tambayar lafiya ba ki fito aiki ba jiya da yau. Na faɗa musu abin da MD yake sanar musu cewar ba kya jin daɗin jikinki."
"Yawwa! Mutuniyata! Kin kyauta da yawa, ki gaishe da kowa don gobe ma da wuya na fito."
Na ƙare maganar ina rufe baki don na san sai ta yi wani ƙorafin bayan wanda ta yi.
"Gaskiya dai ki daure ki zo ko ba ki daÉ—e ba ki koma, saboda aikinki ya yi wa MD yawa ko yau sai da na rage masa wani a madadinki."
"Hmmm! A dai ba shi haƙuri iya gobe da jibi ne kawai hutun, ranar monday tun da sassafe zan shigo har sai na riga ki zuwa."
"To shi kenan! Amma dai..."
"Ke dai me? Plss! Ki ba shi haƙuri idan kin ga da matsala kuma ki sanar da shi bikin kishiyata na tsaya yi."
Ina ƙare maganar na datse kiran, don na san halinta da jan zance ya yi tsawon da sai ta sa na je aikin dole ko ba na so.