← Book details Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 68

Sashe 14

Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

***
_Watana ɗaya da sati biyu gidan Ummata da matar Yayanta suka zo ganin ɗakina. Saboda tsabar murnar ganin su bakina har kunnena, na tarye su da abin da nake da shi sannan na kira shi na sanar da shi zuwan su. Mintuna a tsakani ya zo da kayan marmari da jiƙa maƙoshi, na saka musu a tire na ajiye gabansu suna gaisawa da shi. Kan shi a duƙe cikin tsantsar ladabi har suka gama ya fice, na gabatar musu da abin taɓa bakin muka fara hira. Matar Kawuna ta shiga binciken zamanmu a fakaice na sanar da su komai lafiya, domin su tabbatar da abin da suka ce sun ji a bakin mutane. Dangane da zaman lafiyar da ke tsakanina da Mukhtar. Domin duk wanda ya zo ba ya gani na cikin baƙar fuska balle rashin walwala, hakan ne yake nuna zaman lafiya da jin daɗin aurena a zahiri._
"Zaituna ya zancen lefenki! Mun yi ta jira mu ji kin kira mu zo mu gani amma har yanzu babu labari. Ko dai ya ba ki mu ne ba ki faÉ—a ma ba?"
_Maganar Inna Kulu kenan domin ta ji ba'asi a kan lefen da ni ma nake bitar zancen shi cikin raina koyaushe. Domin na kasa yi wa Mukhtar tuni a kan lefen, saboda ba na so ya ga na cika zalama. Shi ya sa na dakata domin na ga zurfin gudun ruwan shi. Tambayar da Inna Kulu ta yi ta fama mini damuwar abin a raina, amma na bagayar da faÉ—ar,_
"Ko jiya mun yi zancen ya ce na ƙara haƙuri kwanan nan Iyayen shi za su kawo mini".
"Ma Sha Allah! To Ubangiji ya ƙara muku zaman lafiya da fahimtar juna. Idan suka kawo ki sanar da mu cikin lokaci domin a san me za a bayar tukuici".

_Dariyar yaƙe kawai na yi tare da ɗaga kai, cike da fargaban kada Mukhtar ya sa na ji kunya a kan ƙaryar da na yi musu, domin na ƙare masa martabar shi a idanuwansu. Lokacin da za su tafi na kira shi ya ba ni ɗari biyar na ba su, shi kuma ya ba su dubu biyu suka ce ba za su karɓa ba. Da ƙyar na matsa suka karɓa ko shi sai da ya fice sannan suka karɓa a hannuna._

_Da dare lokacin da muka kwanta bacci yana wasa da jikina nake yi masa tambaya a kan lefen, nesa da ni ya koma ya juya mini baya bai ce da ni komai ba. Shiru ya ratsa tsakani sai tashin minsharin shi na ji alamun ya yi bacci. Na É—auki lokaci ina tunanin abin da ya sa ya yi mini haka daga tambaya, ban san lokacin da bacci ya yi awon gaba da ni ba._

Hmmmm! Labari ya soma😅

D. AUTA CE✍🏼

*ABOKIN AIKINA*

*@HADIZA D. AUTA*

*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*

_*Littafina free ne ban yarda a sayar da shi ba, ko a juya shi ta wani ɓangare ba tare da izina na ba😒*_

*LAMBA SHA BIYU.*

_Da safe ma haka muka tashi yana haɗe fuska, shirin fita ofis ya yi yana ƙoƙarin ficewa na sha gaban shi tare da riƙo hannun shi. Cikin damuwar da ta bayyana kanta a saman fuskata na ce da shi,_
"Wai me hakan yake nufi ne? Ban san me na yi maka ba jiya daga magana ka yi fushi da ni. Yanzu ma ga shi kana ƙoƙarin ficewa babu walwala. Don haka don Allah ka yi haƙuri idan har akwai abin da na yi maka ban sani ba"
_Bai ce da ni komai ba, ya zare hannuna daga riƙon da na yi masa ya fice. Zama na yi cikin sanyin jiki tare da yin tagumi hannu biyu ina tunani, da zancen zucin da na shiga yi ni kaɗai ina bai wa kaina amsa. Domin jikina ya ba ni kamar akwai wata matsala dangane da lefen, shi ya sa ba ya son maganar kuma ba ya son tattauna maganar da ni. Ajiyar zuciya na sauke tare da cin alwashi a raina, ba zan sake yi masa maganar lefen ba._
_Domin matuƙar tayar da zancen zai kawo mana rashin jituwa to babu amfanin dawo da hannun agogo baya.Tun daga lokacin ban sake yi masa maganar ba, shi ma bai ce da ni komai a kan hakan ba. Ummata ma tun tana tambaya ta har ta daina, wataƙila kame-kamen da nake yi wurin kare Mukhtar, ya sa ta gano abin da nake ƙoƙarin ɓoye mata._

_Wata uku da aurenmu na samu ciki, wanda ni ban ma san da shi ba, har sai da Mamar shi ta turo mini abokiyar zamanta tana tambayar, yaushe rabon da na ga al'adata. Shiru kawai na yi ina tunani kafin na yi mata bayanin wata ɗaya ne kawai ban gani ba. Farinciki kwance a kan fuskarta ta fice, na bi ta da kallon mamaki domin kaina ya ƙulle da tambayar. Saboda na manta shaf da wani zancen ciki."
_A lokacin da Mukhtar ya dawo gidan da yamma, na fahimci kamar yana cikin damuwa duba da yadda ya yi zaune shiru yana tunani. Domin ko abincin da na kawo masa bai ci ba sai cizon haƙoran shi yake yi. Zama na yi kusa da shi cikin kulawa na ce da shi,_
"Fatan dai lafiya?"
_Shiru ya yi mini ba tare da ya ce da ni komai ba, ya duƙar da kan shi ƙasa yana kallon ledar da ke malale cikin falon nawa. Ni ma ganin haka ban sake cewa da shi komai ba na yi shiru ina tunanin wa ya taɓo shi._

"Yanzu ke kin shirya haihuwa a wannan lokacin da muke ciki?"

_Tambayar da ya jefo mini kenan cikin kaushin muryar da ta tona asirin ɓacin ran da yake ciki. Mamaki fal raina na bi shi da kallo cike da rashin fahimtar inda ya dosa._

"Haihuwa ai ba a shirya mata, domin idan lokacin yin ta ya zo ko ana so ko ba a so sai an..." Zancena kenan wanda bai bari na dire ba ya katse ni da cewa,
"Dakata Malama! Ba wa'azi na ce ki yi mini ba! Kawai amsa nake so ki ba ni."

"Idan har amsata kake son ji a nan, to ni ban da zaɓi ko jayayya da hukuncin Allah. Ko yanzu na samu ciki zan yi godiya ga Ubangiji, idan kuma ban samu ba zan jira lokacin da zai zo, ai abin farinciki ne gare mu duka." _Amsar da na ba shi kenan cikin ɓacin rai, domin na fara fuskantar abin da yake nufi da tambayar, wanda nake ji a raina ba zan lamunci hakan ba._

"To cikin ya zo, kuma ya ba ki ki yi ta farinciki."

_Yana gama faɗar maganar ya miƙe fuu ya fice falon, tare da shura takalmin shi ya bar gidan. Idanuwana a kan kulolin abincin da na kawo masa bai taɓa ba, haka kawai na ji hawaye yana bin kumatuna ba tare da na san lokacin da ya fito ba. Bayana na jingina da kujerar da nake zaune, kaina a sama ina tunanin daman haka auren yake. Domin zuwa lokacin na fara fahimtar farincikin da ke cikin aure kaɗan ne, saboda damuwar da na fuskanta a cikin shi ta fi jin daɗin shi yawa._

_Tun daga wannan maganar ya shiga fushi da ni tsawon kwanaki. Domin bayan abincin da ya daina ci har da ƙaurace mini ya yi a shimfiɗa. Amma damuwar rashin cin abincin da ya haifar wa zuciya, ya fi na haɗa shimfiɗar yawa. Saboda ko kaɗan wannan lamarin bai dame ni ba a lokacin, asali ma ji nake yi kamar an takura ni a duk lokacin da ya nemi haƙƙin shi wurina. Sai dai ba na musa masa balle na yi ƙorafin da zai gano ba na maraba da shi. Mun ja lokaci kafin ya saki fushin mu dawo kamar yadda muke, amma ko kaɗan ba ya zancen cikin. Ni ma ba na yi masa don na gama gano inda ya dosa._

_Na fara fuskantar matsalolin cikin tsakanin ƙyanƙyami da aman da nake sha, a wasu lokutan da idan na ci wani abu zuciyata ta kasa kwanciya. Alhmdulillah! Mahaifiyar shi da 'yan gidansu suna ba ni kulawa, domin duk abin da nake so ko ban nema ba za su kawo mini na ci ko na sha. Ɓangaren shi ne kawai babu gamsasshiyar kulawa, musamman irin wadda masu ciki suke buƙata a yayin laulayi. Duk da ina jin haushin ko-in-kular da yake yi wa cikin, amma ba na nuna masa saboda ko kaɗan ba na son abin da zai haɗa mu rikici._
Chapter 14 · 0% Book details