Sashe 26
Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Zantukan shi ko kaɗan ba su burge ni ba, duk da ya yi ƙoƙarin binne gaskiyar abin da ya faru, a ƙoƙarin shi na gudun zargin da za a yi mana tare da ɓacin sunanmu daga ni har shi.
Bayan ya fice Amina ta zauna ci masa albasa, tana ta ba ni baki a kan na yi haƙuri ko don shi. Ƙanzil ban ce mata ba, domin duk maganar da zan yi a lokacin sai na zubar da ruwan hawaye, kuma ba na so ta ga kasawa ta gudun ta yi tunanin matar MD ta yi nasara kaina.
Jugum-jugum muka yi daga ni har ita babu mai magana, bayan ta gama ba ni haƙuri da maganganu masu daɗin da suka rage mini takaicin MD da matar shi.
Da lokacin tashi ya yi muka fito zuwa bakin gate, sai dai mamakin da na yi duk inda muka wulga zancen faÉ—an ake yi da an hango mu a yi shiru.
Muna gaf da ficewa muka jiyo muryar Sara tana ƙwala wa Amina kira, tare muka juya bayan mun tsaya har ta ƙaraso inda muke. Kafaɗar Amina ta dafa tana dariyar shaƙiyanci ta ce,
"Ashe abin da ya faru kenan a yau? Gaskiya dai abin bai yi daɗi ba, don babu kyau abin da mutum yake yi a ɓoye a fito da shi fili a yi masa terere kowa ya gani. Ubangiji dai ya ƙara tsare tsautsayi, da ranar tonuwar asirin da ya fi wanda aka yi yau."
Ta ƙare maganar tare da yi mini wani kallon rainin hankali ta yi gaba, Amina ta yi hanzarin janyo mayafinta a fusace tana faɗin,
"Duk wanda ya faɗa miki wannan tatsuniyar gizo da ƙoƙin bai san yadda gaskiyar abin yake ba. Domin ita kanta matar MD ta yi ne a rashin sani, amman idan kina tantama ki je wurin shi ki ji gaskiyar komai daga bak..."
"Zo mu je Amina, kin san shi mutum mai mummunan zato da jiran ƙiris, komai za ki faɗa masa gaskiya ba zai hankalta ba. Idan ma abin da take tunanin gaskiya ne ita ta je ta yi idan fitsari banza ne."
Abin da na faɗa kenan bayan na yi gaba na bar su a nan, saboda na sha ganin MD yana kyarar ta ba sau ɗaya ba. A ƙarshe ya yi mata iyaka da ofishin shi komai uzuri, idan ma wani abu ne sai dai ta bai wa wani ya kai masa.
"Allah ya raba ni aikata fasadi da aurena. Ke dai da kika ji za ki iya ki je ki yi ta yi akwai ranar ƙin dillanci."
Maganarta ta sa na juyo a fusace na shaƙo wuyanta, Amina ta shiga ɓanɓare hannuna tare da faɗin a kawo mata ɗauki. Saboda ganin na kai maƙurar ɓacin ran da komai zan iya aikatwa a lokacin, domin zafafan maganganunta sun dakar mini zuciya ba kaɗan ba, wanɗanda nake ji tamkar ta ɗana mini garwashin wuta a cikin zuciyar ta fara cin wuta.
Taro aka yi mana sosai, bayan an ƙwace ta daga hannuna tana tarin wahala, ana ba ni haƙuri tana sake jifa ta da miyagun maganganu masu zafi bayan ƙazafin da take jifa ta da shi son ranta ni da MD.
Babu wanda ya ga zuwan MD sai marin da ya kwaÉ—a mata a fusace yana nuna ta da hannu ya ce,
"Matuƙar kika sake jingina ƙazafinki a kaina, sai na yi ƙarar ki a kulle ki har makulli ya yi rara, domin na ga wanda zai tsaya miki a faɗin garin nan. Me ya sa ku mutane ba ku da adalci ne? To duk iskancinki kada ki bari ganganci ya sa ki saka ni. Idan ban da ke shashasha ce har ni za ki yi ƙoƙarin manna mana sharri? Kaf faɗin ma'aikatar nan ban da wata alaƙa mai ƙarfi da kowa, idan aka wuce ta aikin da ya haɗa ni da mutum abu ne wanda kowa ya sani. Me ya sa kika manta rawar ƙafar da kike yi a kaina, a kan kawai ki samu na saurare ki na ƙi? To tun da tonon sililin kike so, idan kin manta zan tuna miki yanzu, ko satin da ya wuce sai da na ci zarafinki a kan wannan mugun abin, wanda kike ƙoƙarin manna wa wata a bisa zargi ba tare da kin tabbatar ba."
Soshe-soshen kai Sara ta fara yi tana mutsu-mutsun rashin gaskiya, tare da roƙon shi a wayance a kan ya yi shiru ya daina bankaɗa mata labulen sirri.
Murmushi na ji ya suɓuce mini babu shiri, na yi gaba fuskata a washe saboda fiye da rabin ɓacin raina ya zumame. Ban san ya aka ƙarke ba ni dai na haye adaidaita na yi gida, zuciyata cike da tunanin,
'Ya aka yi na baro wallet É—ina a gidan MD har matar shi ta gani.'
Ajiyar zuciya na sauke a lokacin da aka ajiye ni ƙofar gidan. Tunani fal zuciyata na shiga gidan, da sassarfa na faɗa falon saboda kukan Haidar da na ji yana tashi.
Ummu Salma da Iman suka yi kaina da gudu suna ihun murnar gani na. Mamakina da na hango Haidar ya ƙara shan jinin jikin shi, sai matsar ƙwalla yake yi tare da goge hawayen da ya jiƙa masa fuska.
Da sanyin jiki na nufo shi da nufin na ji wa taɓa shi, sai dai kafin na isa wurin shi ya yi hanzarin tashi da gudu ya yi ɗakinsu ya rufe. Baki a sake na bi ƙofar da kallo kafin na dawo da kallona a kan fuskar Ummu Salma, wadda ke wasa da yatsun hannunta tana so ta yi magana tana shayi.
"Me aka yi wa Haidar?"
Tambayar da na jefo mata kenan don na san Iman ba gwanar magana ba ce.
"Don Allah Mama kada ki dake shi don Abbanmu ma ya dake shi."
Gabana ya ƙire ya faɗi cikin sauri bakina yana rawa na ce, "To me ya yi aka sake shi?"
"Taba ya ɗauko ɗakin Abbanmu ya kunna ya sha, ni da Iman ba mu sani ba sai da muka jiyo ihun shi cikin toilet sannan muka je da gudu. A nan muka ga tabar a hannun shi yana ta tari kamar zai mutu. Na fara zuba masa ruwa a fuska ni da Iman muna ta kuka, na ce da ita ta kira Abbanmu kada ya mutu mu shiga uku. Ko da Abban ya zo na faɗa masa taba ya sha shi ne fa ya yi ta dukan shi, da ƙyar ya ƙyale shi saboda ganin muna ta kuka ni da Iman."
Zaman na yi babu shiri tare da furta kalmar, "Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun!" Saboda ita kaÉ—ai ce kalmar da zan iya furtawa a lokacin.
Ni ma dai jikina ya yi sanyi😰🚶ðŸ»â€â™€ï¸
D. AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA ASHIRIN.*
Shiru na yi na ɗan lokaci dafe da kaina da ke ta sarawa, sannan na miƙe su Ummu Salma suka fara kuka tare da roƙo na don Allah kada na buge shi.
Ban bi ta kansu ba balle ta kan Haidar da ke kulle cikin ɗakinsu. Ɗakina na nufa yaraf na zauna bakin gado saboda jirin da ke kwasa ta, mintuna a tsakani na miƙe na ɗoro arwala. Sallah na gabatarwar tare da ɗaga hannuwana sama ina roƙon Allah shiriya zuwa ga 'ya'yana. Ruwan hawaye yana zarya a kan dandamalin fuskata cikin ƙanƙan da kai tare da tawassuli da haƙurin da nake yi a gidan Mukhtar.
Ummu Salma ta shigo ɗauke da kula ta ajiye gefena, tana ƙoƙarin ficewa cikin sanyin murya na ce da ita,
"Kira mini Haidar ku zo tare."
"To" Ta faɗa sannan ta fice jim kaɗan ta dawo riƙe da hannun Haidar yana tirjiya tana janyo shi, Iman ta yi hanzarin zuwa inda nake tana matsar hawaye ta ce,
"Don Allah Mama ki yafe masa Abbanmu ya dake shi sosai."
Kallo na bi fuskar shi tare da tsuke tawa fuskar na ce,
"Zo nan!"
Ya tako yana É—ari-É—ari tare da haÉ—a hannuwan shi wuri É—aya yana faÉ—in,
"Don Allah! Don Allah Mama wallahi ba zan sake ba."
Har ga Allah jikina ya yi sanyi da zancen shi, uwa-uba yanayinsu duka da ya koma kalar tausayi. Wuri na nuna masa da nufin ya zauna, zama ya yi a É—arare yana tsiyayar hawaye daga idanuwan shi da suka yi jawur saboda kuka.
"Kana so na mutu?"
Bayan ya fice Amina ta zauna ci masa albasa, tana ta ba ni baki a kan na yi haƙuri ko don shi. Ƙanzil ban ce mata ba, domin duk maganar da zan yi a lokacin sai na zubar da ruwan hawaye, kuma ba na so ta ga kasawa ta gudun ta yi tunanin matar MD ta yi nasara kaina.
Jugum-jugum muka yi daga ni har ita babu mai magana, bayan ta gama ba ni haƙuri da maganganu masu daɗin da suka rage mini takaicin MD da matar shi.
Da lokacin tashi ya yi muka fito zuwa bakin gate, sai dai mamakin da na yi duk inda muka wulga zancen faÉ—an ake yi da an hango mu a yi shiru.
Muna gaf da ficewa muka jiyo muryar Sara tana ƙwala wa Amina kira, tare muka juya bayan mun tsaya har ta ƙaraso inda muke. Kafaɗar Amina ta dafa tana dariyar shaƙiyanci ta ce,
"Ashe abin da ya faru kenan a yau? Gaskiya dai abin bai yi daɗi ba, don babu kyau abin da mutum yake yi a ɓoye a fito da shi fili a yi masa terere kowa ya gani. Ubangiji dai ya ƙara tsare tsautsayi, da ranar tonuwar asirin da ya fi wanda aka yi yau."
Ta ƙare maganar tare da yi mini wani kallon rainin hankali ta yi gaba, Amina ta yi hanzarin janyo mayafinta a fusace tana faɗin,
"Duk wanda ya faɗa miki wannan tatsuniyar gizo da ƙoƙin bai san yadda gaskiyar abin yake ba. Domin ita kanta matar MD ta yi ne a rashin sani, amman idan kina tantama ki je wurin shi ki ji gaskiyar komai daga bak..."
"Zo mu je Amina, kin san shi mutum mai mummunan zato da jiran ƙiris, komai za ki faɗa masa gaskiya ba zai hankalta ba. Idan ma abin da take tunanin gaskiya ne ita ta je ta yi idan fitsari banza ne."
Abin da na faɗa kenan bayan na yi gaba na bar su a nan, saboda na sha ganin MD yana kyarar ta ba sau ɗaya ba. A ƙarshe ya yi mata iyaka da ofishin shi komai uzuri, idan ma wani abu ne sai dai ta bai wa wani ya kai masa.
"Allah ya raba ni aikata fasadi da aurena. Ke dai da kika ji za ki iya ki je ki yi ta yi akwai ranar ƙin dillanci."
Maganarta ta sa na juyo a fusace na shaƙo wuyanta, Amina ta shiga ɓanɓare hannuna tare da faɗin a kawo mata ɗauki. Saboda ganin na kai maƙurar ɓacin ran da komai zan iya aikatwa a lokacin, domin zafafan maganganunta sun dakar mini zuciya ba kaɗan ba, wanɗanda nake ji tamkar ta ɗana mini garwashin wuta a cikin zuciyar ta fara cin wuta.
Taro aka yi mana sosai, bayan an ƙwace ta daga hannuna tana tarin wahala, ana ba ni haƙuri tana sake jifa ta da miyagun maganganu masu zafi bayan ƙazafin da take jifa ta da shi son ranta ni da MD.
Babu wanda ya ga zuwan MD sai marin da ya kwaÉ—a mata a fusace yana nuna ta da hannu ya ce,
"Matuƙar kika sake jingina ƙazafinki a kaina, sai na yi ƙarar ki a kulle ki har makulli ya yi rara, domin na ga wanda zai tsaya miki a faɗin garin nan. Me ya sa ku mutane ba ku da adalci ne? To duk iskancinki kada ki bari ganganci ya sa ki saka ni. Idan ban da ke shashasha ce har ni za ki yi ƙoƙarin manna mana sharri? Kaf faɗin ma'aikatar nan ban da wata alaƙa mai ƙarfi da kowa, idan aka wuce ta aikin da ya haɗa ni da mutum abu ne wanda kowa ya sani. Me ya sa kika manta rawar ƙafar da kike yi a kaina, a kan kawai ki samu na saurare ki na ƙi? To tun da tonon sililin kike so, idan kin manta zan tuna miki yanzu, ko satin da ya wuce sai da na ci zarafinki a kan wannan mugun abin, wanda kike ƙoƙarin manna wa wata a bisa zargi ba tare da kin tabbatar ba."
Soshe-soshen kai Sara ta fara yi tana mutsu-mutsun rashin gaskiya, tare da roƙon shi a wayance a kan ya yi shiru ya daina bankaɗa mata labulen sirri.
Murmushi na ji ya suɓuce mini babu shiri, na yi gaba fuskata a washe saboda fiye da rabin ɓacin raina ya zumame. Ban san ya aka ƙarke ba ni dai na haye adaidaita na yi gida, zuciyata cike da tunanin,
'Ya aka yi na baro wallet É—ina a gidan MD har matar shi ta gani.'
Ajiyar zuciya na sauke a lokacin da aka ajiye ni ƙofar gidan. Tunani fal zuciyata na shiga gidan, da sassarfa na faɗa falon saboda kukan Haidar da na ji yana tashi.
Ummu Salma da Iman suka yi kaina da gudu suna ihun murnar gani na. Mamakina da na hango Haidar ya ƙara shan jinin jikin shi, sai matsar ƙwalla yake yi tare da goge hawayen da ya jiƙa masa fuska.
Da sanyin jiki na nufo shi da nufin na ji wa taɓa shi, sai dai kafin na isa wurin shi ya yi hanzarin tashi da gudu ya yi ɗakinsu ya rufe. Baki a sake na bi ƙofar da kallo kafin na dawo da kallona a kan fuskar Ummu Salma, wadda ke wasa da yatsun hannunta tana so ta yi magana tana shayi.
"Me aka yi wa Haidar?"
Tambayar da na jefo mata kenan don na san Iman ba gwanar magana ba ce.
"Don Allah Mama kada ki dake shi don Abbanmu ma ya dake shi."
Gabana ya ƙire ya faɗi cikin sauri bakina yana rawa na ce, "To me ya yi aka sake shi?"
"Taba ya ɗauko ɗakin Abbanmu ya kunna ya sha, ni da Iman ba mu sani ba sai da muka jiyo ihun shi cikin toilet sannan muka je da gudu. A nan muka ga tabar a hannun shi yana ta tari kamar zai mutu. Na fara zuba masa ruwa a fuska ni da Iman muna ta kuka, na ce da ita ta kira Abbanmu kada ya mutu mu shiga uku. Ko da Abban ya zo na faɗa masa taba ya sha shi ne fa ya yi ta dukan shi, da ƙyar ya ƙyale shi saboda ganin muna ta kuka ni da Iman."
Zaman na yi babu shiri tare da furta kalmar, "Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun!" Saboda ita kaÉ—ai ce kalmar da zan iya furtawa a lokacin.
Ni ma dai jikina ya yi sanyi😰🚶ðŸ»â€â™€ï¸
D. AUTA CEâœðŸ¼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA ASHIRIN.*
Shiru na yi na ɗan lokaci dafe da kaina da ke ta sarawa, sannan na miƙe su Ummu Salma suka fara kuka tare da roƙo na don Allah kada na buge shi.
Ban bi ta kansu ba balle ta kan Haidar da ke kulle cikin ɗakinsu. Ɗakina na nufa yaraf na zauna bakin gado saboda jirin da ke kwasa ta, mintuna a tsakani na miƙe na ɗoro arwala. Sallah na gabatarwar tare da ɗaga hannuwana sama ina roƙon Allah shiriya zuwa ga 'ya'yana. Ruwan hawaye yana zarya a kan dandamalin fuskata cikin ƙanƙan da kai tare da tawassuli da haƙurin da nake yi a gidan Mukhtar.
Ummu Salma ta shigo ɗauke da kula ta ajiye gefena, tana ƙoƙarin ficewa cikin sanyin murya na ce da ita,
"Kira mini Haidar ku zo tare."
"To" Ta faɗa sannan ta fice jim kaɗan ta dawo riƙe da hannun Haidar yana tirjiya tana janyo shi, Iman ta yi hanzarin zuwa inda nake tana matsar hawaye ta ce,
"Don Allah Mama ki yafe masa Abbanmu ya dake shi sosai."
Kallo na bi fuskar shi tare da tsuke tawa fuskar na ce,
"Zo nan!"
Ya tako yana É—ari-É—ari tare da haÉ—a hannuwan shi wuri É—aya yana faÉ—in,
"Don Allah! Don Allah Mama wallahi ba zan sake ba."
Har ga Allah jikina ya yi sanyi da zancen shi, uwa-uba yanayinsu duka da ya koma kalar tausayi. Wuri na nuna masa da nufin ya zauna, zama ya yi a É—arare yana tsiyayar hawaye daga idanuwan shi da suka yi jawur saboda kuka.
"Kana so na mutu?"