← Book details Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 68

Sashe 10

Abokin Aikina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallon mamaki ta bi ni da shi kafin ta sake cewa, "Kina da damuwa amma ban taɓa gani a kan fuskarki ba? Kina da damuwa amma ba ki taɓa nuna alamun hakan ko a cikin furucinki ba? Kina da damuwar da ta fi tawa kuma kika iya haɗiye ta cikin cikinki, ba tare da kin yi aman jinin fitar da baƙincikinki a fili kin huta ba? Ta ya zan gamsu da hakan bayan ni na kasa shanye rabin kwatar damuwar da kika ce kina da ita? Kaico Zaituna, ni na kasa farinciki balle wanda zai linka ni fuskantar matsalar a rayuwar aure?"

Murmushi na yi mata sannan na fara safa da marwa a tsakiyar offis ɗin, kaina a duƙe hannuwana a baya ina furzar da iska mai zafi daga bakina. Saboda tuno majaujwar tashin hankalin da ta yi ta juyawa da ni a baya har zuwa yanzu.
Hawayen da suka fara gangara a kan fuskata na share da gefen hannuna, sannan na yi jarumtar ba ta amsa a gajarce.
"Ta hanyar sanar da ke labarina"
Ban jira cewarta ba na fara jero mata tambayoyina kamar haka;
"Kin taɓa kama mijinki yana hulɗa da matar aure?"
"Mijinki ya taɓa faɗa wa duniya kin ce sai kin kashe shi?"
"Mijinki ya taɓa damfarar Iyayenki?"
"Mijinki ya taɓa yi wa 'yar aikinki ciki?"
"Mijinki ya taɓa neman auren ƙawayenki na ƙud-da-ƙud waɗanda kuka tashi tun kuna ƙurciya?"
"Mijinki ya taɓa bai wa ɗanki matsayin da ya yi kamanceceniya da zama kishiyarki?"
"Mijinki ya taɓa sayar miki da kayan ɗaki? Ko ya taɓa satar miki kuɗi ko wani abin amfani?"
"Mijinki ya taɓa fallasa ki a bisa ƙazafi cikin dangin shi da naki bayan 'yan'uwa da abokan arziƙi masu ganin girmanki?"
"Mijinki ya taɓa zuwa wurin mutanen da kike jin kunya aron kuɗi ko roƙo?"
"Mijinki ya taɓa yi miki ƙazafin kina tare da wasu mazan waje a gaban 'ya'yanki?"
"Kin taɓa neman haƙƙinki wurin mijinki bai sauke ba?"
"Kin taɓa shekara huɗu ba tare da mijinki ya kasance ki ba...?"

"Dakata Zaituna. Kada ki sanar da ni cewa duk waɗannan abubuwan da ke suka faru?" Hanzarin katse ni ta yi saboda mamakin maganganun da ta ji suna fita bakina. Kafin na ba ta amsa cikin muryar kukan da ya kasa tsaya mini, saboda ta sa na fama mikin baƙinckin da ya daskare mini zuciya.

"Tabbas da ni waÉ—annan abubuwan duka suka faru, har ma da sauran wasu tambayoyin da kika katse ni ban samu sararin furzowa ba..."
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun! Ke kam wace irin zuciya ce da ke haka mai shanye baƙƙan ciki manyan kashi kashi irin haka? Ni ko zan so na ji waɗannan abubu ɗaya bayan ɗaya, don na san tabbas akwai karatun da zan kwashe a cikin tarihin rayuwarki. Kuma zan ɗauki darussa a ciki ko don na magance matsalar da ta addabe ni. Cabɗijam! Ashe daman akwai wadda ta fi ni shiga matsala a rayuwar gidan aure?"

Akwai Amina. Domin kuwa kafin a je ko'ina ga Zaituna nan a kusa da ke🥲

D. AUTA CE✍🏼

*ABOKIN AIKINA*

*@HADIZA D. AUTA*

*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*

*LAMBA TA TARA.*

"Tabbas! Akwai wadda ta linka ki fuskantar baƙƙan cikin aure. Kuma ba wata ba ce face ni nan Zaituna"
Kallon mamaki na ga ta bi ni da shi tana jinjina kai, kafin ta yi tagumi tana kallo na tamkar wata sabuwar halitta a gabanta. A hankali na tako na zo wurinta na dafa kafaɗarta fuskata ɗauke da murmushin ƙarfin hali, wanda na yi amfani da shi ne kawai domin na kore rabin damuwata, kuma na ƙarfafa mata zuciya ta zamo jaruma a fagen shanye takaici, jajirtacciya a wurin kawar da kai da hangen nesa.

"Akwai mata da yawa waÉ—anda suke fuskantar matsalolin aure a wannan lokacin da muke ciki. Saboda sauyin da zamani ya zo mana da shi, da kuma tsarin yadda ake gina tubalin auren tun tushen shi. Ba tare da an yi duba da nagartar mutum ko asalin shi ba".

Zancen da na yi kenan a lokacin da nake duƙe wurin Amina domin na tunatar da ita mutuwar yawa kaka ce. Sannan na miƙe na nufi kujerata na zauna, idonta a kaina wanda alamu ya nuna mamakina da ke kwance a kan fuskarta.
Daga can inda take zaune ta jefo mini tambaya cikin sanyin murya. "Ina mamakin yadda kika iya shanye waɗannan abubuwan duka a cikin zuciyarki. A rayuwata ban taɓa sanin akwai mai ƙarfin zuciya irinki ba, domin ina da yaƙinin da ni ce ke da tuni na mutu har an manta da ni. Amma ke ga ki sharr da ke ma sha Allah tamkar ba ki san wani abu damuwa ko ɓacin rai ba.."
"Ni ma ɗin ba yin kaina ba ne daga Allah ne. Saboda na yi kuka tamkar zan ƙarar da ruwan hawayena, haka ma na shiga ƙunci da damuwa tamkar ba zan sake shaƙar iskan numfashi ba. Amma duk da hakan Allah ya inganta mini lafiya har yanzu ba a ce ina ɗauke da hawan jinin ba. Don haka ke ma ki mayar da komai ba komai ba, ki kalli komai ki kawar da kai kamar ba ki hango komai ba. Ina tabbatar miki sannu a hankali komai zai zo miki fiye da tsammanin ki. Abin da ya saka ki kuka a yau zai dawo yana ba ki dariya, abin da ya ba ki takaici zai dawo hannunki kina juya shi ta yadda kika ga dama. Amma duk wannan ba zai samu ba har sai kin cusa wa zuciyarki haƙuri, haƙurin ma na gasken gaske".

Shiru ya ratsa tsakani kafin na ji ta sauke ajiyar zuciya cikin sanyi ta ce, "Ke mutum ce har da rabi Zaituna. Na gode wa Allah da ya kawo ki ma'aikatar nan kuma ya haɗa ni zama da ke. Saboda kina da zuciya mai kyau tare da hangen nesa. Na gode sosai Allah ya ƙara mana haƙuri gabaɗaya".

Murmushi kawai na yi cike da jin daɗin yabon da ta yi mini, duk da wani sashe na zuciyata yana tunatar mini da ɓoyayyen laifina, tare da wannan da nake ƙoƙarin aikatawa a sirrance.
Agogon hannuna na duba cikin sauri na fara haɗa takardu ina sakawa jakata, saboda ganin har ƙarfe biyu ta wuce uku ta doso. Miƙewa na yi na nufi ƙofa da nufin zuwa gida, Amina ma ta tashi daga zaman dirsham ɗin da ta yi a dandamalin siminti tana gyara zaman zaninta. Ina ƙoƙarin ficewa ta yi hanzarin dafa kafaɗata ta ce "Ina sha'awar jin labarin tarihin rayuwarki. Idan babu damuwa ki ba ni lokacin da zan zo har gida, domin na ji wannan badaƙalar da kika fara yi mini tsokaci. Saboda jikina ya ba ni zan ƙaru da wasu abubuwa fiye da na yanzu".

"Idan kuma mijina bai aminta da hakan ba fa?"
"Sai na haƙura".
Ta ƙare maganar cikin kwantar da kai da muryar tausayi. Murmushi a kan fuskata na ce, "Zan sanar da ke amma ba gidana ba. Saboda ba na so na yi sara da mutum sama".
Ita ma fuskarta ta faÉ—aÉ—a da murmushin alamun ta hasko abin da nake nufi.

Tare muka fito inda muka tarad da mutane da yawa sun yi gida, saboda a ƙa'ida ƙarfe biyu dam muke tashi. Amma yau ga mu har ƙarfe uku saboda batutuwan da muka tattauna sun janyo lokaci ya tafi ba mu sani ba.

Cike da damuwa muka doshi bakin gate ɗin ma'aikatar, saboda haushin rashin ganin motar MD, wanda alamu ya nuna shi ma ya yi gida. Muna ƙoƙarin fita gate sai ga motar shi ta doso babu shiri muka yi gefe ya shige. Kamar na tsaya na yi masa sai gobe, amma na dake na fice muka ja tunga a bakin titi. Abin hawa muka samu dukanmu, ni na fara shiga tawa na zauna har muna ƙoƙarin barin wurin. Sai ga muryar Baba maigadi yana ƙwala mana kira ni da Amina, da sauri na leƙo kai bayan na dakatar da mai adaidaitan ya tsaya. Baba maigadi ya iso wurinmu da ledodi biyu a hannun shi ya miƙo mini ɗaya ya bai wa Amina ɗaya. Kafin mu tambaye shi ya riga mu da faɗar,

"Ranka ya daÉ—e ne ya ce na kawo muku".

Baki sake na kai kallona cikin ma'aikatar, sannan na dawo da kallon a kan Baba maigadin na ce, "Kuma mu ya ce a bai wa?"

Kai-tsaye ya amsa mini da "Tabbas! Ko tantama babu Hajiya".
"Ka ce masa mun gode. Allah ya ƙara rufa asiri". Cewar Amina kenan cike da jin daɗin da ya bayyana kan fuskarta.
"Hajiya mu je kawai Allah ne ya tsaga da rabonmu".
Abin da ta sake faÉ—a mini kenan ta shige adaidaita suka wuce, ganin hakan ya sa ni ma na yi godiyar cikin sanyin jiki muka tafi.

Tafe nake cike da mamakin wannan kyauta da MD ya yi mana ni da Amina. Duk da ba wannan ne karo na farko da yake yi wa mutanen wurinmu alheri ba, amma dai ni kam na ji abin har cikin raina.
Ban san lokacin da muka isa unguwar ba, sai da mai adaidaitan ya tambayi wani layi zai shiga. A nan na dawo natsuwata na yi masa kwatance muka doshi ƙofar gidanmu.

Tun daga nesa na hango Mukhtar zaune a kan dakalin ƙofar gidan, tare da wata mai tallar masara bakin shi har kunne suna hira. Haushi ya turnuƙe ni cikin sauri na miƙa wa mai adaidaita kuɗin shi na ja ledata. Ban kalli inda yake ba balle na tsaya sauraron borin kunyar da yake yi.
"Tashi ki je malama, tun da na biya ki kuÉ—in masararki zaman me kike yi a nan kuma? Salon ki janyo mini zargi..."
Iya abin da kunnuwana suka ji kenan na shige ciki. Da gudu yarana suka tarye ni suna ihun murnar gani na, da masara a hannunsu suna ci. Ban yi mamakin ganin su da masarar ba don na san Mukhtar ne ya saya musu.
Zama na yi a falon ina faɗin "Wash! Allah!" Iman da Haidar suka fara yi mini sannu da zuwa cikin farinciki. Sai ga Ummu Salma da plate ɗin taliya shaƙe ta dire a kan teburin tsakiyar falon. Sannan ta ɗauko ruwa biyu a firij ta dire mini tana wasar bakin faɗin,

"Sannu da zuwa Mama".
Chapter 10 · 0% Book details