Sashe 20
A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel · about 2 min read
sa ido, abinda ya sa a ransa shine wata kila Ibrahim din ne bata so.<br /> Shi kuwa Ibrahim har su Husna ya kwaso ya kawo mata tabbacin cewa Sakina ta sani kenan.<br /> Wannan bai dami Nusaiba ba, domin bata san irin bala in da ya sha a gida ba, akan hakan.<br / > Ta fara riga ta ga duniya, babu wata yaudar da Da namiji zai nuna mata.<br /> Idan gaskiya ne, ya ce zai kai ta gun Sakinar mana?<br /> Bai ta6a gigi ba, sai dai ya kwaso mata su Husna.<br /> Kwatsam! Sai ga Alh. Basheer a Jordan, ba zato ba tsammani. Kai murna a wajen Nusaiba, kamar ta zuba ruka k'asa ta sha.Tana kewar sa sosai, tunda ya zo take like da shi.<br /> Shi kuwa Ameer ke zuciyar sa, ji yake kamar in zai koma ya wuce da shi, ya zauna gidan sa.<br / > Yaron yayi saurin girma kamar ba dan shekara 2 da watanni ba.<br /> Suna zaune dare ya fara yi ga Injiniya ga Antinta.<br /> "Alhaji ya tambaya,"Wai 'yar gidan ta ku bata fidda wani ba? Jin haka yasa Nusaiba ta tashi ta bar falon.<br /> Injiniya ya ce,"Ai mu Nusaiba ba mu san inda ta dosa ba."<br /> Kamar yaya?<br /> Ya ce,"Wani yaro ke son ta kamar zai yi hauka,<br /> amma ba ka ga yadda take wahalar da shi ba.<br /> Ni Wallahi tausayi yake ba ni.<br /> Yana da mata da 'ya'ya'yen sa 3.<br /> Ibrahim sunansa, yana aiki da (Nijeriyan Embasy) , yaro mai hankali, amma ta ki ba shi goyon baya."<br /> Ya ce,"Ibrahim?<br /> Ni kuwa kamar na san sunan nan?<br /> Anya kuwa ba yaron nan ba ne daya so auran ta da?<br /> Fatima ta ce,"Oho,"Nusaiba wani bayani za ta zauna ta yi.<br /> Yarinya da ka fara magana, sai kuka.<br /> Ni dai yara suke gaya min wai a (Super market) suka hadu, amma sun ga kamar dama can ya san ta.<br /> Ya ce,"Lalai Ibrahim din da na ke magana ne.<br /> Kuma da akwai alamun tana son sa, ni ne na cusa mata Zancen Naseer.<br /> To me yasa yanzu ba za ta aure shi ba?<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ----------------------------------------------------------------------------------------------