← Book details A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 28

Sashe 10

A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Yayi zuru kafin, ya numfasa ya dube ta ido sun kawo kwalla.<br /> "Shi kenan Umma, na gode. Abinda na ke son ki rokin min Abba, shine, don Allah yayi hkr, idan na gaishe shi ya rinka amsawa. Ni zan fita, ga wannan koda Ameer yana bukatar wani abu." Ya ciro dubu 2, ya aje bisa hannun kujera ya tashi ya fice.<br /> ~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~­ ~~~~~~~~~~------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Karfe 9 ta gota kadan Jeep din su Hajiya Zulai ta yi fakin kofar gidan su Naseer. Suka fito Ummi na rike da hannun Nusaiba. Ummi ta yi sallama tsakar gida. Umma ta amsa daga falo, a lkcn kuwa ta kammala shirya Ameer tsaf!Yana ta tashin kamshin hoda. Bata dauki murya sosai ba, don haka ta ce,"Maraba, ku shigo mana." Ummi ta yaye labule. Umma ta mike baki har kunne,"Hajiya!<br /> Ah!<br /> Nusaiba!<br /> Sannun ku da zuwa."<br /> Suka zauna a kujera Umma ta mikawa Ummi Ameer, ta karbe shi. Sai ta wuce firj za ta dauko kayan sha.<br /> "Dama kin bar shi, kin san safiya ce." Duk da haka ta kawo da Jus din kananan kwali da kufuna 2.<br /> Bayan sun gaisa, Umma ta tambayi Alhj? Sai Ummi ta ci gaba da cewa,"Ba wani abu ya kawo mu ba.<br /> Ameer mu ka zo tafiya da shi, ya zauna wajen uwar sa ta shayar da shi. Ko dama 6acin rai ne yasa aka aje shi."<br /> Kwalla suka cika idanuwan Umma ta ce,"Gaskiya ne kuwa, na ji dadi, domin a gaba daya wannan al'amari Ameer shine abin tausayi.<br /> Shi kuma wancan sakaran, ai kyale shi ya gasu, duk da cewar ya ce yayi nadama." Ummi ta yi dan murmushi ta ce,"Ai ba'a soyayya dole, mu ma mun san haka shi yasa Alhj ya ce a gaya masa, tana jiran takardarta, ko zuwa jibi. Insha- Allah za mu turo mota akwashe kayan ta a dauki motar ta."<br /> Umma ta goge kwalla ta ce,"Ba laifi, ki yi hkr Nusaiba kin ji? Allah ya amfana miki dan ki. Ta dan sadda kai ta ce,"Ba komai Umma.<br /> Idan kuma na yi miki wani laifi, ki yafe min." Ta girgiza kai,"Baba abinda ki ka yi min Nusaiba, Allah yayi miki albarka."<br /> Ta ce,"Amin." Ummi ta ce,"To bari mu je, za ta debi wasu kayan kafin a zo kwashewa." Umma ta ce,"To bari in kawo maku wani makullin, ya fita da na hannun sa."Nusaiba ta ce,"Ina Antina Umma?<br /> Ta ce,"Ita ma ta tafi."<br /> Suka dubi juna, kafin Ummi ta tambaya,"Saboda me?------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------
Chapter 10 · 0% Book details