Sashe 19
A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
min Husna."<br /> Ta fadi tana tura keken (Shopping) tana ci gaba da kiran yara,"Sumayya ina ku ke? Ku zo mu tafi! <br /> Ya dan sauke numfashi, ya biyo ta a hankali.<br / > Suka hadu da yaran a wata kwana,"Anti ba mu gama ba,"Inji babbar cikin su Sumayyah.<br /> Dai-dai Ibrahim na tsayuwa wajen.<br /> Ta ce,"Gaskiya ba zan jira ku ba, gobe Direba ya sake kawo ku." Yayi fit yasa masu baki,"Haba Anti, bai kamata ba, ki kyale su su gama."<br /> Duk suka bi shi da kallo.<br /> Ya juya kan sa,"Ga Sumayyah ko? Ke fa? Ya nuna mai bi mata, ta ce,"Khadija."<br /> Ke fa? Ta ce,"Mahadiyya." Ya duka ya kamo 'yar kamar ,"Ke fa? Ta ce,"Zainab." Ya runtse ido ya ce"Wash! Uwa da magani. Sannu Husna.<br /> Mahadiyya ta cafe,"Ba husna sunanta ba ZEE AFLAN! Ta kai mata duka, suka kwashe mata da dariya. Takaici ya ishi Nusaiba, ta tura keke ta yi gaba.Ta bar shi yana rabon fada, wa ya radawa uwa ta ZEE AFLAM? Lalai ba zai sha (Ice-cream) ba yau."Mahadiyya ta ce,"Ba ni bace. Anti Sumayyah ce."<br /> Ya kada kai,"Ba ki kyauta ba.<br /> To ku tsaya in tambaye ku, yaushe Anti Nusaiba ta zo nan? Sumayya ta ce,"Ta dade, tun Ameer na jariri." Baban Ameer yana nan garin ne? Ta ce,"A'a yana Nijeriya." Wai ko ba za ku zo mu tafi ba ne?<br /> Yau na ga yara.<br /> Nusaiba ta leko tana kiran su.<br /> Sumayya ta wuce da saurarinta. Khadija ta biyo bayanta. Ya kamo hannayen su. Zainab tana tambayar sa,"Kai ya sunan ka? Ya dube ta ya ce,"Suna na mai son Anti."<br /> Suka kwashe da dariya,"Wannan suna, ban ta6a jin irin sa ba."<br /> Inji Mahadiyya,"Ya ce,"Ga shi yau kin ji. Ko a gida aka tambaye ki, ki ce mai son Anti, sunana."<br / > Ta ce,"To."<br /> Ya debo kwalayen cakulet 2 da biskit 2, ya mika ma su. Suka yi godiya.<br /> Wajen biyan kudi, suka same su, duk cin maganin Nusaiba sai da Ibrahim ya biya kudin.<br /> Suka shiga mota, yana tsaye yana tunanin ta yaya zai binciko gaskiyar lamarin? Sun bada baya kadan, ya manta bai ma tambayi inda gidan su yake ba.<br /> Ya zabura da sauri, ya fada motar shi, ya bi bayan su.<br /> A haka a hankali yake bin su.<br /> Nusaiba na jin Mahadiyya na tambayar su,"Kun san sunan mutumin nan? "Wai mai son Anti."<br /> Gabanta ya fadi, ta zaro ido.<br /> Sumayya ta ce,"Ah lallai ma wannan.<br /> Antin Nusaiba, wai kin san shi ne? Ta ce,"Ina fa na shan shi, ku da ganin mutum kun tsaya ku na surutu da shi." Ta ce,"Anti ba ki san shi ba, shine ya san sunan ki da na Ameer? Ta ce,"To saura in ji maganar a bakin Anti, sai na murje bakin yarinya." Sumayayya ta kwa6e fuska, ta dubi 'yan uwanta, suka kama dariya,<br /> suna toshe baki.A haka suka iso gida, yana biye da su. Yana kallo suka shiga get, yana kallo duk suka wuce cikin gida.<br /> Farin cikin ya kama shi, domin ya san mai gidan.<br /> Injiniya Ahmad Kaita.<br /> Abokin ogan sa ne a ofis, kuma yana aiki da (Internet Global Services Jordan) ne."<br /> Suna da manya rassa a Potugal, Iraq, Swedan,. Hedikwatarsu na birnin New-York. Hamdala yayi, sannan yayi ribas ya koma, farin cikin zuciyar sa ya dawo sabo ful!<br /> Washe gari karfe 9, yana (Internet Globar Services). Ofishin Injinya Ahamd Kaita.<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ a<br /> Bai sha wahalar ganin sa ba, saboda dama sun saba gaisawa idan ya zo wajen ogan sa.<br /> Bayan sun gaisa, yayi masa bayanin abinda ke tafe da shi. Nan take dadi ya kama Injiniya, domin ya san Ibrahim mutumin kirki ne, ogansa ma na yabon sa.<br /> Nan take yayi maraba da shi, ya kuma ba shi kati, ya ce idan ya zo ya kira wannan lambar.<br /> Yayi godiya, ya fito.<br /> Ofishinsu ya wuce yana mai murna da farin ciki, babu abinda yake hangowa, sai an daura auran sa da Nusaiba.<br /> Wai! Yaya zai ji ranat? Yayi sauri ya dafe kirji, dadi zai kashe shi.<br /> Injiniya na koma wa gidan kan sa ya kira Nusaiba, ya gaya mata anjima za ta yi bako, kuma yana rokon ta, don Allah ta ba shi hadin kai, domin mutumin kirki ne.<br /> Ta amsa da to.<br /> Ta koma dakin ta, ta yi iya tunanin ta, amma ta kasa gano mai neman dama mata lissafi. Su Sumayya da sun rantse sun maya ba su gayaea Ibrahim gidan su ba, balle ya san mai gidan.<br / > To ko hadin Injiniya ne? Ta tambayi kan ta. Ta runtse ido takaicin duniya ya isheta.Dan ta karami, an dame ta da maganar aure.<br /> Ita kuma ba shine a gaban ta ba, tana son isashen lokaci, don kula da dan ta.<br /> Ta sallaci isha'i. Bayan cin abinci.<br /> Wankan ma ta ki yi, balle ta gyara jikinta.<br /> Yadda take tun safe, haka take zaune tana tana jiran ta ga dan rigimar dake neman auranta.<br / > Bata gama tunanin ta ba.<br /> Zainab ta zo da gudu ta gaya mata sako, inji Abbanta.<br /> Ta kura wa Ameer ido dake barci, sannan ta wuce ta fito.<br /> Zuwa karamin falo, inda aka ce bakon yake.<br /> Kai,"Inna-lillahi"Wa-Inna-ilahir-raji'un!<br /> Haka ta fada lkcn da ta yi ido 4 da Ibrahim.<br / > Ya ce,"Dole ki yi salati, kin ga mayaeb zai cinye ki."<br /> Ta ce,"Saboda Allah menene na bn diddigi? Ya girgiza kai,"Ba ki ma sani ba?<br /> Lallai yau ne na gane cewa da hadin bakin ki Abba ya hana ni auran ki."<br /> Ta dan yamutsa fuska,"Allah ne,Abba bai isa ya hana ka ba."<br /> Kin di ni baki Nusaiba, kuma hakan yana k'ara min son ki.<br /> Wannan karon da alamun nasara, ki dubi tsawon tazarar dake tsakanin Najeriya da Jordan, amma Allah ya ce je ki Nusaiba mijin ki na can." Ta yi dan murmushi, ta rasa me za ta ce da shi."<br /> Ba karamin dadi murmushi ta yasa shi ba.<br /> Ya dan langwabar da kai, ya sake fadin,"Kamar an fama min gyambo Nusaiba, tun ranar da na sake ganin ki tare da Sakina, kodayaushe sai mun yi hirar Ameer ni da Husna, shi yasa har yanzu bata mance da shi ba.<br /> Da gangan ki ka batar da lambar da Sakina ta ba ki, saboda ba kya son in san komai game da ke? <br /> Ta ce,"Tabbas haka ne, na kuma kar6i lambar ta ne kafin in san ko ita wace ce, da na zo na sani, sai na kiyayi kai na, saboda tunanin me zai je ya dawo?<br /> Ya jinjina kai,"Kin yi gaskiya, amma da yake Ibrahim mai sa'a ne sai ga shi abinda ya je, ya dawo din.<br /> Ko ba haka ba? Saura a ban dama, ayi ta ta kare"<br /> Ta ce,"Yaro na karami ne, ban ko yaye shi ba, da dai............<br /> Ya katse ta,"Ki na nufin Ameer? Je ki ji yadda yayi suna a gida na, balle kuma ki kawo min shi, gaba daya zai zama da na.Ta ce,"Ban tsara masa hakan ba."<br /> Ko?<br /> Ta ce,"Tabbas."<br /> Yayi dan shiru, kafin ya ce,"Ba kya so na dai ke nan."<br /> Ta ce,"Ban fad'a ba."<br /> Ya ce,"Idan ba haka ba,"Ameer ne kawai zai hana ki k'i aure na? Ta nisa kafin ta ce,"Har da matarka, domin na lura Sakina na son ka da yawa, bai kamata in shiga tsakanin ku ba.<br /> Mun yi hira sosai da ita a jirgi, amma ka na zuwa, ka nuna mata ka sanni, shi ke nan ta sauya min fuska.<br /> Ka ji dalilin yaga lambar da ta bani, don ba na son tashin hankali."<br /> Hankalinsa ya tashi kwarai, ya ce,"Ba ki fahimce ta ba ne Nusaiba.......<br /> Ta ce,"Haka ne Wallahi, ai ka ga lokacin ba ta ma san halin da na ke ciki ba.<br /> Ta ganni da Bebi, ba ita ba, kai kan ka ka yi zaton ina gidan mijina.<br /> Quite O.K a lokacin ba mu rabu ba, sai daga baya.<br /> To ina ga ace ga shi za ka aure ni?<br /> "Babu abinda zai faru. Haka Sakina take, bata iya rufe kishin ta, amma bata da fada, idan ku ka fahime juna za ki gane tana da hakuri."<br /> Ta ce,"Na ji."<br /> In turo kenan?<br /> "Ai na gaya maka ba yanzu na shirya yin aure ba."<br /> Ya runtse ido, dafe da goshi ya ce,"Nusaiba ba kya so na.<br /> Please!<br /> Ki je ki yi shawara, abinda ki ke fadi ba hujja bace."<br /> Ya bata tausayi kwarai, amma gaskiya ba za ta iya aure yanzu ba, shi yasa haka suka tashi hirar babu fahimtar juna, kowannan su ya koma cike da tunani.Musamman Ibrahim da yake ganin Nusaiba na son ta yi wasa da rayuwarsa, bayan ya lashi takobin wannan karon, sai ya ga abinda zai ture wa buzu nadi."<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Abubuwa da dama suke damun Nusaiba, ta kan ji kamar ta tsero ta bar k'asar, domin Injiniya da Antina sun tasa ta gaba, akan zancan Ibrahim, kamar yadda shi kan sa ya addabe ta da zuwa.<br /> A hak'ik'anin gaskiya tana tunanin Istaharar ta, kuma tana aji a jikin ta akwai maganar da Naseer yake son gaya mata, dama ce kai bata ba shi ba.<br /> A wannan gwagwarmayar suka shafe shekarar har ta yaye Ameer, yana neman wata 6 da yaye.<br /> Ibrahim bai hakura ba, ita kuma bata sakar masa ba.<br /> Anti kam har ta yi fushi ta daina yi mata magana, kamar yadda Injiniya ya