Sashe 13
A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
kodayake yana min godiya ne akan dauko Ameer da aka yi, har ya ce zai zo musamman yayi min godiya.<br /> Nace ya bar shi kawai, ta wayar ma ya wadatar, na kuma ji dadi. To koma dai menene, ban son mutane su dame ni akan maganar nan.<br /> Lokacin da zan ba Naseer 'ya ta ban yi shawara da kowa ba.<br /> Shi yasa ban son kowa ya sanya min baki, duk hukuncin da na yanke. Na riga na yanke shi. Saboda haka na kira wayar Fatima, na gaya mata za kikoma Jordan, ni zan kar6ar miki takardarki ki a wajen Naseer.<br /> Ina fatan hakan yayi dai-dai.<br /> Idan kuma akwai gyara ina jin ku?<br /> Ummi ta ce,"Zabin Nusaiba ne, me ki ka gani? Ta ce,"Hakan ya ma fi Abba na.<br /> Hankalina zai fi kwanciya."<br /> Ya ce,"To shi kenan.<br /> Insha Allahu nan da kwana 3 za ki bar kasar nan.<br /> Allah ya kawo miki mai son ki, ki aura."<br /> Ummi ta ce,"Amin."Sun jima suna hira nan, kafin Nusaiba ta dawo dakinta, duk bata da kuzari a jikinta, ita kanta bata san dalilin ba. Ta dan kwanta don ta huta. Sai ga Ummi da Ameer ya sake tashi barci.<br /> Ta kar6e shi. Ummi ta fice.<br /> Bayan ya gama sha tashinfidar da shi, ita ma ta kwanta tana fuskartar shi. Rike yatsun sa ta yi tana dan kada su, tana murmushin jin dadi. Sai da ta ci abincin rana, sannan ta kira Kausar suka kebe. Ita ma Kausar din ta goyi bayan Alhj akan komawar Nusaiba Jordan, domin a ganin ta zatafi samun nutsuwa.------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> ~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~<br /> Al'amarin Naseer kuwa, bayan ya baro wajen Yakubu, don jin yadda suka yi da Alhj, ransa 6ace ya isa gidan su Zarah.<br /> An riga anyi sallar la'asar. Yana shiga Inna ta yi masa albishir da cewa su Nusaiba sun zo, sun dauki Ameer. Take nan yayi wa Ubangiji sujada, yayi godiya gare shi, sbd tsabar tausayin da Ameer ke ba shi.<br /> Nan da nan wani yanki na 6acin ran sa ya goge. Sai da ya natsa. Inna ta sake fadin,"Sannan su zo nan sun rarrashi Zarah, ta ce za ta koma, nan ma kai take jira, dama kuma ko ba ka zo ba, ni zan maida ta anjima." Ya numfasa, kaunar Nusaiba ta k'ara shigarsa.<br /> Yarinya mai hankali, haka kawai ya tsaneta. Ko me yasa? Ya karkada kai ya ce,"Inna na gode. Ina Zaran take? Ta zo mu tafi." Ta ce,"Tana nan a ciki tana jin ka." Ya mike daga inda yake zaune, ya shiga dakin. Tana zaune bisa kujera, jakarta na aje gefe.<br /> Ya tsaya kan ta ya ce,"Sai na miki dukan musulunci tukuna, bari ki gani." Ya nad'e gefen rigar sa, ya tsula mata." Ni ki ke ba wuya ko? Ta 6alla masa harara. Ya mammare kuncinta. Idanuwanta suka kawo kwalla, sbd Nusaiba da ta fado mata rai.<br /> Ya tsugunna ya kama kunnuwan sa 2, ,"Na tuba." Ya zura mata ido, tana share kwalla," In dai amarya ce, ki kwantar da hankalin ki. Insha Allah za ta dawo. Taso mu tafi." Bata tanka masa ba, ta mike tana ci gaba da share fuska, ya dauki jakar tayo waje, ya biyo ta.<br /> Inna tana zaune, suka sallame ta, ta k'ara jajja masu kunni, suka tafi.<br /> Ko cikn mota ta k'i magana, ya dubeta, yayi d'an murmushi,"Zarah manya,<br /> yanzu ke ma ko tausayina ba kya ji, ina ku ke so in sa raina?<br /> Ta yamutsa fuska, a karo na farko, ta ce da shi.<br /> Oho?<br /> Ai dama wanda bai ji bari bari ba, zai ji hoho! <br /> In banda son kai ma, wa ka ke zaton zai tausaya maka?Ya ce,"Ke mana sanyin raina. Ina ganin ai saboda ke hakan ta kasance, sbd sonki kadai na aje wa zuciya ta. Bai kamata ki juya min baya ba, idan duka duniya sun dora min laifi.<br /> Kalaman sa suka sa jikinta yayi sanyi, ta yi dan shiru kafin ta ce,"Na san haka yayana, amma lokacin da kowa ke gaya maka gaskiya, bai dace ka ki daukar maganar na gaba da kai ba.<br /> Yanzu ina amfanin abinda ya faru? Ya kamo hannunta ya ce,"Wallahi babu, ban ta6a gane ni ba ni da wayau ba, sai wannan karon Zarah. Abin kamar almara na ke ganin sa."<br /> Ta ce,"To yanzu menene abin yi? Ya ce,"Gaskiya ban sani ba, domin Yakubu ya je, amma Alhj ya ce mai kama da ni ma bai son gani, balle ya ji wata magana akan bikon Nusaiba.<br /> A karshe ya ce masa ya riga ya soke ni a rayuwar sa.<br /> Kin ji bayanin Alhj, sbd haka ni ban da wata dabara."<br /> Ta yi tagumi, kafin ta ce,"Tabd'i!<br /> Kai yanzu in tambaye ka tsakanin da Allah, ka na son amarya ta dawo? Ya dube ta ya ce,"D'ari bisa d'ari na zuciyata ke kaunar Nusaiba ta dawo, sbd ta yi min abinda ba zan ta6a mancewa da ita ba a rayuwa."<br /> Ta ce,"To ka gwada wannan dabarar ka gani. Ka ajiye wani tura mutante wajen sa, ka tafi da kan ka, ka ce masa, sai ka ga abinda ya ture wa buzu nadi.!Duk wata bak'ar magana da wulak'anci, ka jure shi, da kansa zai hakura, yana ji, yana gani zai sakar maka 'yar."<br /> Yayi d'an murmushi,"Zarah ke nan, bai saurari manya ba ma, sai ni uban laifi? To zan gwada. Amma ni kunya ma na ke ji mu hada ido da shi." Lallai ba sokake ta dawo ba, kunya ai murje ta ake yi." An gama Zarah,"Allah yasa amarya ta dawo, ko don in huta da ciwon kai."<br /> Ta 6allo masa harara, ya dube ta yayi murmushi,"Ai kin ga na dan sami sauki, ko hararar na rinka sha ta isheni jin dadi." Ta d'an buge shi a kafada,"Allah za ka sani yayana."<br / > Ya take birki a kofar gida, ta dauko jaka a kujerar baya, ta fito ta riga shiga gida. A falon Umma ya isketa.<br /> Umma na mata fada. Ya zauna gefe ya ce,"Umma sun zo sun kar6i Ameer ko?<br /> Cikin rashin kulawa ta ce,"Sun zo."<br /> Ya ce,"An gode ma su."<br /> Ta yi biris da shi ta ci gaba da mgnr ta da Zarah. Jimawa kadan ta koma sasan su, ta yi share- share da goge-goge.<br /> Har dakin Nusaiba ta gyara shi, ta goge zuciyarta na saka mata lallai amarya za ta dawo da zarar Naseer ya je da kan shi.<br /> Kwana 3 kenan Naseer ya kasa zuwa Kaduna, sbd kunya da jin nauyin Alhj. Yau kan Zarah har kuka tayi masa, tana hada shi da Allah da Manzon sa.------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Yayi shiri tsaf!<br /> Ya biya ya dauki Sageer suka danki hanya. Gida suka fara zuwa. Mai gadi ya ce ma su babu kowa cikin gidan, duk sun yi tafiya.Daga can ofis suka nufa, sakataransa ya gaya masa Alhj ya tafi Abuja.<br /> Kai abinda babu sa'a. Haka suka dawo jiki babu kwari tare da mamakin ina za su je kuma gaba dayan su har da Nusaiba?<br /> Koda suka dawo irin tambayar da Zarah ta rink'a yi kenan.<br /> Har ta k"arawa Naseer haushi ya ce,"Wai ina zan sani ne Zarah da ki ka dame ni da tambayar nan?<br /> Haba!<br /> Yayi tsaki, ya tashi ya bar mata gidan, don sai su yi fada.------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Karfe 10 na safiya su Alh. Basheer na filin jirgin. An gama bincike, an tantance Nusaiba da Ameer tare da kayayyakin ta. Suka yi sallma da su Ummi, ta wuce tana hawaye sabeda Ameer bisa kafadarta, hannunta daya yana kan Beby. Sai dai jirgin da za su shiga, sai sun dan jira shi, ya gama hutawa.<br /> Kamar yadda aka bada sanarwa.<br /> Duk fasinjojin da ake tantance su, na zaune falon, kafin a ba su umurnin shiga jirgi. Nusaiba ta zo ta zauna kusa da wata mata.<br /> Ita ma rungume take da Bebi cikin shawul, ga wata yarinya a tsaye gaban ta, za ta kai shekaru 4.<br /> Tana zama, ba ta yi aune ba, ta ga yarinyar nan a gabanta, tana ta6a Ameer,"Bebi! Mamanta ta juyo tana murmushi ta ce,"Husna ba kya ji ko? Ba na ce ki tsaya waje daya ba? Ta ce," Umma kin ga Bebi mai kyau? Zo ki gan shi."<br /> Suka fara dariya.<br /> Nusaiba ta ce,"In ba ki shi ne ku hada da na ku? Ta ce,"Eh.<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Ya sunan shi? Ta ce,"Ameer, ke ya sunan ku? Ta ce,"Adnan.<br /> Mamanta ta ce,"Oh ni, kin ji dadin halinki Husna."<br /> Ko a jikin ta, sai k'ara kwanciya take jikin Nusaiba, tana wasa da kuncin Ameer.------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Tun daga nan hira ta goce tsakanin Maman Husna da Nusaiba.<br /> Kamar minti 15, aka sanarwa fasinjoji. Su wuce su shiga jirgi.<br /> Tare suka sa6a yara suka wuce, ita fa Husna bata yarda ba, son Ameer take yi, don haka Nusaiba ta kamawa jaka tana bin ta da gudu.(First class) dukkan