← Book details A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 28

Sashe 12

A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ajininsa yake 3-03 Posted by ANaM Dorayi on 11:46 PM, 21-Nov-15 _______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______<br /> Fa ce,"Ita ma ba za ta zauna ba.<br /> Sai Nusaiba ta dawo.<br /> Kin ga ya 6ata 2 kenan, sai wani gyaran Allah.<br /> Nusaiba ta dafa kirji ido waje, sun kawo kwalla, ta dubi Ummi ta ce,"Me yasa Antina za ta yi haka? Ai ni ba zan ta6a dawowa ba, yakamata yayi ta gane wamman.<br /> Ummi mu je in debi kayan, mu wuce wajen ta."<br /> Suka mike, Umma ta kawo makulli. Nusaiba ta debi kayayyakin da take son diba. Abubuwan dake firj din ta duk ta kwaso ta kaiwa Umma. Bayan Direba ya zuba kaya a mota, suka sallami Umma suka rabu suna daga wa juna hannu.<br / > Babu Abinda zata yi, Nusaiba ta hana ta tafiya, babi abinda za ta iya yi.<br /> Duk iya kaunar da take wa Nusaiba data zauna dakinta, dole ta kyale.------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Babban abin godiya ma shine, da suka tausayawa baWan Allah suka zo da kan su suka dauke shi.<br /> Shi yasa take ta yi wa Allah godiya, ba 6ata lkc ta kira wayar Abba a kasuwa, ta shaida masa. Ba karamin farin ciki yayi ba, domin rabon sa da fara'a tin asubahin jiya. Sai kuwa yau da aka ce su Hjy sun zo da kan su sun dauki Ameer.<br /> Cikin gidan su Zarah su kai sallama yanzu. Inna ta amsa. Ta leko daga dakin Malam Umar. Ah! Nusaiba! Maraba. Fit Zarah ta fito daga dakin Inna, baki har kunne,"Amarya! Antina." Zarah ta matso suka rungume juna." Kin dawo ko amarya? <br /> Ta daga ta dube ta,"Haba Antina, zo mu je daga cikin in gan ki."Ta kama hannunta suka shige daki. Inna ta ce,"Ke Hajiya shigo nan, kafin su gama ganawar. Ina fatan dai na dawo mata da amaryarta ne, mu huta." Bata ce komai ba, suka shige, tana 'yar dariya.<br /> Nusaiba ta dubi Zarah,"Me yasa haka Antina? Bai kamata ki yi wa yayanki haka ba." Ta ce,"Ni kuwa a waje na hakan ya kamata, domin ciwon 'Ya mace, duk na 'Ya mace ne. Na kuma shaku dake amarya tafiyar ki za ki ta jefa ni cikin wani yanayi na dacin rai."<br /> Ta dafa kafadar ta, ta ce,"Kin fadi gaskiya,"Antina, kuma na san ki ni nuna min iyakar kaunar da ba duka mace za ta nuna wa abokiyat zamanta wannan kaunar ba.<br /> Allah ne ya kaddaro zan sami Ameer, amma ke ce sila Antina.<br /> Ban mancewa har ta kai ki ga rasa na ki cikin. Ina so ki sani Naseer, yana da halayya masu kyau, yana da kula tare da tsare hakki, ni ce kawai da bai so yake nuna min banbanci.Bai damu da ni ba, balle ya kula da hakkoki na. Kar ki damu Antina, ba laifin yayanki ba ne. Allah ne bai sa masa soyayyata ba, saboda haka na ke rokon ki idan ya zo daukan ki, ki yarda ki bi shi, domin ke ce rayuwar sa.<br /> Ke yake so, da ya ke yake ra'ayin zaman aure. Abin alfaharin ki ne a wannan zamanin da ki ka sami miji kamar Naseer, mai tsayuwa akan alkawarin soyayya. A karshe ina son ki sani, har karshen rayuwata ba zan ta6a mancewa da ke ba Antina. Hasalima dole wata rana Ameer wajen ki zai dawo, kin ga har yanzu mu na tare ke nan. Kin hakura ko?<br /> Abinda ya fi ba Zarah mmk, shine ashe Nusaiba na sane da abinda ya faru kafin Naseer ya shiga dakin ta. Gaskiya Nusaiba mai hakuri ce, irin wanda sai an sha bincike kafin a sami irin sa. Ta zura mata ido cike da kwallan tausayi. Allah na ganin bata son rabuwa da amaryar ta.<br /> Nusaiba ta kamo hannun ta, ta dora bisa kan ta,"Ki yi min Alkawarin Antina, a yau za ki koma dakin ki, ba gobe ba, kin ji? Ta goce da kuka, suka rungume juna, haka wahayen ya kubce wa Nusaiba,"Za ki koma ko? Ta dago ta goge kwalla ta ce,"Zan koma Amarya, amma kema ina rokon ki idan a an dai-daita da su Abba, don Allah kar ki kafe ki ce ba za ki dawo ba.Ta yi dan murmushi, ta ce,"Shi ke nan, bari mu zo mu tafi, sai mun yi waya, shi kenan na ji, alkawarin za ki min kamar yadda na yi miki." Ta yi dan jim, kafin ta ce,"Ai ba laifi na bane Antina, ke ma ba za ki yarda in zauna inda ba'a so na ba."<br /> Ta kada kai.------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Da ke nan amarya, amma yanzu ina mai tabbatar miki yayanmu yayi nadama, ko bai gaya min da bakin sa ba, ni na yi imanin yana son ki, ba ki ga yadda ya fita hayayyacin sa ba, lkcn da lalura ta kama ki kuma ya kula da ke yadda yakamata.<br /> Ta ce,"Anitina ki na so ki gyara yayanki ne kawai, amma ni na san tausayine irin na musulunci. Kin san musulmi mai imani ya kan tausayawa dan- uwansa a lkcn daya shiga wani hali.<br /> A bar maganar nan Antina, ki yi min addu'ar Allah ya zaba min abinda ya fi zama alkhairi."<br /> Ta numfasa, hannun ta bisa kafadar ta,"Zan miki amarya. Allah yasa alkhairin a gidan yayanmu yake."<br /> Ta mike tana dan murmushi, ta fito ba tare da ta ce komai ba, sbd bata son maimaita zancan. Dakin da su Ummi suke, suka yi sallama. Inna na rike da Ameer.<br /> Zarah ta nufi gun sa, ta dauka, Ummi ta ce,"Zo nan. Ta wuce wajen ta da Bebi a hannun ta, ta tsugunna gefenta, ta dafa kafadar ta, ta ce," Zarah ba'a wasa da aure, hkr za ki yi ki koma dakin ki kinji?Kan ta sunkuye tana dan ta6a kuncin Ameer, ta amsa da kai, sannan ta ce,"Wallahi Ummi Naseer ya gane kuskuren sa, tun jiya yake kuka, yana bin mutane ya samu aje masa biko. Abban sa ne ke fushi da shi, ya ki bada hadin kai.<br /> Don Allah Ummi, ku yafe masa ku bar amarya ta dawo."<br /> Ta ce,"Babu abinda Innar ki bata fada ba yanzu, amma Naseer ya riga ya rushe katangarsa.<br /> Alhj na da saukin kai, sai dai idan ka ta6i shi, nan ne za ka gane ma yana da zafi.<br /> Saboda haka ku taya mu addu'a. Allah yayi masa zabi." Zarah ta yi shiru idunwanta suka kawo kwalla. Ummi ta mike, ta ce,"Allah yasa mu gana." Duk suka tashi suna fadin Amin.<br /> Har mota suka rako su, sannan Zarah ta mikawa Ummi yaron. Ta dubi Nusaiba, kowacce hawaye ya zo mata, suka rungume juna. Da sauri Nusaiba ta shige mota, haka ita ma Zarah ta ruga cikin gida, bata son ganin tafiyar Nusaiba.<br /> Hawayen ta suka yawaita, tana sharewa, wasu na sauka. Direba ya damki hanya. Nusaiba ta yi shiru cikin mota, ta sak'a wannan, ta kwance wancan a game da maganganun Zarah. Tabbas su Abba sun gaya mata Naseer yayi dawainiya da ita sosai a cikin kwanakin nan 50 da ta samu kanta a wani yanayi.Sai dai babu wanda zai tantace me Naseer ke nufi cikin ransa? Ko ita ma Zarah hasashe ta yi, domin da bakinta ta ce bai fito fili ya gaya mata ba.<br /> A cikin tunanin ne ta ji Ummi na fadin,"Ke ba shi nono ya sha, ya farka."------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Ta dube su firgigi. Ummi na masa mika tana cewa ka sha barci ko? Nusaiba ta mika ruwa aka ba shi, sannan ta karbe shi, ta mika masa nono ya kama yana sha.<br /> Nan da nan so da kaunar sa suka kara shiga zuciyar ta har bata san lkcn da fa kura masa ido ba.<br /> Karo na farko da ta tantance kamanin danta.<br /> Tamkar Ameer na farko. Haka kuma hoton Naseer take gani zahiri bisa cinyoyinta. Tsigar jikinta ta tashi yar!<br /> Saboda kyan surar yaron nan, musamman daya buda ido tar!<br /> Yana dube-duben sa.<br /> Ya sha sosai. Ta juya shi daya gefen, nan ma ya sha mai isar sa. Bai koma barci ba. Ummi ta karbe shi, ta ci gaba da renon mai gida.<br /> Jimawa kadan Kausar ta kira wayar Ummi, ta mika wa Nusaiba ta ce,"Ungo Kausar ce." Ta kar6a da saurinta, ta danna O.K."<br /> "Hello."<br /> Ta ce,"Hello Nusaiba ya karfin jiki? Alhamdulillahi."<br /> Ta ce,"Ya maganar Bebi ne? kin san Allah jiya ban yi barci ba." Ta ce,"Bisa hanyar komawa gida muke yanzu, mun je an dauko shi.Ta nisa ta ce,"Better. Ai ni ba zan iya ba, ka aje a jariri, ai ka cuce shi.<br /> Shi me ya sani? Ta yi dan murmushi,"Kausar kenan."<br /> Ta ce,"Tare ku ke da Ummi ko? Bari in yi shiru, idan kin kebe, kya kira ni. Ku sauka lafiya." Ta ce amin. Ta kashe waya.<br /> ~~~~~~~~~~~~~~~~~~~­ ~~~~~~~~~~------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sun iso gida 2 rana. Alhj na falon kasa. Suna isowa Ameer yasa a kafada ya haye sama, yana fadin "Ku hayo sama in gan ku."<br /> Suka haye suka bar Direba na shigo da kaya. Mariya na taya shi. Bayan sun natsa a zaune.<br /> Alhj ya dube su ya ce,"Bayan tafiyar ku. Yakubu ya zo min da maganar Naseeer, haka shima M.Balarabe ya kira ni a waya,
Chapter 12 · 0% Book details