Sashe 17
A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ajinisa Yake3-04 Posted by ANaM Dorayi on 05:24 AM, 23-Nov-15 Under: Ajininsa yake _______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______<br /> Zan yafe maka komai, ya wuce har abada, amma sai ka kawo min takardar Nusaiba."Kansa cikin giuwa, ya girgiza kai, ya ce,"Ba zan iya ba Abba, ka yi hkr." Ya ce,"Wannan ba hukunci na ba ne.Nusaiba ce ta buk'ata ta kuma bar min sallahu jiya kafin su wuce Jordan.." Ji yayi numfashinsa ya shake gaba daya, yana neman faduwa.<br /> Ya kasa motsi, balle ya ce wani abu. Ya ci gaba da cewa,"Na ba ka nan da jibi ka zomin da takardar, daga nan zan maka bayanan wasu abubuwa da suka kamata ka sani.<br /> Ka na iya tafiya dare yana k'ar yi." Ya dago idanuwa jajur! Ya ce,"Ummi ku taimake ni, ku ba ni lambar ta mu yi magana, na san zata saurare ni. Amma a raba auran a haka, abin babu dadi.."Abba ya ba shi amsa,"Ban son dogon nace Naseer, raina k'ara 6aci yake yi. Kwanciyar hankalin na da kai shine ka kawo min takardar Nusaiba. Yadda ba ka so, haka ita ma bata so, shi kenan magana ta k'are babu lallai babu tilas."<br /> Ya sunkuyar da kai, yayi shiru. Ummi ta ce,"Yakamata ka tafi, dare ya fara yi Naseer, muna sauraronka."Yayi wawan ajiyar zuciya, ya mike da kyar ya ce da su,"Sai da safe,gaba daya suka amsa,"Allah ya kai mu, a gaida mutan gidan."Bai k'ara komai ba, ya sakko a hankali ya tafi.<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Karfe 11 dare, ya shigo gida,. Zarah na zaune a falo ta ci uban tagumi, ya turo kofar ya shigo." Ta mike tsaye da sauri ta tarbe shi."<br /> Yayana!<br /> Kai kuwa ina ka shiga yau?<br /> Bai tanka ba, ya wuce kujera ya zauna, ta bi shi hannun kujerar ita ma ta zauna. Ganin yayi zuru- zuru, yasa tausayinsa ya rufe ta.<br /> Ta nunfasa ta ce,"Ina ka je yayana? Ya ce,"Kaduna na koma." Ya aka yi to? Ya mayar mata da abubuwan da Alhj ya ce,yayi shiru ta rasa ta cewa. Ya kwanto da kan sa bisa cinyoyinta, shi ma ya yi shirun Ta dafa kan sa ta ce,"Kai yanzu me ka shawarta."Ya ce,"Na hukara Zarah. Allah na gani na yi ikayar kokarina. Abinda ya fi damuna maganganun da Alhj yayi. Ba k'aramin dafa min jiki suka yi ba, sbd a zahiri Alhj masoyina ne.Sai kin ga yadda ya cika hotuna na a falonsa, kya rantse da Allah ni ne dan masu gidan.<br /> Ni dai na yi abin kunya, ban san ta yadda zan yi in wanke kai na ba."<br /> Ta ce,"Gaskiya ne, amma duk da haka ka tuntubi su Umma ka ji ko za ta ce wani abu." Ya mike ya wuce bayi, yayi wanka ya ji sanyi a jikin sa, sannan ya kwanta.<br /> Zarah na k'ara kwantar masa da hankali.<br /> Da safe ya shiga wajen su Umma ya gaishe su.<br /> Abba bai amsa ba, ya tashi ya koma cikin daki.<br /> Daga can yana jin duk bayayin da yake wa Umma.<br /> Yana gamawa ta ce.<br /> "To ne menene nawa a ciki? Duk abinda ka ga ya dace, ka yi, tunda wannan 'ya ba ta mu bace, k'arewa ma ka ce bata k'asar.<br /> Ka ga da gaske Abbanta ya ke yi." Yayi dan jim kafin ya mike, ya bar falon.<br /> Umma ta bi shi da kallo, tausayin sa ya dan kama ta, ta kada kai ta ce,"Kai ka jawo wa kan ka."<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sati 1 Naseer yayi yana sintiri Kaduna, wai ko ya sanmi sauyin baki daga Alh.Basheer, amma sam babu.<br /> Yau daya je ma. Alhj cewa yayi yau ce rana ta karshe daya ba shi, idan bai kawo takardar ba, to kar ya sake zuwa gun sa, kuma duk abinda ya biyo baya, kar ya ce yayi masa wulakanci.<br /> Babu yadda zai yi, a daren ya rubuta takarda, saki 1 ya sa a ambulan ya rufe.<br /> Washe gari ya isa gida, ya sami Alhj yana shirin fita.Bayan sun gaisa Alhj, na kallo irin ramar da Naseer din yayi. Ummi ta zo suka gaisa. Yasa hannun aljihu ya ciro ambulan, ya tsugunna ya mika wa Alhj. Ya kar6a, ya buda, ya karanta, bai ko karasa ba, ya rufe saboda irin lausasan kalaman da ke cikin takardar.<br /> Ya dube shi ya ce,"Magana ta kare Naseer, kuma duniya da lahira na yafe maka abinda ka yi min. Son ka a cikin jini na yake, na rantse da Allah ba zan iya cire shi ba, saboda haka ka saki jikin ka, kai da na ne.<br /> Magana ta 2, ita ce,"Gida da motocin da na ba ka, mallakin ka ne, ba na bukatar su. Abinda na ke son ka da shi ne, ka dauki Zarah ku koma can da zama.<br /> Wannan umurni ne a matsayin na Babanka."Gaba daya tsigar jikinsa suka tashi yar! Idanuwansa suka kawo kwalla.<br /> Ya zamo daga kujera ya ce,"Na gode Abba. Allah ya saka da alkhairi."<br /> Ya ce,"Koma ka zauna. Yanzu yaushe za ka kammala karatun ka? Ya sunkuyar da kai, kunya ta rufe shi, ya rasa me zai ce? Da kyar ya daure ya ce,"Ai dama ban fara ba."<br /> Da mamakinsa ya maimaita ,"Ba ka fara ba? To da ka ce min ka na zuwa?<br /> Ya sunkuyar da kai, kamar ya ratsa kujera ya shige. Alhj yayi dan murmushi ya ce,"Allah da iko yake, yanzu yaushe za ka fara? Kidimewa tasa ya ce,"Gobe." Ummi ta ce,"Gobo kuwa? Ba dai gobe- gobe ba, ai kuma sai an sake nema ko? Ko kuwa ka na da "(Admission) ne a hannun ka?<br /> Ya girgiza kai,"A'a.Duk sun lura a daburce yake, saboda haka Alhj ya ce,"Shi ke nan, ka je ka yi duk abinda ya kamata, idan ka sami ( Admission) din ka kawo min." Ya ce,"To na gode Abba."<br / > Ya kosa ya tashi saboda tsarguwa, zufa ce kawai ke kwararo masa cikin riga.<br /> Yana samu aka sallame shi, jikin sa na rawa yayi godiya, ya fice.<br /> Alhj ya dubi Ummi ya ce,"Kawai Allah ne ya dora min son yaron nan, ba don haka ba, inda na ke ma idan aka ce ya zo da kudi ba zai zo ba."<br /> Ta ce,"Ya za'ayi, ga kuma zuri'a a tsakani, dole a rage wani abin." Ya numfasa yana kada ambulan, sannan ya mika mata,"Karanta ki ji bayanan dake ciki." Ta kar6a ta karanta, ta yi dan murmushi ta ce,"Allah sarki da alama ya saduda Alhj."<br /> Ya ce,"Kyale ni da shi dai."<br /> Ta ce,"Na kyale."<br /> Kowa ya ji abinda Alhj yayi, sai ya sanya masa albarka.<br /> A hakikanin gaskiya Alh.Basheer mutum ne wanda ba'a samun su a wannan zamanin, sai an shekara ana bincike cikin mutanen kirkin da ake wa zaton suna da halin mutan da can. Karshen soyayya Alh.Basheer ya nuna wa, Naseer shi yasa Naseer din ke k'ara nadama kan nadama, so da kaunar Nusaiba ke k'ara dabaibaye zuciyarsa.<br /> Kewar ta ke jefa shi.<br /> Nisan tunanin ta musamman lukutan daya samu a asibiti yana jinyarta.Ya kan rink'a ganin kamar wata sabuwar rayuwar soyayya ce suka yi a tsakanin su, wacce yake mafarkin ci gaba da irin ta.<br /> Malam Balarabe kuwa kalaman godiya sun kare a bakin sa.<br /> Washe gari daya tafi Kaduna, ba tare da sanin kowa ba, don nuna girmamawa ga Alh. Basheer. Tabbas ya nuna halin girman, dole a jinjina masa. Haka shi ma Alhjn ya roke shi akan ya daina fushi da Naseer, tunda ya tuba, to ya kamata ya karbi tuban sa, sbd fushin sa tamkar dafi ne a gare shi.<br /> Malam Balarabe ya amince, yayi farin ciki ya kuma zubda kwallan bakin cikin rabuwar auran Naseer da Nusaiba.<br /> Ba 6angaran su Malam Balarabe kadai bakin cikin rabuwan auran ya dama ba, ita kan ta uwar gayyar, yau ta tsinci kanta cikin wani yanayin da bata gane masa ba, a tun lokacin da sako ya zo mata ta waya daga Nijeriya cewar ta fara iddar ta.<br /> Zaune take dirshan bisa gado, ta takure kanta, tunanin yayi mata yawa.<br /> Tana tambayar kan ta, ita kuma haka Allah ya kaddaro mata? Mutuwar aure ita ce matsala ta farko da ke ci mata tuwo a kwarya, a rayuwarta.<br /> Ta tsani, ace anyi aure ya mutu, sai ga shi yau ya tabbata akan ta.<br /> "Kaddara!<br /> Ta fada a ranta hawaye, suka kubce.<br /> Ta dawo tana zargin kan ta,"Watakila Naseer ya so ya gaya mata wata magana lkcn da ta wayi gari ta gan shi tare da ita asibitin, amma ta ki ba shi dama.<br /> Yi hakuri ki ba Bebinmu nono. Haba 'yar gidan Abba."<br /> Tabbas rarrashin ta yake yi, amma ta dauke kai, ta nuna bata san abinda take yi ba.<br /> Alhalin ta warke, hankalin ta ya dawo jikinta.<br / > Da kenan amarya, amma, a yanzu ina mai tabbatar miki yayanmu yayi nadama, ko bai gaya min da bakin sa ba, ni na yi imanin yana son ki.<br /> Ba ki ga yadda ya fita hayyacin sa ba.<br /> Lokacin da lalura ta kama ki, kuma ya kula dake yadda ya kamata!<br /> Ta toshe kunnuwanta ta daga kai.<br /> Idanuwanta tamau a rintse, hawaye suka ci gaba da sauka.<br /> Istaharar ta ta tabbata gaskiya.<br /> Bata sami isashen barci ba, sbd a yanzu take tunanin ya kamata ace ta ba Naseer dama shi da ita sun yi magana.<br /> Yanayin daya suka kwana ita da Naseer, domin a ranar suka koma Hanwa. Yayi sintiri a sashin ta iya yadda ya ishe shi, wanda a da bai ta6a shiga cikinsa ba. Tun Zarah na taya shi sintirin,