Sashe 14
A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
su za su zauna, sbd haka ga kujerar Nusaiba, ga ta su. Adnan da Manan sa. Su dai ba su yi sukuni ba. Sai da barci ya kwashe Husna. Sun sauka lafiya, ga 'yan tarbar 'yan uwan su nan fululu kowa na jira. Nusaiba ta dudduba, bata hango Antinan ba, haka Maman Husna ke fadin,"Husna kin ga Abbanki bai zo ba ko?<br /> Tana rufe baki ta yana kira,"Husna! Ta kwace hannun ta, ta bi 6angaran da ta hango shi." Abba!<br /> Karo na farko da Nusaiba ta dubi Abban Husna, sam bata gaskanta idanuwan ta ba. Ta kara duban sa da kyau, babu ko shakkar Ibrahim ne.<br /> Jikin ta duk yayi la'asar saboda al'ajabin sake haduwar ta da Ibrahim, wanda tuni ta mance da shi a duniya. Suna tafe Maman Husna na fadin,"Sai yaushe ke nan?<br /> Ta ce,"Ai ina hada layi na, za ki ji kira na. Ai ba zan yi wasa da lambar da ki ka ba ni ba, dole ne in kira Husna."<br /> Suka yi dariya. Nusaiba yanke tabi wani 6angare,"Bari in jira su Antina a nan. Ta ce,"Ah! Ba za ki sallama da Husnar ta ki ba." Ta ce kyale ta, ta ga Abban ta, ta mance da ni." To shi kenan, sai na ji ki." Ta wuce inda su Husna ke tsaye da Abban ta, duk da cukuikuye shi, ta hana shi sukuni.<br /> Babban yaron dake tare da shi, ya rugo ya rungume Maman su, shi ma zai kai shekara 6 ko 5 da rabi. Nusaiba na tsaye duk ta kosa Antinta su zo.......Ta bar wajen. Don bata son Ibrahim ya gan ta, kawai ji tayi Husna na rikota tana fadin,"Zo ka gan shi Abba, Bebi mai kyau."<br /> Gabanta ya fadi, ta waigo cikin tsarguwa, suna hada ido da Abban Husna ya ji kamar zai fadi, sbd faduwar gaba. Bai san lkcn da yayi zuru, ya zuba mata ido ba.<br /> Ta shiga dan yake, tana wa Husna magana,"Ke wai ba mun yi sallama tun a jirgi ba?<br /> Tsayuwayar Maman Husna wajen yasa Ibrahim ya dawo duniyar daya tafi, yayin da Husna ke fadin,"Abba na zai ga Bebi mai kyau.<br /> Ka gan shi? Suka fara dariya, ya kar6e shi ya dan daga sama ya ce,"Good day handsome Bebi!<br / > Yayin da Nusaiba ta juya tana tambyara sunan yayan Husna, ya ce,"Imran." Ta ce,"Uhnmm..............Sunanka da dadi." Husna ta ce,"Ni ma sunana da dadi. Ta kama habarta ta ce,"Sosai ma, ke mai babban suna ma ba'a fadi, shi yaya ake kiran ki Husna."<br /> Dadi ya kamata har da yi wa Imran gwalo.<br /> Ibrahin ya numfasa, ya dubi matar sa ya ce,"Gaskiya wannan haduwa tana da ban mmk. Ai dole ayi dalla-dalla. Wannan ita ce,"Nusaiban da na ta6a ba ki labari. Nusaiba ga Madan din na Sakina." Mamaki ya kama Maman Husna, take nan kishi ya kulle ta. Ta dan daure fuskata ta ce,"Ka ce min wacce ta kusan zarar min da kai.<br /> Nusaiba ma ta gyara fuska, ta ce,"Ki bar maganar nan Maman Husna ta riga ta wuce." Ya ce,"Sai zumunci ko? Yana da kyau, ina fatan kin bata adires, kafin ta koma, za ta kawo mana Ziyara."Sakina ta gyada kai tana yamutse fuska,."Na dai bata lambar waya."<br /> "Mts, ina ganin ya kamata mu wuce Abban Husna, na fara gajiya wallahi."<br /> Ya ce ,"Tunda ba'a zo daukan ki ba, why not ba za ki bi mu, mu sauke ki gida ba? Sakina ta kauda kai yayin da Nusaiba ke 'yar dariya, tana fadin,"Ku bar shi Allah na gode. Ai na san za su zo."<br /> Ta mika hannu ta kar6i Ameer a hannun sa.<br / > Ya maida hannaye aljihu, ya numfasa, amma bai iya cewa komai ba.<br /> Ta shashshafa kan su Husna ta ce,"Sai anjima ko Husna!? "Bye-bye Bebi, sai ka zo gidan mu." Suka yi sallama da Sakina, ba wata walwala a fuskarta, ganin haka Ibrahim yayi gaba rike da hannayen yaran sa.<br /> Sakinta ta bi bayan su cike da kishin babu gaira babu dalili.<br /> Nusaiba na nan tsaye, duk takaicin al'amarin ya dameta ta, kamar minti 5 da wucewar su.<br /> Antinta ta iso,"Allah sarki Nusaiba, sorry,"Wallahi sharrin mota ne, cak ta tsaya mana a titi da kyar Direba ya gyara."<br /> Yaranta mata duga guda 4, suka yayyame ta, kowa son ya dauki Bebi yake yi.<br /> Babu 6ata lkc. Direba ya kwashe kaya suka rankya.<br /> Tunda daga mota, har gida Antin Jordan ke balbala tsiya akan abinda ya faru.<br /> Dakin ta daban, aka ware mata ita da Bebin ta, bayan an gama duk kayaniyar ganin juna har da maigidan ya tofa na sa albarkacin bakin sa.<br /> Sai dai nasihohi yayi mata akan ta aje hankalinta waje daya, kar ta sa wa ranta damuwa.Daki ta koma ta yi wanka, ta yi alwala ta yi sallolinta. Gefen gado ta zauna tana tanunanin yanayin da suka hadu da Sakina, fara'a kamar gonar auduga, amma tashi guda ta sauya fuska, saboda mijinta ya nuna ya santa.<br /> Ta yi dan murmushi, ta ce,"Allah sarki Antina, alkhairin Allah ya kai miki."<br /> Ta sa hannu ta jawo jakar Bebi, ta daukko lambar da Sakinta ta bata a rubuce, ta sa hannu ta yayyaga, tana fadi a ranta,"Sa ran ki a inuwa Maman Husna, kullum ni da mijinki haduwar [Aiport] ce, rabuwar (Airport)." Ta matse a hannun ta, ta wuce bayi ta watsa (Dosbin).<br /> ----------------------------------------------------------------------------------------------- <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> ~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~<br /> Washe gari da wuri Naseer ya nufi Kaduna. Shi kadai kuma ya tafi, wannan karon zuciyar sa ta bushe, matar sa kawai yake son ta dawo.<br /> Shi yasa ya kwashe duk wani tunanin dake ran sa a game dake ran sa a game da tinkarar Alhj.<br / > Yayi fakin, ya fito kai tsaye falon yayi sallama.<br /> Mariya dake goge-goge, ta amsa sannan, ta durk'usa ta gaishe shi ya ce,"Hau sama ki kira min Ummi." Ta ce,"Tana ma kicin, bari na kira ta."<br /> Ya zauna Mariya ta wuce. Jin kadan ta dawo ta ce,"Ga ta nan zuwa." Ya share minti 5 nan, kafin Ummi ta iso falon.<br /> Ya mike kai sunkuye ya ce,"Sannu Ummi." Bata tanka masa ba, ta wuce ta haye sama. Yayi tsaye nan kirjin sa na harbawa.Bai sake ganin kowa ba, wucewar minti 30 har ya gaji da tsayuwa ya koma ya zauna.<br /> Can Alh.Basheer ya tinkaro falon.<br /> Ummi na rike da jakar sa suna maganganun su.<br /> Naseer ya kuma mikewa yayi tsaye irin na marasa gaskiya. Ko inda yake Alhj bai kalla ba, jakarsa ya karba. Ummi ta ce," A dawo lafiya." Ya ce,"Amin." Ya fice.<br /> Ummi na ta wuce kicin, ta ci gaba da hidimomin ta.<br /> Naseer yayi kamar ya nutse a kasa, jiki babu kwari ya biyo bayan Alhj, amma kafin ya karaso.<br /> Alhj ya shiga mota. Deriba ya tayar. Haka ya tsaya kamar dolo, yana kallo aka bude get.<br /> Motar ta fice. Ya wuce ya shiga ta sa, ya bi bayan sa.<br /> Ofis ya ga sun nufa, shi ma ya bi su. Yana zuwa zai wuce sakatare, ya ce,"Alhj ya ce ka dan jira shi a nan tukuna."<br /> Ya ce,"To." Ya zauna.<br /> Shi kansa sakataran dauke da mamaki yake, domin bai ta6a yi wa Naseer iso ba wajen Alhj.<br /> Yana nan zaune Alhjn ya kira waya, ya bada izinin Naseer ya shigo.<br /> Ya mike ya tura kofa, ya sjiga Alhjn na ta aikin sa bisa (Laptop), bai ko kalle shi ba. Ya duka ya gaishe shi, ya amsa a dakile.<br /> Yayi shiru, haka shima Alhjn bai dube shi ba.<br /> A haka ya daure ya fara magana,"Abba, na san babu abinda zan gaya maka wanda zai faranta maka rai, amma duk da haka ina mai gurfanar da kai na gare ka a matsayin mai laifi.Ka yanke min duk hukuncin da ya dace dani, wanda zai sanyaya maka rai, har ka huce ka ban Nusaiba, in koma da ita.<br /> Da sunan Allah na ke wannan rokon Abba, ka taimake ni don son Manzon mu.<br /> Yayi shiru. Shi kuwa Alhj sai a aikinsa yake yi.<br /> Kamar ba zai tanka ba, wucewar mintoci, kafin ya ce,"Ka na iya tafiya, zan neme ka."<br /> Ya durk'usa guiwa 2 ya ce,"To shi kenan, na gode Abba.<br /> Kuma ina k'ara neman afuwa akan kuskuran da na yi.<br /> Ka gafarce ni Abba."<br /> Ya ce,"Ka je zan neme ka na ce."<br /> Ya mike yana fadin,"Na gode, a tashi lafiya."<br / > Bai amsa masa ba ya fice.<br /> Alhaji ya sauke numfashi, ya dafe goshinsa, bai san dalilin da yasa son Naseer yayi masa yawa a zuciya ba, duk lokacin da ya gan shi kaunar sa karuwa take.<br /> Dole ce tasa ya yanke hukuncin nan, saboda ya kar6o wa Nusaiba 'yancinta.<br /> Ofishin su Yakubu Naseer ya nufa, can bargar dawakai, amma wurin na kulle babu kowa, sai mai ba dawaki abinci.<br /> Bai tsaya 6ata lkc ba, ya damko hanyar dawowa gida, yana tafe wasi-wasi ne fal cikin ransa, wata zuciyar na saka masa zai yi wuya Nusiba ta dawo, wata kuma na tabbatar masa za ta dawo ne, tunda ya ce zai neme ka.,<br /> Ai kai d'an gaban goshin sa ne. Daya iso shago, ya tsaya wajen Sageer.<br /> Bai dawo gida ba, sai karfe 1,abu na farko sada fara gani, shine babu motar Nusaiba dake lullu6e a wajen.<br /> Gabnsa ya fadi, ya fito da sauri ya fada cikin gida.<br /> Zarah na zaune a barndar sasan su, tana ta faman goge kwalla."Menene wai?<br /> Ban ga motar Nusaiba ba a waje!<br /> Murya na rawa ta ce,"An kwashe kayanta, ka ga shi kenan ta faru, ta k'are, tuntuni na ke gaya maka, ka je ka k'i................<br /> Ya katse ta da masifa,"Don Allah isa haka, kar ki kara 6ata min rai!<br /> Ko yanzu daga ina na ke? Ya ce zai neme ni?