← Book details A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 28

Sashe 18

A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

har ta hakura ta sakar masa. Daga ranar ya daukar wa kan sa alkawarin zama lafiya da kowa, zuwa k'arshen rayuwarsa.<br /> Idan ba shi gida, yana shagon dinki ne, daya samu Abba ya fara amsa gaisuwar sa, kuma bin sa yake sau da kafa.<br /> Komai bai zartarwa sai abinda ya ce. Haka yake bin Alhj, bai ketare umurinin sa. A haka aka share watanin 2. Mamakin sa 1 shine. Alhj ya ki dawo da wasan Polo, shi kuma yana jin nauyin yi masa magana.<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> A 'yan tsakanin ne. Fa'iza ta haihu da namiji k'aton gaske mai kama da Babansa. Ranar suna, ya rada masa Mohammad. Zarah gidan sunan ta wuni duk da ta wayi gari baya jin dadi.<br /> Tun daga ranar jikinta ya k'i yi mata dadi,<br /> tsoro ya fara kamata, sbd fargaba daukan ciki.<br /> Lalurar ta ta fara bata tsoro.<br /> Lalai kuwa, abinda take wa tsoron ne ya samu.<br /> Shi kan sa Naseer tausayi take ba shi, shi yasa wannan karon murnar sa raggiya ce.<br /> Zarah na tsakiyar laulayi, aka biya kudin jarrabawar (External)<br /> Naseer ya biya duka WAEC da NECO.<br /> Daga nan Sageer ya shawarce shi daya fada makarantun bada (Lesson), don ya k'ara wanke masa kwakwalwa.<br /> Babu musu, ya nema ya shiga guda 2, yana zuwa.<br /> Ranar da za'a kai Zarah daurin mahaifa, ranar ce suke da jarabawar farko. Hankalin Naseer ba'a kwance yake ba, babu yadda zai yi.<br /> Haka nan ya hakura suka tafi tare da su.<br /> Umma da Inna Sageer ya kai su a Jeep din sa.<br /> Shi ya tafi jarabawar sa da Civic.A saukake yayi jarabawar sa, duk da ba shi cikin nutsuwa, babu tambayar da ta gagare shi amsawa.<br /> Yana tashi ya wuce asibiti abin sa, ya duba Zaraha, sannan ya dawo shago yayi ayyukansa. Can yake zama su ci su yi hira, zuwa karfe 9 ya dawo gida.<br /> Zaman sa shi kadai yana kara taso masa da kewar Nusaiba, a lkc irin wannan can baya, duk da ta san baya maraba da ita cikin dakin sa, ta kan shigo har ta tambaye shi ko yana da bukatar wani abu.<br /> Shi yasa ya dauki filo ya nufi sashin ta cikin dakin barcinta, ya jefa pilo bisa kafet ya kwanta.<br /> Nan ya kasance wajen barcinsa, kodayaushe, yana laluben inda zai ji motsinta.<br /> Watannin 3 sakamakon jarabawarsa ta fito.<br /> Allah da ikon sa gaba daya sakamakon Naseer masu kyau ne.<br /> Yayi matukar sa'a.<br /> Allah ya kubutar da shi daga sharrin hukumar jarabawa da yanzu abin yake neman zama kasuwanci.<br /> Ko ma ince ya zama din."<br /> Magidanci na fama da kansa, duk da haka ya dage da karma-karma ya biya zunzurutin kudi, sai jarabawa ta fito, ace yaro bai ci ba, alhali da kokarin sa da komai.<br /> Sannan ya dage wajen neman taimakon makarantun (Lesson), tunda daman makarantun gwamnati sai a hankali.<br /> Ba duka (Syllabus) ake (Covering) , ba, balle yaro ya san makamar jarabawarsa.<br /> Allah ya sawwake.<br /> Ilimi ya zama wahala ga 'ya'yanmu talakawa.Shi kam Naseer yayi sa'a kamar yadda Allah ya halicce shi, shi mai sa'a ne a rayuwarsa.<br /> Da rawar jikinsa ya kai wa Alh. Basheer takardun ya gani.<br /> Yayi murna kwarai, daga nan ya shiga neman makaranta, don samun (Admission).<br /> Sageer na taimaka masa.<br /> Ba jimawa ba, ya sami Poly ta hannun Sageer din, Babu kudin kirki a hannunsa a wannan 'yan tsakanin, sbd zaman Zarah a asibiti.<br /> Ya zauna yana tunanin yadda za'ayi.<br /> Ba tare daya takurawa kowa ba.<br /> Abin mamaki yana zuwa Kaduna, ya nuna wa Alhj,("Admission) din, kamar yadda ya umurce shi, cewar da ya samu ya kawo masa ya gani.<br /> Take nan ya ware dubu 50 ya ba shi, ya ce ya je yayi hidimar makaranta.<br /> Allah mai iko.<br /> Tun daga ofid har ya dawo gida, godiya yake wa Alhj cikin ransa.<br /> Ya kawo wa Abbansa, suka sa albarka shi da Umma, balle Zarah da take jin tausayin sa, sbd hidimar da yake sha a asibiti, ga kuma makaranta ta kunno kai.<br /> Lallai Alhj ba karamin taimako yayi ma su ba.<br /> Ciki lafiya, ba ka lafiya, ya kama karatun sa a (Poly Computer Science) yake karantawa, kamar almara yake ganin abin.<br /> Lokacin kuwa cikin Zarah ya shiga wata 7.<br /> Zullumi ya ishi kowa, musamman ita mai dauke da cikin.<br /> Kusan kullun da ciwon mara take kwana.<br /> Bata dai yin magana ne kawai.<br /> Saboda ciwon ba wai ya tsananta ba ne.<br /> Sati 2 da fara karatunsa, abinda ake gudun ya faru.<br /> Ta haifi da namiji.<br /> Aka sanya shi a kwalba kwana 7. Ya ce ga garin ku nan kuma shi ya ci sunan Alhaji, watau Mohammad Basheeeeeeeeeeeeerrr­ rrrr!!!!!.......<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Labarin haihuwar Zarah har Jordan, amma da aka ce ya koma. Jikin Nusaiba yayi sanyi, ta dubi Ameer yana ta rarrafen sa, yayi k'atob gasket, dauki da nishi jajur, ga suma baka wulik! Kamar kan Babansa.<br /> Tausayin Antinta ya kama ta, ta yi tagumi ta ce a ranta,"Allah sarki Antina." Ta numfasa, Ameer ya rarrafo gun ta, ya dafa ta ya mike, ta sa hannun ta dauke shi ta rungume.<br /> Tabbas ta sani dole Naseer ya sa Ameer a ransa.<br /> Ta k'ara matse shi jikin ta, tunanin ta wai ace Naseer ya tada k'ayar baya, dan sa yake so a ba shi. Abinda ba zai samu ba kenan, yadda ta shaku da Ameer.<br /> Ai mai raba ta da shi, sai wanda ya bata shi. Ta yi dai yi masu addu'ar Allah ya ba su mai albarka."<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> BAYAN SHEKARA DAYA<br /> Shekara guda da rushe(DABAI RIBERS),sauran kolub-kolub din wasannin polo sai kawo wa Naseer takardun gayyata suke, suna neman ya koma kungiyoyinsu.<br /> Gayyata har da Ghana, Kamaru, Benin Republic, da sauran kasashen makwafta, wadanda suka san Naseer, suka kuma san irin rawar daya taka a wasan tsern Polo.<br /> Amma sam ya ki amsa kiransu, duk da ya san dumbin alkhairin da zai samu a can. Sam-sam zuciyarsa ta fita daga wasan Polo tunda Alh. Basheer ya bar harkar.Hakan ya gaya wa Yakubu ranar da ya same shi da wata takarda da ta zo ta hannun sa daga Sakkwato. Magana ta kawo magana, suna hira tsakanin Yakubun da Alhj.<br /> Shi kuma yake ba shi labari.<br /> Saboda haka Alh.Basheer ya kira Naseer yayi masa magana. Baya ketare umurinin Alhjn, amma wannan karon Naseer kad'a kai yai ya ce,"Abba karatuna ya fi min wannan wasan, kuma ban jin zan iya wasa da wani (Polo club) a halin yanzu.<br /> Alhj ya bi shi da kallo, tsaf ya kasa ganeme yake nufi.<br /> Yayi dan murmushi ya ce,"Shi kenan tunda ka kawo zancen karatu. Allah ya bada sa'a."Ya ce"Amin. Alh.Basheer ya dade yana nazarin maganganun Naseer kuma yana tausaya masa, domin ya saba da Polo.<br /> Yana sha'awarsa, bugu da k'ari wasan Polo A JININSA YAKE.Abinda kuwa daka saba da shi zai yi wuya ya fice maka a rai, sai dole. Alhjn bai yanke hukunci ba, tukuna, amma yana nan yana nazari a kai.<br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin habakashi....<br /> https://mbasic.facebook.com/HAUSA- Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_ ID10%2C7370123473<br /> Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara gudanar dashi<br /> <br /> ------------------------------------------------------------------------------------------------ <br /> Al'amarin Nusaiba kuwa a birnin Jordan, ba yabo, ba fallasa a yanayin jikinta. Ta kasa samun natsuwa a ranta, saboda yawan zancen aure da Antin Jordan ke yi mata, tunda Ameer yayi wayau sosai, yana gudun sa ko'ina gwanin sha'awa.<br /> Kullum amsar ta ita ce bata da wani bazawari tsayayye ko a Nijeriya, balle kuma a nan Jordan da babu wanda ta sani kasancewar ba fita take yi ba.Idan ba (Shopping) ba tare da yaran gidan da Direba. Ta damu kwarai domin ba ta san dalilin da yasa Antin ta damu da yin sabon aurenna taba. Shekara 1 kacal da mutuwar auranta.<br /> A yammacin yau (Shopping) din za su da yaran gidan.<br /> Kowace ta shirya cikin dogayen kaya kala daban- daban.<br /> Direba ya aje su katuwar (Super market) din da suke saba zuwa.<br /> Suka shige kowa, yayi na sa wuri, yana neman abinda yake so.<br /> Nusaiba na jaye da Ameer cikin kwandon Shopping din ta saka shi, don kar ya rink'a bata wahala, yana gudu, tana kamo shi.<br /> Bata ko lura da mutumin dake tsaye 6angarn kayan abincin yara ba, sai da ta ji yana fad'in,"Ameer!<br /> Haka ka yi girma?<br /> Ta waigo da sauri ta dube shi.<br /> Ibrahim ne ke wasa da habar Ameer.<br /> Bai kalle ta ba, ya ci gaba da cewa,"Ka ba Husna kewa, kullum maganar ka take."<br /> Ameer washe baki yake yana dariya.<br /> Ita kuwa Nusaiba jikinta rawa ya dauka, ta tsura masa ido.<br /> A hankali ya dago, ya dube ta yayi dan murmushi ya ce,"Hajiya Nusaiba."<br /> Ta yi yake, tana fadin a ranta, "Ibrahim ko maye ne?Kafin ta ce ,"Ya ku ke? Ina su Husna da Mamanta? Ya ce,"Lafiya lau suke.<br /> Amma ba ki da kirki? Ta gyara fuska,"Da aka yi me?<br /> Shekara 1 ki na garin nan, ki kasa kawo mana ziyara, ba ki yi alkawari ba.<br /> Sakin ta ce min ta ba ki (Phone Number), amma ba ki kira ba." Lambar ce ta 6ace. Ka gaida
Chapter 18 · 0% Book details