← Book details Zuma A Baki Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 42

Sashe 27

Zuma A Baki Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Zaune yake dagashi se dogon farin wandon yadin kufta system ce a saman cinyarshi yana dannawa sabida wani aiki dayake gudanarwa acikinta.
Idanunshi manne da farin gilashi wanda ya zauna das a fuskar tashi abin sha'awa.
Cikin wani irin yauƙi da gwalli sakina ta ƙarasa gabanshi tare da saka hannu ta janye system ɗin dayake aiki da ita ta, kana ta mayar da jikinta ta zauna a saman cinyarshi hannunta ta ɗora a saman sajenshi taɗanja kaɗan tana wani irin ƙifta idanunta.
"Beby nai missing naka amman shine ka tawomin da yarana babu ko sallamar kirki ko?"
TafaÉ—i maganar cike da salon jan hankali.
Murmushi ya sauke kaɗan domin a iya wannan lokacin yagama karantar cutar mai da yara da takeyi a bayan idanunshi, amman danya ɓatar mata da tunaninta yasa yace mata.
"Dafatan kin dawo lafiya?"
Ya kauda wannan maganar datake soko masa.
"Lafiya kalau na dawo se É—unbin kewar Æ´aÆ´ana"
TafaÉ—a da wata irin siga.
Shikam dariyama ta basa a wannan karon.
"Ƴaƴanki ko? kima daina damuwa dasu fa kin manta uwar data haifesu ma tana can tana rayuwarta babu su bare ke?"
YafaÉ—i maganar da siga biyu.
Jikinta ne yay sanyi a wannan karon tai danasanin jefa mai tambayar ma gaba É—aya.
"Nida ita akwai bam-banci domin ni ina sonka".
TafaÉ—a a zuciye.
"Ita kuma ƙina take? look sakina idan kinsan cin zarafina zakiyi daga zuwanki zaki koma inda kika fito yanzu".
Yafaɗa cikin ɓacin rai matuƙa.
Wanda yasa hatta idanunshi seda ya soma fitar da jar kala.
Numfashi taja a galabaice dajin wannan baƙin furucin nashi.
"Umar mai kake nufi akan waccan marar mutunci kake gayamin waɗan nan maganganun? kalla fuskana akan naje gidansu gaisar da mahaifanta dan kawai mamanta tace ni matarka ce jiba yadda ta miƙe ta zubamin maruka har biyar jere"
TafaÉ—a tana mai nuna mai fuskarta data kuma yin ja abinka da farar fata.
Zaro idanunshi yay waje cike da mamaki.
"Toke waya baki ikon zuwar musu gida da izinin waye?"
Rau rau tai da idanunta.
"Tsautsayine ya kaini ba wani abun ba".
"Yayi miki kyau amman bana tunanin Aisha zata mareki akan kawai dan kince ke matata ce gaskiya domin wannan kalmar bazata saka ta mareki ba? sakina sau tari kina yin abun da nake kallonki dasu kada fa ki manta ina aikine da shashin bincike ne na masu manyan laifuka wallahi! wanda ya fiki rashin gaskiya ma tashi É—aya nake ganoshi bare ke! ke kina cin alfarmar aurena ne amman bada ban haka ba da tuni na watsaki waje, Sabida haka ki taka a hankali kisan da wa kike zaune ba sakarai bane sedai kawaici irin na fulanin usul".
Yakai maganar yana mai tashi yabar mata wajan ya nufi bedroom É—insa zama yayi a gefen gado gaba É—aya abin duniya yay masa zafi.
Ya soma gajiya da halin sakina wanda kawai kallonta yake dasu bawai baya sane bane musamman akan yaransa wallahi kawai yana mata kawaici ne akansu.
Wayarsa dake yashe a bakin gadon ya É—auka ya shiga contact É—insa lambar ogansa ya shiga kira bugu É—aya ya É—auka gaisawa suka shigayi, sannan suka É—ora akan bayanin binciken da aka sakashi ya gudanar akan wani mutum wanda ake zargi daya saci yara guda biyu yayi garkuwa dasu, sosai suka zanta akan maganar yanzu haka an samu nasarar gano inda mutumin yake zaune sabida haka dole ogan nasa yace mai zasu turashi kano sabida akwai waÉ—anda aka gano suna tare da mutumin sedai su suna zaune ne anan kano bayan sun gama maganar sallama sukai sannan ya kashe wayar yana mai dafe kansa dake barazanar tarwatse masa.
Sam bai shirya tunkarar kano a wannan lokacinba, sabida yaransa suna tsaka da karatune shikuma baya son abinda ze nesanta shi da yaranshi musamman a wannan lokacin da sakina take gallaza musu duk da bai nuna mata yasan komi ba, amman abin yana mugun taɓa masa ransa amman ta kusan tuƙeshi takaishi bango domin shi ɗabi'arshi ce kawaici zai taraka in kana masa abu amman da zarar ka kaishi bango tofa komi ma ze iya faruwa.
Tsaki yaja mai ƙarfi sannan ya miƙe tawul ya dauro a west ɗinshi kana ya faɗa toilet ya sakarma kanshi ruwa,ya jima yana cuɗe jikinshi da lallausan soson dake hannunshi,sannan ya kammala wankan nashi ya fito a centern ɗakin ya tsaya ya goge ruwan jikinshi gaban jerin kayansa ya tsaya ya ɗauki yadin kufta ruwan madara mai ɗinkin riga har ƙasa se wando sakawa yay kana ya feshe kansa da turare mai ƙamshi gyara sajen fuskarshi yayi sosai sannan ya ɗauki makullin motarshi ya fita makarantar su islam.
A hanya nuratu ta kirashi tsiya take mai akan rashin zumuncin sa wai ya manta da ita kwana biyu baya nimanta murmushi yayi yana mai bata hakuri akan yanayin aikinsa ne ya kawo hakan.
Koda ya ƙarasa makarantar seda ya jira su aka tashi sannan ya kamo hanya suka yo gida tun a mota daya ce musu mommy ta dawo yaga islam ta haɗe ranta saɓanin ada daya daukosu sunata murnar ganinshi, Amman tunda yace musu mommy ta dawo sukaja bakinsu suka tsuke harya ƙarasa gida basu tanka masa ba, abakin gate ɗinsa ya tsayar da motar tare da bude musu kofar kallon islam yayi gaba ɗaya yarinyar ta kom kamannin mahaifiyarta sak,inka cire farar fatarshi data ɗauko shiyasa tafi aslam kyau nesa ba kusaba sabida ita ta haɗe da kamannin humaira da kuma manyan idanun mahaifinta ne,
"My happiness zanje nai mana take away na dinner kuje gida maza ki kula da ƙaninki kafin na dawo".
Tura baki tai gaba tamkar yadda humaira ke masa inzatai rigima sannan tace mai.
"Mudai daddy kaje damu zamu bika can É—in"
TafaÉ—a tana mai kafesa da manyan idanunta.
murmushi ya sauke mata yana mai lakato kumatunta yana maijin soyayyar ta acikin ransa fiye da komi na rayuwarsa.
"Sorry my love jeki cire uniform ɗinki kicirewa ƙaninki ku zauna a ɗakinku kujirani ina zuwa"
YafaÉ—i maganar cikin tausayin kansa dana yaran nasa.
Babu damar musu haka taja aslam tana ƙunci kamar zata kurma ihu! suka nufi gidan.
Ya jima yana kallonsu don seda suka ƙulewa ganinshi sannan yaja motar ya nufi inda ze amso musu abincin dare.
Yana tafe yana tunanin su aransa tare da fargabar abinda zeje ya dawo akan su.
Cikin sanÉ—a kamar munafukai sukai sallama a falon hannun islam rike dana aslam.
Tana zaune ta haÉ—e kai da gwiwa tana nanata cin zarafin da umar yay mata a É—azun wanda shiya hanata tashi daga wajan bare ma ta kintsa kayan ta datazo dasu.
Cikin rawar jiki suka zube a gabanta.
"Mommy barka da yamma"
Islam ta faÉ—a sabida itace mai baki aslam kam bayada wani wayon kirki bare bakin magana sosai.
Wata uwar harara ta maka musu cike da tsanarsu.
"Dan ubanki inda banyi yammar ba zaki ganni anan wato baku so na dawo gidan ubanku bako? shegiya mai fuska kamar anyi ɓarin kayan miya a injin markaɗe kutashi kubani waje ƴaƴan jaraba" ta saka ƙafa ta haure islam tai baya amman tsabar tsoronta bai bar islam tai kuka ba da sauri taja ƙaninta suka bar falon ɗakinsu suka nufa kuka! yarinyar ta saka a ƙasan tiles tana mai sosa wajan data duketan.
Cikin kuka aslam ya matso gabanta ya saka hannu ya share mata hawayen.
"Yaya ki bar kuka! dan gayawa daddy"
YafaÉ—a da gwaranci sabida baya iya magana sosai.
Cikin son kanin nata ta janyoshi jikinta tana share mai hawayen dayake.
"Aslam É—ina kada ka gayawa dady kaga mommy tace in muka gaya masa zata yanka mu mudaina ganin daddy da inno da maman kano wadda na kwana a wajanta".
TafaÉ—a tana mai tashi tsaye ta wanko fuskarta suka cire kayansu tsuru sukai a É—akin suna jiran ubansu ya dawo domin tsoron fita suke waje.
*********
"Yaya humaira ki tashi ga abin karyawarki inji anty"
Naji muryar anisa kanwata akaina tana min magana.
ÆŠago da jajayen idanuna nai na sauke akanta.
"Anisa kiramin anty ƙafata kamar zata cire wayyo yatsana...........

TOFA!
*GABA ÆŠAYA SADAUKAR WANE GA*

*HAJIYA ZULAIHAT* ( *MRS DR BASHIR*)
*Kainuwa dashan Allah, Rabbi ya ƙara lafiya da wadata mama*🌹

                          *37 & 38*
Chapter 27 · 0% Book details