Sashe 25
Zuma A Baki Part 2 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Ɗora tafikan hannuna biyar a saman fuskarta bata gama dawowa a hayyacinta ba na kuma wanketa da wani bahagon marin, kafin ta sosa na ƙara mata uku a jere masu ɗan karen zafi.
Da azabar ƙunar zuci na dubeta.
"Wallahi sakina sekinyi mamakin yaudara ta da kikai zan nuna miki ni ƴar kano ce cikakka ba zuwau ba kuma sena nuna miki wacece ni! cikin ilimi da nutsuwa irinta ƴaƴa masu tarbiya daga ƙarshe kuma ina mai tabbatar miki da cewa GANGAR JIKIN UMAR KIKA AURA ba zuciyarsa ba domin zuciyar umar ta AISHA HUMAIRA ce da ƴaƴanta har abada sakina bazaki mallaki umar ba matukar ina raye nai gabanki nai miki gudun wuce sa'a a fagen soyayyar umar domin ni sona yake daga zuci har baki haka zalika sone daga Allah ba boka ba malam ba kirsa bare bariki soyayyace ta asali ƴar gaske wadda turawa kewa laƙani da Pure love wadda ba algus cikinta kuma ko yanzu na mutu nagodewa Allah dayasa kika ci arzikin ƴaƴana har kika sami soyayyarsa koda haka seki bawa jakar ƙwaƙwalwarki amsar wacece aisha a zuciyar umar? bazan ji komi dan kinmin haka ba,domin sau tari daman makashinka yana tare dakai sedai kuma ta yaro kyau take bata ƙarko mu zuba"
NafaÉ—a a dake.
Tare da saurin barin wajan zuciyata na suya na nufi gidanmu.
*SAKINA*
Azabure ta dafe fuskarta da dukkan tafukan hannayenta tsananin mamakin humaira ya hanata tafiya bare ta ɗago daga dogon suman wucin gadin azabar zafin marin data afka sosai humaira ta bata mamaki yaushe humaira ta zama jan wuya haka? yaushe humaira ta zama mai dakakkiyar zuciya haka wadda harta ɗaga hannu ta zuba mata maruka biyar lallai ɗan hakin daka raina shike tsone maka idanu, jikinta sanyi ƙalau ta nufi gidansu kai tsaye kicin ta nufa batare data amsa maganar da ummanta ke mata ba, harseda ta sami ruwan ɗumi ta wanke fuskarta dashi abinka da farar fata tuni fuskar ta haye tai suntum dole seda ta haɗiyi maganin zazzaɓi sannan ta wuce ɗaki ta kwanta da shirin tafiya gidan mijinta gobe dakuma tsananin tsanar humaihar mai zafi a zuciyarta.
*Humairah*
Kamar ƴar maye haka nake tangaɗi a hanya harna isa gida kai tsaye ɗakin anty na nufa ina zunduma ihu kamar ƙaramar yarinya, da sassarfa anty da baba wanda ya dawo daga wajan sana'arsa kenan suka fito rumfar suna tambayata a ruɗe.
Ajikin anty na zube ina cigaba da kukana wanda fitarsa ce kaÉ—ai zata sakani jin sanyi acikin zuciyata.
"Ke humairah bani son sakarci, mi aka maki zakizo kina mana kuka kamar wata ƙaramar yarinya bana tunanin ko anisa zatayi wannan shirmen naki".
Naji muryar baba akaina yana faman faÉ—a.
Cikin hakan su umma da baffa suka shigo É—akin a kiÉ—ime sabida suma sunji kukan danike yi ashe.
Itako anti janyoni tai jikinta muka zauna a tsakar É—akin hakan yasa suma su baba suka zauna suna sauraran kukana.
"Anty na shiga ukuna wayyo yaya zanyi?"
NafaÉ—a cikin kuka, kusan a tare baba da baffa sukace.
"Wani abunne ya sami umar da Æ´aÆ´an a hanya?"
Girgiza kaina nai tare da share hawayena kana na dubi anty na soma bata labarin abinda ke faruwa tundaga haÉ—uwa da sakina har kawo yau hatta abubuwan danikewa ya umar seda na faÉ—a ina kuka!
Daga ƙarshe na ɗora da cewa.
"Baba ku yafeni nasan ban kyauta muku ba domin ba irin tarbiyar da kuka bani kenan ba amman sakina tayi amfani da ƙaramin tunanina ta yaudaran harta auren mijina"
NafaÉ—a ina kuka.
Gaba É—aya tausayin tane ya kamasu tabbas wannan wata jarrabata ce tare kuma da ishara Allah ya nuna musu, gaba É—ayansu domin abin da ya sami É—anka ai ya sameka.
"Karki damu humairah kanta taiwa amman kema kinyi sakaci waya gaya miki ana yarda da mutum yanzu ai mutum se Allah".
Cewar ummah wadda take share hawayenta.
Shikuwa baffa tsabar kiÉ—ima ma kasa cewa komi yayi se uban share zufar dayake famanyi.
"Kinga wannan ma ya zama izina gareko? gaba in akace ki sake yin abu babu shawarar mahaifanki kya kumayi sakarar banza uban wama ya haɗaki da ita? wato ni ina nan ina miki tarbiya wata nacan tana rushemin, amman Allah ya sakawa da umar da alkairi yanzu a wannan zamanin wani namijine zeyi abinda umar yayi wani namijin zaki dinga sheƙawa wannan iskancin ya zauna dake? to wannan matsalar da kika shiga haƙƙi biyune ya jefaki cikinta domin kinsan yanzu tun a duniya ake nuna ishara, abu na farko hakkin mijinki da kuma hakkina ni mahaifiyarki danafi kowa kusanci dake amman kika je kika haɗa kai da wata take miki zagon ƙasa, to mu bazama mu nuna wannan maganar ta faruba ki zuba musu idanu Allah ze nuna ikonsa".
Anty ta faɗa tana zubar ƙwallah domin tsananin jin tausayin ɗiyar tata.
Shikuwa babanmu tunda ya sada kansa a ƙasa bai kuma ɗagowa ba har seda su baffa sukai sallama suka wuce nasu ɓarin sannan yaja hucin takaici.
"Yanzu Aisha wannan sakarcin kikai taiwa Umari ashe? ah dole yaron nan ya dauke mana ƙafa, ashe da walakin goro a miya! ikon Allah inda ranka zaka sha kallo wato ita wannan yarinyar ku rabu da ita kanta taima amman kuma wannan ma babban darasi ne wato inzaka shekara kana bawa ɗanka tarbiya daga can zaka sami wanda yake rusa masa, to dama munata shawarar zaki koma karatu nida imirana to matsalar nifa naji tsoro kada ki kuma haɗuwa da wata ƙawar ta kuma jefaki a illah amman da naso ki fara koda fce ce kafin Allah ya kawo miki wani mijin, Allah yay miki albarka aike ba abar jin haushi bace yanzu abar tausayice tabbas alokacin akwai kuruciya da kuma wauta Allah ya saka miki Aisha shikuma umari Allah ya fitar dashi daga sarƙar wannan hatsabiya amin".
Baba ya faÉ—a yana mai kokarin fita daga cikin É—akin.
"Baba".
Nakira sunanshi.
Ya dakata yana kallona da tausaya wa.
BuÉ—e bakina nai kana nace mai........
#AUTAR MANYA
*GABA ÆŠAYA SADAUKAR WANE GA*
*HAJIYA ZULAIHAT* ( *MRS DR BASHIR*)
*Kainuwa dashan Allah, Rabbi ya ƙara lafiya da wadata mama*🌹
             *33 & 34*
Da azabar ƙunar zuci na dubeta.
"Wallahi sakina sekinyi mamakin yaudara ta da kikai zan nuna miki ni ƴar kano ce cikakka ba zuwau ba kuma sena nuna miki wacece ni! cikin ilimi da nutsuwa irinta ƴaƴa masu tarbiya daga ƙarshe kuma ina mai tabbatar miki da cewa GANGAR JIKIN UMAR KIKA AURA ba zuciyarsa ba domin zuciyar umar ta AISHA HUMAIRA ce da ƴaƴanta har abada sakina bazaki mallaki umar ba matukar ina raye nai gabanki nai miki gudun wuce sa'a a fagen soyayyar umar domin ni sona yake daga zuci har baki haka zalika sone daga Allah ba boka ba malam ba kirsa bare bariki soyayyace ta asali ƴar gaske wadda turawa kewa laƙani da Pure love wadda ba algus cikinta kuma ko yanzu na mutu nagodewa Allah dayasa kika ci arzikin ƴaƴana har kika sami soyayyarsa koda haka seki bawa jakar ƙwaƙwalwarki amsar wacece aisha a zuciyar umar? bazan ji komi dan kinmin haka ba,domin sau tari daman makashinka yana tare dakai sedai kuma ta yaro kyau take bata ƙarko mu zuba"
NafaÉ—a a dake.
Tare da saurin barin wajan zuciyata na suya na nufi gidanmu.
*SAKINA*
Azabure ta dafe fuskarta da dukkan tafukan hannayenta tsananin mamakin humaira ya hanata tafiya bare ta ɗago daga dogon suman wucin gadin azabar zafin marin data afka sosai humaira ta bata mamaki yaushe humaira ta zama jan wuya haka? yaushe humaira ta zama mai dakakkiyar zuciya haka wadda harta ɗaga hannu ta zuba mata maruka biyar lallai ɗan hakin daka raina shike tsone maka idanu, jikinta sanyi ƙalau ta nufi gidansu kai tsaye kicin ta nufa batare data amsa maganar da ummanta ke mata ba, harseda ta sami ruwan ɗumi ta wanke fuskarta dashi abinka da farar fata tuni fuskar ta haye tai suntum dole seda ta haɗiyi maganin zazzaɓi sannan ta wuce ɗaki ta kwanta da shirin tafiya gidan mijinta gobe dakuma tsananin tsanar humaihar mai zafi a zuciyarta.
*Humairah*
Kamar ƴar maye haka nake tangaɗi a hanya harna isa gida kai tsaye ɗakin anty na nufa ina zunduma ihu kamar ƙaramar yarinya, da sassarfa anty da baba wanda ya dawo daga wajan sana'arsa kenan suka fito rumfar suna tambayata a ruɗe.
Ajikin anty na zube ina cigaba da kukana wanda fitarsa ce kaÉ—ai zata sakani jin sanyi acikin zuciyata.
"Ke humairah bani son sakarci, mi aka maki zakizo kina mana kuka kamar wata ƙaramar yarinya bana tunanin ko anisa zatayi wannan shirmen naki".
Naji muryar baba akaina yana faman faÉ—a.
Cikin hakan su umma da baffa suka shigo É—akin a kiÉ—ime sabida suma sunji kukan danike yi ashe.
Itako anti janyoni tai jikinta muka zauna a tsakar É—akin hakan yasa suma su baba suka zauna suna sauraran kukana.
"Anty na shiga ukuna wayyo yaya zanyi?"
NafaÉ—a cikin kuka, kusan a tare baba da baffa sukace.
"Wani abunne ya sami umar da Æ´aÆ´an a hanya?"
Girgiza kaina nai tare da share hawayena kana na dubi anty na soma bata labarin abinda ke faruwa tundaga haÉ—uwa da sakina har kawo yau hatta abubuwan danikewa ya umar seda na faÉ—a ina kuka!
Daga ƙarshe na ɗora da cewa.
"Baba ku yafeni nasan ban kyauta muku ba domin ba irin tarbiyar da kuka bani kenan ba amman sakina tayi amfani da ƙaramin tunanina ta yaudaran harta auren mijina"
NafaÉ—a ina kuka.
Gaba É—aya tausayin tane ya kamasu tabbas wannan wata jarrabata ce tare kuma da ishara Allah ya nuna musu, gaba É—ayansu domin abin da ya sami É—anka ai ya sameka.
"Karki damu humairah kanta taiwa amman kema kinyi sakaci waya gaya miki ana yarda da mutum yanzu ai mutum se Allah".
Cewar ummah wadda take share hawayenta.
Shikuwa baffa tsabar kiÉ—ima ma kasa cewa komi yayi se uban share zufar dayake famanyi.
"Kinga wannan ma ya zama izina gareko? gaba in akace ki sake yin abu babu shawarar mahaifanki kya kumayi sakarar banza uban wama ya haɗaki da ita? wato ni ina nan ina miki tarbiya wata nacan tana rushemin, amman Allah ya sakawa da umar da alkairi yanzu a wannan zamanin wani namijine zeyi abinda umar yayi wani namijin zaki dinga sheƙawa wannan iskancin ya zauna dake? to wannan matsalar da kika shiga haƙƙi biyune ya jefaki cikinta domin kinsan yanzu tun a duniya ake nuna ishara, abu na farko hakkin mijinki da kuma hakkina ni mahaifiyarki danafi kowa kusanci dake amman kika je kika haɗa kai da wata take miki zagon ƙasa, to mu bazama mu nuna wannan maganar ta faruba ki zuba musu idanu Allah ze nuna ikonsa".
Anty ta faɗa tana zubar ƙwallah domin tsananin jin tausayin ɗiyar tata.
Shikuwa babanmu tunda ya sada kansa a ƙasa bai kuma ɗagowa ba har seda su baffa sukai sallama suka wuce nasu ɓarin sannan yaja hucin takaici.
"Yanzu Aisha wannan sakarcin kikai taiwa Umari ashe? ah dole yaron nan ya dauke mana ƙafa, ashe da walakin goro a miya! ikon Allah inda ranka zaka sha kallo wato ita wannan yarinyar ku rabu da ita kanta taima amman kuma wannan ma babban darasi ne wato inzaka shekara kana bawa ɗanka tarbiya daga can zaka sami wanda yake rusa masa, to dama munata shawarar zaki koma karatu nida imirana to matsalar nifa naji tsoro kada ki kuma haɗuwa da wata ƙawar ta kuma jefaki a illah amman da naso ki fara koda fce ce kafin Allah ya kawo miki wani mijin, Allah yay miki albarka aike ba abar jin haushi bace yanzu abar tausayice tabbas alokacin akwai kuruciya da kuma wauta Allah ya saka miki Aisha shikuma umari Allah ya fitar dashi daga sarƙar wannan hatsabiya amin".
Baba ya faÉ—a yana mai kokarin fita daga cikin É—akin.
"Baba".
Nakira sunanshi.
Ya dakata yana kallona da tausaya wa.
BuÉ—e bakina nai kana nace mai........
#AUTAR MANYA
*GABA ÆŠAYA SADAUKAR WANE GA*
*HAJIYA ZULAIHAT* ( *MRS DR BASHIR*)
*Kainuwa dashan Allah, Rabbi ya ƙara lafiya da wadata mama*🌹
             *33 & 34*