← Book details Zaman Aure Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 25

Sashe 12

Zaman Aure Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

tafiyarsa yayi ya nufi saman Abbansu,suka gaisa bejima ba ya sakko,dakin mama ya nufa ,nan yasameta zaune a parlonta sai suhaif dake kwance da waya a hannunsa yai sallama ya shiga guri yasamu ya gaisheta taamsa da sakin fuska ,suhaif ne yatasu ya gaida yayan nasa

"Yaya kamal barka da asuba,ya auntyna"

"yauwasuhaif ,lpy kalau,yana ganka a kwance ba shirin school,lpy de ko?

dan karamin tsaki yayi ,sannan yashafi sumar kansa kana ya dora da

"wlh yaya yau sai ahankali, wani banzan abokina ne yabani ciwon kai da safen nan,shiyasa nakasa fita"

dariya suka sa kasancewar suhaif mutum mai barkwanci ,sallama yaimusu yatafi kai tsaye office ya nufa ,

sakna kuwa tun bayan futarsu ta koma ta kwanta kuka tasaki mai tsuma rai tare da shafa cikinta tana kwance sai ji tayi,

*jameel*

~~kai jameel ya dafe,saboda yadda labiba take yawan bashi ciwon kai,ahankali ya jata jikinsa yace

"Everlasting,to mekikeson ci yanzu,wai ma meke damunki"?

shiru tayi tare da lumshe ido,ahamkali takira sunan sa

"jameel,tashi ka kaini asibiti kawai ni kam bansan meke damuna ba"

cikin sauri yadaga ta daki yanufa ya dakko mata mayafi ya yafa mata hannuta ya rike suka karasa gurin motar dakansa ya bude mata ta shiga ya mayar ya rufe,da sauri ya ja motar suka nufi Amir hospital basu wani jimaba suka shiga ganin likitan yana zaune akujera sanye yake da farin glass a fuskar sa,sai rubuce rubucansa yake can yadago yabawa jameel hannu suka gaisa,take yafara duba labiba,tare da yimata tambayoyi ,gwajin farko yagano tana dauke da ciki,na wata biyu,murna gurin jameel baamagana labiba kuwa duf tayi ranta yaimasifar baci ,tashi tayi ta fita binta jameel yayi da ido,take gabansa ya fadi,dan yasan yanacikin wata masifar,sallama yayiwa likitan ya fita tana cikin mota ,nan ya shiga,yasameta,shiru yayimata can yadago ya dubeta suka hada ido,harara tasakar masa take ya dauke idonsa ahaka yaja motar suka bar harabar asibitin cikin bacin rai tace

"ka kaini gidanmmu kawai"

"Angama madam,amma ....

"Dan Allah kaimin shiru jameel,kabarni inji da damuwar da kabani "

shiru yayi,har suka karasa gidan su ,ya sauketa , shiru yayi can ta dago ta dubeshi tace

"kawuce gida ,sai zuwa dare kazo ka daukeni"

"To,madam,amma ina neman alfarma daya"

"kaadana ta inmun koma gida naji,baka da abinda zaka ce dani yanzu

fita tayi ta nufi ciki,yadade yana kallon kofar gidan nasu sannan yaja motar kai tsaye office ya nufa yana zuwa sukai kacibus da manajan wani kallo yabishi dashi ya gyada kansa dakatar da shi yayi anan gurin batare da yabarshi ya nufi office din nasa ba,

*Abdulmalik*

~~Inna na tsaye a kofar dakin Ruhaima Abdulmalik yai sallama ya shigo da ledoji a hannunsa yozali yayi da inna a kofar dakin su,da sauri ya nufota,yace

"inna sannu,da gida dafatan de lpy?

cikin kwabe fuska tace

"To,lafiyar kenan,ni da matar ka ne,yanzu ni banisa infada mata gsky ba,sai ta tsiri yimin rashin kunya,ko ba uwar mijin ta ba ce ni ,ai a haife na haifeta,ko ma ince na haifi uwarta ko,amma ba komai nagode "

shiru yayi sai kuma yace

"inna,dan Allah kiyi hakuri inshaallahu zanmata magana,banga matar da zan aura ba ta wulakanta min uwa ba"

leda daya ya mika mata da sauri tasa hannu ta karba ,ta nufi dakinta ,ciki ya nufa tana zaune,tahada kai da gwiwa tanata aikin kuka wayar ta a hannunta da dukkan alamu kira take,da sauri ya karasa gabanta wayar hannunta yafara karba yanadubawa yaga sunan ummata dubanta yayi ransa a mutukar bace yace

"Haba my dear ,yanzu akan abinda betaka kara ya karya ba zaki kira umma kifadamata ,dan Allah kiyi hakuri inshaallahu komai zaizama normal"

"malik,nagaji,inna batasona nagaji kabarni intafi ka auro wacce inna zata so,ko kaima ka zauna lpy"

katseta yayi tahanyar dora danyatsansa a lebanta zaiyi magana kenan sai jin muryar inna yayi tana kwalla masa kira shiru sukayi sai can kuma ya ,

*Hafeez*

Areefa tana shiga gidan ta mayar da jakar ta da takalmanta daki kamar bata fita ba kudinta tafito dasu tana kirgawa 50k murmushi tasaki komawa tayi tai kwanciyar ta a kujera take bacci barawo yai gaba da ita,

Hafeez kuwa da sauri yabi bayan fauza yana kwallamata kira banza taimasa ahaka yasha gabanta yafara bata hakuri dakatar da shi tayi tace

"Hmmm,haba,
Hafeez,yaushe akai daran bare gari ya waye?

"ban fahimci inda kalamanki suka sa gaba ba ,my queen"

"eh zakaiya cewa haka tunda badaga jinsin hausawa ka fito ba"

tanagama fadar haka taitafiyarta wani mai mota ta tsayar kawai tashiga ,bashi da wani zabi banda yashiga tasa motar ya nufi gidansa ,cikin kankanin lokaci yakarasa gidan yanashiga yai tozali da Areefa,tana kwance a kujera kan table kuwa kudi yagani tsayawa yayi yazuba musu ido can kuma yadada karasawa yasa hannu ya,

*NASEEBA GAWO*✍🏻
[3/19, 10:30] ‪+234 814 620 5819‬: [5:59Am,2017]

*@💦💦NASEEBA GAWO*💦💦💦💦

*💦N I G*💦

*ZAMAN AURE*
💦🤦🏻‍♂🤦🏻‍♀💦

*NA*

NASEEBA I UBA💐

*ya hayyu ya kayyumu birahamatika astagisu aslihili shaani kullahu la ila hailla anta*👏🏻

💦
*Nasadaukar ga wannan shafin ga SHAMSUDEEN YUSIF UBA GAWO ya Allah kajikan sa kai masa rahama kabamu hakurin rashinsa dan Allah duk wanda yai tozali da wannan page din ya taimaka mana da addua*😭👏🏻

*20*

~~~Bugun kofar da ake yi ne yadakatar da sakna daga kukan da take ,tashi tayi da kyar ta nufi toilet ta wanke fuskar ta ,ta fito parlor tadanyi shiru nan aka cigaba da bugun da ake,da muryar ta mai sannyi ta tambayi waye ,shiru akai hannu tasa ta bude kofar tana budewa ta yi tozalli da kanwar ta Fiddausi murmushi ta sakar mata tare da rungume juna ,nan suka sami guri sukka zauna,cikin kulawa fiddausi ta dubi yayar tata tace

"Yaya sakna,meke damunki ,kinganki kuwa?"

murmushi tayi tare da shafar cikinta kana ta dora fuskar ta akan ta yar uwar tata tace,

"Ai de kya bari mugaisa ko?da farko ya su umma da malam ina usman?

"Duk suna lpy,to meyasameki dan Allah?

"Fiddausi kenan,bani da lpy ba ina kwance ,amma nasami sauki"

"Ayya sannu,kuma ko kiyi waya kifada ,kekam zurfin cikin ki ya isa"

Nan de suka yini ita taimata komai dangane da aikin gida ko dawasa sakna bata fadawa fiddausi abinda ke faruwa da ita ba dangane da *zaman auransu* da kamal,da yamma ta shirya ta tafi,tun bayan tafiyar ta ta dau kuraani tashiga karantawa nan tadada samun nutsuwa,

kamal bedawo ba sai misalin12,na dare kamar kullum abige ya shigo tana parlor bacci ya dan debeta sai jin gigitacan,

*jameel*

jameel na tsaye a gurin ,manajan ya fito,dawata farar takarda a hannunsa,mika masa yayi ,hannunsa na rawa ya karba yana dubawa yaga,takardar sallama ce daga aiki hankalinsa ne yai masifar tashi,hakuri yashiga bashi ko sauraran sa beyiba,yai tafiyarsa,bashi da zabi,haka ya fita jikinsa asabule ya shiga mota ya nufi gurin hajiyarsa

labiba,kam tana shiga gida tasami mahaifiyar ta a parlor ,jikinta ta fada tasaki kuka nan hankalin uwar ya tashi,tashiga tambayarta ,

"ke labiba,lafiyar ki ,meyadameki ,da har zai saki kuka haka,kinsanni sarai banyarda yata tayi kuka a gidan miji ba,meyayi miki jameel din"?

dagowa tayi ta kalli mahaifiyar tata tace

"momy daga asibiti muke,wai ciki ne dani,ni wlh banaso ,zubarwa zanyi"

ido momy tazaro waje cikin kwantar da murya ta ce

"Bazaa zubar ba,labiba,ai wata damacce tasamu ,kinsan dalili?

kai ta girgiza alamar aa,

*Abdulmalik*

Tashi yayi ya fita,a bakin kofa ya hadu da inna dariya tayi ,sannan tadora da

"yauwa yaron kirki taho muje kaci abinci kaji"

shiru yayi shi yarasa yazaiyi da inna ,ba yadda zaiyi binta yayi zuwa dakin nata ta zuba masa abincin yafara ci amma hankalinsa yana gurin matar sa,hira tashiga yimasa tun yana fahimta har ya gaza fahimtar ta ,kiran sallar ishaai ne yabashi damar fita ,kai tsaye dakin Ruhaima ya nufa tana zaune akan sallaya agabanta ya tsuguna tare da cire hijjab din jikinta ,ahankali ya jata jikinsa tare da zuge zip din rigarta hannunta tasa tarike nasa hannun ta zubawa fuskar sa ido,cikin kasalalliyar murya yace,

"my dear ya zaki dakatar da hannaye na daga taba abinda yake mallakin ki,why?

shiru tayi ,sai hawaye kamar anbude fanfo,ahankali ta dago da idanunta ta dube shi tace,

"Malik,kayi hakuri,da furucin da bakina zaiyi baason raina zanyi ba,sai dan bani da wani zabi ,agaskiya ina mai bakin cikin sanar da kunnuwanka ,

sai kuma tayi shiru tada sakin kuka mai tsuma rai,shikuwa hankalinsa ne yadada tashi,cikin shashshekar kuka ta cigaba da fadin,

*Hafeez*

Areefa,tana ta bacci Hafeez ya dauke kudin da ta samo a gurin Alhj Namadi,daki yanufa dasu ya bude side bed yazuba wanka yadhiga yayi ,ya dawo parlorn yasami guri ya zauna ya zaro wayarsa ya fara chart da yanmatansa can,Areefa ta bude idonta tozali tayi da shi yana karkada fkafa,mai da dubanta tayi ga,kudin ta ,sai gani tayi babu su,da sauri ta dubeshi ta gefan ido yake kallonta,tasowa tayi ta tsaya a gabansa tace

"Hafeez,kamar da kudi a kan center table dinnan ko?

"kina tambaya ta ne,ko me? to,intambaya kike,ni bangansuba"

wani banzan kallo ta watsa masa,kana tadora da ,

"Hmm,baka gansuba,to ai bangansu ba,wata kalma ce da makafi suke amfani da ita,ke kuwa,iya sani na da kai baka jerin makafi "

cikin daga murya da tsawa ya dakatar da ita ,

"Areefa ni kike kalla kike fadawa haka,saboda kin raina ni ,ko me"

wayarta ce ta hau ruri atare suka nufi inda wayar take tare da rigen dauka,

*NASEEBA GAWO*✍🏻
[3/19, 10:30] ‪+234 814 620 5819‬: [8:45PM,2017]

*@💦💦NASEEBA GAWO*💦💦💦

*💦N I G*💦

*ZAMAN AURE*
💦🤦🏻‍♀🤦🏻‍♂💦

*NA*

NASEEBA I UBA💐

*Astagafirilla waatubu ilehe,Allahumma afini fi badani Allahymma afini fi sami,Allahumma afini fi basari,Allahumna afini fi sam,i*👏🏻

*Dedicated 2 my friend, Rukayya Ashir imam thanx 4 ur support Naseeba said we are 2gether*🤝🤝

*21*

~~Cikin tsananin firgici sakna ta mike saboda bugun daakewa kofar parlorn nasu,da sauri ta karasa bakin kofar ta shiga tambayar waye?

murya a dakile kamal ya ce,

"Yaazancin ,waye,wace irin tambaya kenan?,malama bude min kofa"
Chapter 12 · 0% Book details