Sashe 10
So Da Alkawari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Idanunta ne suka soma juyawa wani irin Mugun jiri ya kwasheta.
Baba dake fitowa daga cikin gida ne yaci karo da Jiddan kwance kamar marar rai cikin tsumar Jiki Baba ya koma gida ya shiga Kiran Innah yadda Baba ke Kiran innah ne ya jawo hankalin su Khadija duk suka Biyo Baba wanda yake Cewa Innah.
"Hafsatu zo ki gani tawo da ruwa Yarinyar mutane mai ya sameta"
Innah har zaninta na kuncewa garin sauri haka take bin bayan Baba itama yadda taga Jidda abin ya bata tsoro haka Ummi ta Ebo ruwa a kofi Innah ta shiga zubawa Jidda a jiki da shafa mata a fuska amman ko gezau da Ummi da khadija ne suka kama Jidda kamar gawa suka shiga gida da ita bisa umarnin Baba a rumfar Innah aka shinfiɗe ta, a tabarma Baba ya ce da Innah ta cigaba da shafa mata ruwa In bata farfaɗo ba su tafi asibiti Kusan Minti Goma innah na shafa wa Jiddah Ruwa a fuska tana hura mata Iska gaba ɗaya duk sun firgita dan Khadija ma kuka take yi sosai, Sabida Jiddah Aminiyarta ce.
Sai can taja wani ƙaƙƙarfan Numfashi kafin ta tashi a firgice ta Rungume Innah se kuka mai ƙarfi ya tawo mata cikin kukan take cewa.
"Innah don Allah karki bari kawu Saadik! ya auri wata ba ni ba, Innah wai aure zakuyi mashi da wata?"
Baba ya kalli su Ummi waÉ—an da suka yi saurin ta shi suka bar wajan.
Rumfar tayi shuru babu abin da yake ta shi acikin ta sai sautin Kukan Jiddah.
DaÉ—a rungumeta Innah tayi gaba É—aya abin duniya ya taru yayi mata yawa ga tausayin Jiddah na ratsa mata zuciyarta.
"Hafsatu sake ta dawo nan Hauwa'u zo kusa dani ki zauna muyi magana"
Baba ya faɗa a hankali shima jikinsa yayi sanyi matiƙa duk yadda yake zaton lamarin ya wuce Zaton sa.
Innah ta saki Jiddah wadda take ta faman share hawayenta Gaba daya wannan kunyar da take wa Iyayen Saadik ta kau idanunta ya rufe bata hango komi sai tina abin da kunnuwanta suka ji.
Baba ya kalleta Yana ƙara jin ƙimarta da girmanta a zuciyarshi duk wannan suman da kukan akan son ɗansu ne take yi lallai wannan yarinya ta cancanci komai na kyautatawa a wajan su.
"Hauwa'u ki nutsu kar shaiɗan ya saka ki ji wani abu acikin zuciyarki, Aure dai nufi ne na Allah shima kanshi sadauki! bai san da wannan aure ba, sabida magana ce ta ALƘAWARI! Wanda muka ɗaura nida ɗan uwana ga Hafsatu shaida ce abin da nake so dake shine ki kwantar da hankalin ki, wannan kukan ki daina auren ki da Sadauki babu fashi yadda yayi mana biyayya ya karɓi auren nan kema ba zamu hana ya aureki ba da zarar kin kammala karatun ki"
Har baba ya kammala maganganun shi Jiddah bata ce komi ba sai hawayen da take sharewa nasiha sosai Baba yayi mata kafin ya kira Khadija yace ta rakata Gidansu.
Bayan fitarsu Jiddah Innah ta kalli Baba ranta a jagule tace.
"Gaskiya Babansu ya kamata a duba yaran nan shi kanshi Sadauki ba auren yake soba dan Allah karku cutar da su"
Ya É—aga mata hannu tare da cewa.
"Don Allah Hafsatu kibi yadda nake so bana son ƙananun maganganu Sadauki fa Namiji ne yana da damar auren mace har huɗu sabida haka muyi wa lamarin fatan alheri"
Ba don ran Innah yaso ba sai don tsananin Biyayyar Mijin nata yasa taja baki tai shuru Baba ya saka takalman shi yabar gidan Itama fita tayi wajan daka daddawarta bayan ta gama daka wa ta É—ora sanwar tuwon dare.
Sai dai ƙasan ranta damuwa ce fal.
Nana tana zaune a tabarma tana tankaÉ—e, Innah ta dube ta.
"Nana É—auko min wayata ki kiramin Babar su Hassan"
Da yake bata kiran sunan Aunty Aminah Babbar Ƴarta sai dai tace mata Babarsu Hassan, ko wannan yarinyar.
Nana ta ɗauko wayar ta kirata mata Aunty Aminar ta miƙa mata.
Wayar tana Ringing! Innah ta kwaÉ—awa Ummi kira wadda take É—aki tace mata taje wajan tukunyar tuwo taga in ruwan ya tafasa tayi ruÉ—e.
Aunty Amina ta É—auki wayar tana sallama.
Inna ta amsa a nutse.
"Innarmu barka da yammaci yanzun nan fa maganarki muke da Saadik bai jima da shigowa ba"
Inna tai murmushi tana cewa.
"Au dama gidan ki ya tawo to ki faÉ—a masa ga Jidda can tana suma"
Aunty Amina ta hau salati tana cewa.
"Subhanallahi Innah Jiddan Saadik É—in to garin yaya haka ta faru?"
Cikin damuwa Innah take faÉ—awa Aunty Amina abin da yake faruwa
Shuru Aunty Amina tayi tana sauraron Mahaifiyar tasu har ta gama maganganun nata, dama kuma hirar da suke da Saadik kenan daya zo mata da maganar don duk basu sani ba.
Nisawa Aunty Aminah tayi tare da cewa.
"Innah karki tashi hankalin ki Addu'ar dai da ake ita za a cigaba Yanzun nan Kawu Saadik yake faɗa min ashe aura masa Rabi'atu za ai to mudai bamu da ja don aure nufin Allah ne kuma muna fatan Allah yasa albarka a lamarin, ita kuma jidda haƙuri zatai tinda dai aure halal ne ba haramun ba"
Innah ta sauke ajiyar zuciya tana cewa.
"Hakane yarinyar ta bani tausayi ne shiyasa naji duk hankalina ya tashi da lamarin to bari na barku ku tattauna É—in amman kice mai ya tawo gida da wuri dan ban ganewa Hauwa'u ba"
Dariya Aunty Aminah tayi tana cewa.
"Wato abin cikin ƙwan yafi ƙwan daɗi innah kada fa Rabi'ah tazo ai mana ƴan ubanci"
Itama innar dariya tayi tana katse wayar.
Saadik ya shiga murza goshin sa cikin damuwa yace wa Aunty Aminah.
"Kinga sakarcin ko don Allah menene abin suma daga maganar aure nifa bana son damuwa Allah in batai wasa ba sai na fasa auren nata ma gaba É—aya duk wannan damuwar don wa nakeyi in ba domin taba, ba zata tayani kwantar da hankalina ba sai É—agamin"
Aunty Amina dariya ta saki tana kiran Hussaina Æ´arta.
"Hussaina kawo wa kawu saadik ruwa mai sanyi dan naga sai gumi yake"
"Haba Yaya dole nai zufa nama rasa inda zan saka kaina ne"
Hussaina ta kawo masa ruwan a plate É—in roba ya É—auki guda ya shanye Ganin ya sami Nutsuwa Aunty Amina ta fara masa magana.
"Kabi komai cikin nutsuwa mu dama mata an sammu da kishi sai dai kowacce kalar nata daban Dan Allah kada kaiwa Jiddah magana marar daɗi kayi mata uziri ka rarrasheta, sannan batun lefen da kake min shima ba ka da matsala Abban su yana kawo min kayayyaki daga kasuwa ina siyarwa ina ɗora nawa, sabida haka zan daukar maka duk abin da kake so in yaso a hankali ni sai mu ƙarƙare"
Zuba mata ido yayi harta ƙare maganar.
"Yaya niko wani irin rashin imani zai saka na amshe kayanki na saidawa nakai lefe"
Yayi É—an shuru sannan ya cigaba.
"Yanzu dai ki bani account number ɗinki na saka abin da ya samu zuwa jibi in sha Allah zan ƙara sai ku sissiyo ko keda Yaya Hajjo ne"
Ta kalle shi.
"In banda abin ka ba daɗin nakan kenan ba, karka takura kanka akwai kuɗi a wajena kasan Bikin Hussaina yana ta ƙaratowa to na ɗau dashin dazan ƙarasa siyayyar kayan kitchen in baka son na ɗauki kayan Abban nasu saina baka kuɗin daga baya ko yaushe ka samu sai ka biyani"
Murmushi yayi.
"Kai Yaya nifa bashin ne bana so"
Ta kalle shi.
"Auta na baka kyauta tunda baka son bashi"
Da sauri yace.
"Wallahi ba zan amshi kuÉ—in kuba kowa yana fama da kanshi da É—anshi akan me"
"Saadik kenan ni na rasa irin zuciyarka Ubangiji ya sa kafi haka duk hidimar da kake mana kace kai taka tazo ba zamu taimaka maka ba, Bani manta Bikin jawahir kaifa kai mana kayan kitchen sannan Abbansu kasuwar bata garawa don Allah ka amshi kuÉ—in nan Saadik nasan rayuwar ana fama amman Allah zai warware"
Cikin son kauda maganar yace.
"Ki bani account ɗin sauri nake yi in yaso sai ki ma Yaya Hajjo waya ku tattauna nidai bana son ƙananun atamfofi gwara ko ba yawa a sayi masu aminci"
Duk yadda taso su sasanta ya amshi bashin kayan kona kuɗin yaƙi Sabida acewarsa kowa yana fama da kanshi ba zaka ɗora mai wahala ba.
Ya amshi Account Number ɗin nata ya saka mata Kuɗin da suka rage mai yayi mata sallama ya tafi gida duk da taso ya tsaya yaci abinci tinda an kusa gamawa amman fafur yaƙi tsayawa.
A bakin titi ya sauka ya shiga shagon mai fura da nono ya siyawa innah sanin tana son surki sannan ya saiwa Zarah alewa ya nufi lungun su.
Bai iya ɗakin shi dake soro ba sai da ya ƙarasa cikin gida ya sami su innah suna ƙoƙarin ɗaura alwalar sallar magariba da ake ƙoƙarin kira.
Ya miƙawa zarah alewarta wadda tazo ta ɗane shi yana kallon innah wadda ta zabga mai harara.
"Wai innah nikam mai nayi daga zuwana ga furarki na sayo"
Sai da ta É—aura alwalarta sannan tace.
"Ka kyauta ka bar Æ´ar mutane cikin wani hali kai tafiyarka"
Ya wani zaro ido waje.
"Inna itan ce tace nai mata wani abun nifa kawai biyoni tayi da kuka shiyasa na bar mata wurin"
"Oho ca nake kasan sanda ta faɗin, yanzu kayi sallah sai ka leƙa gidan nasu kaji yadda take nima danai sallar zan shiga"
Ya miƙa mata ledar furar tare da amsa mata da cewa.
"To"
Yana juyawa ya nufi ɗakin shi da fitilar ƙaramar wayarshi yayi amfani wajan haska banɗaki yayi uzirin gabanshi tare da ɗaura alwala, ya fita masallaci.
Bayan ya idar da sallar magariba, ya dawo É—aki yayi wanka Nura saiti ya kira a waya yana tambayar shi akan koya dawo Nurah yace mishi yana bakin titi yanzu zai shigo lungun da sauri yace masa inya shigo É—in ya biyo don Allah zai rakashi Gidansu Jiddah.
Zama yayi yana jiran Nuran bayan ya katse wayar jim kaÉ—an nurah ya shigo tashi kawai yayi suka fita.
A ƙofar gidan su Jiddah suka dakata yana tunanin ta yadda zai sami yaron da zai musu iso zuwa gidan dan shi yana jin nauyin kiran Umma a waya yace yazo.
Baba dake fitowa daga cikin gida ne yaci karo da Jiddan kwance kamar marar rai cikin tsumar Jiki Baba ya koma gida ya shiga Kiran Innah yadda Baba ke Kiran innah ne ya jawo hankalin su Khadija duk suka Biyo Baba wanda yake Cewa Innah.
"Hafsatu zo ki gani tawo da ruwa Yarinyar mutane mai ya sameta"
Innah har zaninta na kuncewa garin sauri haka take bin bayan Baba itama yadda taga Jidda abin ya bata tsoro haka Ummi ta Ebo ruwa a kofi Innah ta shiga zubawa Jidda a jiki da shafa mata a fuska amman ko gezau da Ummi da khadija ne suka kama Jidda kamar gawa suka shiga gida da ita bisa umarnin Baba a rumfar Innah aka shinfiɗe ta, a tabarma Baba ya ce da Innah ta cigaba da shafa mata ruwa In bata farfaɗo ba su tafi asibiti Kusan Minti Goma innah na shafa wa Jiddah Ruwa a fuska tana hura mata Iska gaba ɗaya duk sun firgita dan Khadija ma kuka take yi sosai, Sabida Jiddah Aminiyarta ce.
Sai can taja wani ƙaƙƙarfan Numfashi kafin ta tashi a firgice ta Rungume Innah se kuka mai ƙarfi ya tawo mata cikin kukan take cewa.
"Innah don Allah karki bari kawu Saadik! ya auri wata ba ni ba, Innah wai aure zakuyi mashi da wata?"
Baba ya kalli su Ummi waÉ—an da suka yi saurin ta shi suka bar wajan.
Rumfar tayi shuru babu abin da yake ta shi acikin ta sai sautin Kukan Jiddah.
DaÉ—a rungumeta Innah tayi gaba É—aya abin duniya ya taru yayi mata yawa ga tausayin Jiddah na ratsa mata zuciyarta.
"Hafsatu sake ta dawo nan Hauwa'u zo kusa dani ki zauna muyi magana"
Baba ya faɗa a hankali shima jikinsa yayi sanyi matiƙa duk yadda yake zaton lamarin ya wuce Zaton sa.
Innah ta saki Jiddah wadda take ta faman share hawayenta Gaba daya wannan kunyar da take wa Iyayen Saadik ta kau idanunta ya rufe bata hango komi sai tina abin da kunnuwanta suka ji.
Baba ya kalleta Yana ƙara jin ƙimarta da girmanta a zuciyarshi duk wannan suman da kukan akan son ɗansu ne take yi lallai wannan yarinya ta cancanci komai na kyautatawa a wajan su.
"Hauwa'u ki nutsu kar shaiɗan ya saka ki ji wani abu acikin zuciyarki, Aure dai nufi ne na Allah shima kanshi sadauki! bai san da wannan aure ba, sabida magana ce ta ALƘAWARI! Wanda muka ɗaura nida ɗan uwana ga Hafsatu shaida ce abin da nake so dake shine ki kwantar da hankalin ki, wannan kukan ki daina auren ki da Sadauki babu fashi yadda yayi mana biyayya ya karɓi auren nan kema ba zamu hana ya aureki ba da zarar kin kammala karatun ki"
Har baba ya kammala maganganun shi Jiddah bata ce komi ba sai hawayen da take sharewa nasiha sosai Baba yayi mata kafin ya kira Khadija yace ta rakata Gidansu.
Bayan fitarsu Jiddah Innah ta kalli Baba ranta a jagule tace.
"Gaskiya Babansu ya kamata a duba yaran nan shi kanshi Sadauki ba auren yake soba dan Allah karku cutar da su"
Ya É—aga mata hannu tare da cewa.
"Don Allah Hafsatu kibi yadda nake so bana son ƙananun maganganu Sadauki fa Namiji ne yana da damar auren mace har huɗu sabida haka muyi wa lamarin fatan alheri"
Ba don ran Innah yaso ba sai don tsananin Biyayyar Mijin nata yasa taja baki tai shuru Baba ya saka takalman shi yabar gidan Itama fita tayi wajan daka daddawarta bayan ta gama daka wa ta É—ora sanwar tuwon dare.
Sai dai ƙasan ranta damuwa ce fal.
Nana tana zaune a tabarma tana tankaÉ—e, Innah ta dube ta.
"Nana É—auko min wayata ki kiramin Babar su Hassan"
Da yake bata kiran sunan Aunty Aminah Babbar Ƴarta sai dai tace mata Babarsu Hassan, ko wannan yarinyar.
Nana ta ɗauko wayar ta kirata mata Aunty Aminar ta miƙa mata.
Wayar tana Ringing! Innah ta kwaÉ—awa Ummi kira wadda take É—aki tace mata taje wajan tukunyar tuwo taga in ruwan ya tafasa tayi ruÉ—e.
Aunty Amina ta É—auki wayar tana sallama.
Inna ta amsa a nutse.
"Innarmu barka da yammaci yanzun nan fa maganarki muke da Saadik bai jima da shigowa ba"
Inna tai murmushi tana cewa.
"Au dama gidan ki ya tawo to ki faÉ—a masa ga Jidda can tana suma"
Aunty Amina ta hau salati tana cewa.
"Subhanallahi Innah Jiddan Saadik É—in to garin yaya haka ta faru?"
Cikin damuwa Innah take faÉ—awa Aunty Amina abin da yake faruwa
Shuru Aunty Amina tayi tana sauraron Mahaifiyar tasu har ta gama maganganun nata, dama kuma hirar da suke da Saadik kenan daya zo mata da maganar don duk basu sani ba.
Nisawa Aunty Aminah tayi tare da cewa.
"Innah karki tashi hankalin ki Addu'ar dai da ake ita za a cigaba Yanzun nan Kawu Saadik yake faɗa min ashe aura masa Rabi'atu za ai to mudai bamu da ja don aure nufin Allah ne kuma muna fatan Allah yasa albarka a lamarin, ita kuma jidda haƙuri zatai tinda dai aure halal ne ba haramun ba"
Innah ta sauke ajiyar zuciya tana cewa.
"Hakane yarinyar ta bani tausayi ne shiyasa naji duk hankalina ya tashi da lamarin to bari na barku ku tattauna É—in amman kice mai ya tawo gida da wuri dan ban ganewa Hauwa'u ba"
Dariya Aunty Aminah tayi tana cewa.
"Wato abin cikin ƙwan yafi ƙwan daɗi innah kada fa Rabi'ah tazo ai mana ƴan ubanci"
Itama innar dariya tayi tana katse wayar.
Saadik ya shiga murza goshin sa cikin damuwa yace wa Aunty Aminah.
"Kinga sakarcin ko don Allah menene abin suma daga maganar aure nifa bana son damuwa Allah in batai wasa ba sai na fasa auren nata ma gaba É—aya duk wannan damuwar don wa nakeyi in ba domin taba, ba zata tayani kwantar da hankalina ba sai É—agamin"
Aunty Amina dariya ta saki tana kiran Hussaina Æ´arta.
"Hussaina kawo wa kawu saadik ruwa mai sanyi dan naga sai gumi yake"
"Haba Yaya dole nai zufa nama rasa inda zan saka kaina ne"
Hussaina ta kawo masa ruwan a plate É—in roba ya É—auki guda ya shanye Ganin ya sami Nutsuwa Aunty Amina ta fara masa magana.
"Kabi komai cikin nutsuwa mu dama mata an sammu da kishi sai dai kowacce kalar nata daban Dan Allah kada kaiwa Jiddah magana marar daɗi kayi mata uziri ka rarrasheta, sannan batun lefen da kake min shima ba ka da matsala Abban su yana kawo min kayayyaki daga kasuwa ina siyarwa ina ɗora nawa, sabida haka zan daukar maka duk abin da kake so in yaso a hankali ni sai mu ƙarƙare"
Zuba mata ido yayi harta ƙare maganar.
"Yaya niko wani irin rashin imani zai saka na amshe kayanki na saidawa nakai lefe"
Yayi É—an shuru sannan ya cigaba.
"Yanzu dai ki bani account number ɗinki na saka abin da ya samu zuwa jibi in sha Allah zan ƙara sai ku sissiyo ko keda Yaya Hajjo ne"
Ta kalle shi.
"In banda abin ka ba daɗin nakan kenan ba, karka takura kanka akwai kuɗi a wajena kasan Bikin Hussaina yana ta ƙaratowa to na ɗau dashin dazan ƙarasa siyayyar kayan kitchen in baka son na ɗauki kayan Abban nasu saina baka kuɗin daga baya ko yaushe ka samu sai ka biyani"
Murmushi yayi.
"Kai Yaya nifa bashin ne bana so"
Ta kalle shi.
"Auta na baka kyauta tunda baka son bashi"
Da sauri yace.
"Wallahi ba zan amshi kuÉ—in kuba kowa yana fama da kanshi da É—anshi akan me"
"Saadik kenan ni na rasa irin zuciyarka Ubangiji ya sa kafi haka duk hidimar da kake mana kace kai taka tazo ba zamu taimaka maka ba, Bani manta Bikin jawahir kaifa kai mana kayan kitchen sannan Abbansu kasuwar bata garawa don Allah ka amshi kuÉ—in nan Saadik nasan rayuwar ana fama amman Allah zai warware"
Cikin son kauda maganar yace.
"Ki bani account ɗin sauri nake yi in yaso sai ki ma Yaya Hajjo waya ku tattauna nidai bana son ƙananun atamfofi gwara ko ba yawa a sayi masu aminci"
Duk yadda taso su sasanta ya amshi bashin kayan kona kuɗin yaƙi Sabida acewarsa kowa yana fama da kanshi ba zaka ɗora mai wahala ba.
Ya amshi Account Number ɗin nata ya saka mata Kuɗin da suka rage mai yayi mata sallama ya tafi gida duk da taso ya tsaya yaci abinci tinda an kusa gamawa amman fafur yaƙi tsayawa.
A bakin titi ya sauka ya shiga shagon mai fura da nono ya siyawa innah sanin tana son surki sannan ya saiwa Zarah alewa ya nufi lungun su.
Bai iya ɗakin shi dake soro ba sai da ya ƙarasa cikin gida ya sami su innah suna ƙoƙarin ɗaura alwalar sallar magariba da ake ƙoƙarin kira.
Ya miƙawa zarah alewarta wadda tazo ta ɗane shi yana kallon innah wadda ta zabga mai harara.
"Wai innah nikam mai nayi daga zuwana ga furarki na sayo"
Sai da ta É—aura alwalarta sannan tace.
"Ka kyauta ka bar Æ´ar mutane cikin wani hali kai tafiyarka"
Ya wani zaro ido waje.
"Inna itan ce tace nai mata wani abun nifa kawai biyoni tayi da kuka shiyasa na bar mata wurin"
"Oho ca nake kasan sanda ta faɗin, yanzu kayi sallah sai ka leƙa gidan nasu kaji yadda take nima danai sallar zan shiga"
Ya miƙa mata ledar furar tare da amsa mata da cewa.
"To"
Yana juyawa ya nufi ɗakin shi da fitilar ƙaramar wayarshi yayi amfani wajan haska banɗaki yayi uzirin gabanshi tare da ɗaura alwala, ya fita masallaci.
Bayan ya idar da sallar magariba, ya dawo É—aki yayi wanka Nura saiti ya kira a waya yana tambayar shi akan koya dawo Nurah yace mishi yana bakin titi yanzu zai shigo lungun da sauri yace masa inya shigo É—in ya biyo don Allah zai rakashi Gidansu Jiddah.
Zama yayi yana jiran Nuran bayan ya katse wayar jim kaÉ—an nurah ya shigo tashi kawai yayi suka fita.
A ƙofar gidan su Jiddah suka dakata yana tunanin ta yadda zai sami yaron da zai musu iso zuwa gidan dan shi yana jin nauyin kiran Umma a waya yace yazo.