Sashe 13
Sanadin Caca Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wayyo bayana"
Na faÉ—a ina kama kunkumi,gaskiya na dade banyi aiki mai yawa irin wannan ba.
Mopar na É—auka da bokitin ruwan dattin na fita dasu. Dawowa nayi ina kallon gyaran,gaskiya ya burgeni sosai,kalar kitchen É—in ya fito sosai kaman ba shiba.
Saidai ba girki za'ayi a cikiba,dan babu kayan abinci ma a ciki,na faÉ—an ina sunkuyar da kai.
Hanyar sashenmu na nufa nayi domin na tsaftace jikina,ga ƙura ga kuma dama ina son yin wankan..
Rana tayi a lokacin,dan har an fara kiran sallah a wasu masallatan na anguwa.
Hanyar cikin gidan na nufah,anan na haÉ—u da wannan wacce taje sashen Ahmad jiya.
Motarta ta buÉ—e ta fito,hannunta É—auke da key É—in mota tana kakkaÉ—awa..
Murmushi take da alama tana cikin yanayi mai kyau kenan,bata kuladani ba tashige cikin gidan. Nima yafimin,dan tun haÉ—uwar da mukayi jiya haka kawai naji bana sonta.
"Sumaimah ina kika shigane,daga zuwa gyaran sashe ɗaya sai yanzu kika dawo? Kizo to inna ladiyo tana nemanki,an ƙara miki aikin sashen hajiya maryam,mai aikinta bata nan ta tafi gida anyi mata rasuwa,kuma naji ana cewa wai aure zatayi"
"Kai aure kuma,yanzu shikenan aikina ya ƙaru?"
"Ohh da kinace a iya gyaran waccan wajen za'a baki dubu ashirin,nida kika ganni nan bayan wanke wanke ina gyaran sashen Æ´an biyun gidan"
"Suwaye kuma Æ´an biyu ohh sorry ashe inna ladiyo tafaÉ—amin yanda gidan yake da mutanen,wacce tashigo yanzu itace Mulaifah koh?"
Naƙarisa maganar a hankali kar a jiyoni.
"Ehh itace kinga ni inada aikinyi ba surutu ba,maza kije ki kai mata abinci,babban falo ma yana cikin sashenta,ke zaki dunga kulada shi keda Kultum"
"Wacece kuma Kultum?"
"Inkin fara aikin zaki santa ai,tana aikin kulada kaiwa abinci da kuma gyara sashen hajiya Mammah"
Wai da alama fah saina maida hankali,naga alamar bansan abubuwan gidan ba sosai,ta wani bangaren kuma naji daÉ—in yin aiki a sashen hajiyah maryam koba komai zan gano wacece ita..
Falon nata na shiga,babu kowa sai wata mata tana rubutu a system ɗin gabanta,farace kamar mamar tasu,tasa ƙaramin glass a fuskarta,ko ba'a fadaba nasan itace Maimuna,don Fatee itace ƙaramace ba kaman wannan ba,shekarar ƙarshe take a jami'a.
"Barka da rana hajiyah"
NafaÉ—a ina rusunawa,É—agowa tayi ta kalleni tareda yimin murmushi.
"Yawwa barka,amma kidaina cemin wannan hajiyar,anty Maimuna ma ya isa,kece wacce zata ƙarbi Amina kenan?"
Duk da bansan wa take nufi ba amma nasan wacce ta tafi take nufi.
"Eh nice"
"Ayya ki fara aikinki kawai,karki damu dani,amma ki fara da gyara ciki tukunna"
To nace tareda shigewa ciki,nazo buɗe ƙofar kenan naji ana magana sama sama.
"Hmmm kinji wata sabuwa kuma du,wai yanzu abin ya koma kan wa zai aura,aure ma yanzu bai isa yayi ba,saboda hakan matsala zai jawo. Ni na gaji da wannan abun sam"
Cikin masifah take maganar,mutum bazai gane haushin maganar takeji ko kuma haushin shi mai yin auren ba.
"Ta mutu mana ni mai ya shafeni dama yarinyar ba sonta nake ba, tunda ya dawo iya shegenta yafi na da,nakula baya son ita take rawarta take kiÉ—inta...............har yanzu babu wani zance ina gameda akwatinnan?
Gwanda ma da bai bayyana ba,dama banason yashiga wannan shugaba na ukun ballantana kuma hannun ta,to amma a ina kikega yake?........
Uhm mtsw wancan ba? shima so yake ya kawomin ciwon kai........,kedai ki cigaba da kulada abinda yake,nayi tunanin daya dawo zai bar wannan aikin ya kama wani,amma na kula taurin kaine dashi,zanyi magana dashi nayi masa gargaɗi idan yaƙi dainawa kuma bansan me zanyi ba gaba"
Maganganun sun isheni haka,a da inda zare mai baki kala kala,amma bansan a ina suke ba. Yanzu kuma na fara kamo bakin zarurrukan. Babu makawa dasaka hannun hajiyah maryam a dukkan komai dayake faruwa,harma da waccar ƙungiyar duk da saka hannunta a ciki.
A zuciye na tura ƙofar na shiga ɗakin,na manta ma da cewar itace fah mai juya komai.
Juyowa tayi ta sauri tana kallona,nayi saurin sauƙar da kaina ina rarraba ido.
"Ke kuma fah daga ina?"
"Uhm nice sabuwar mai aikin nan sashen"
"Ohh kuma shine kikayimin wannan shigowar tamkar an koroki"
"Kiyi haƙuri hajiyah,uhm barina farada banɗaki"
Cikeda tsoro da roƙon Allah yasa kada tace komai nayi hanyar banɗaki da sauri,saida naga na shige na maida ƙyauren kafin naja ajiyar zuciya,wayyo ni Sumaimah nakawo kaina ga hallaka.
Bayan nagama gyaran na fito kenan daga É—akin naga wata tashigo falon da sauri tana kuka kaman anyi mata mutuwa.
"Mommy mommy wayyo mommy"
Da ƙarfi take maganar,anty Maimuna tunda ta daga ido ta kalleta tacigaba da abinda take,da alama kenan ta saba hakan.
Hajiya maryam ce ta fito daga É—akin tana kallon Fatee.
Tana ganinta kuwa da sauri tazo ta rungumeta tareda ƙara sautin kukanta.
Nidai gefe na koma ina kallon ikon Allah.
"Yau kuma meya faru,ke wai bakya girmane uhm kullum kina cikin rigima?"
"Ba.....bba carry over HOD ɗin mu ya bani ba wai....kuma yana sane fah wannan ce shakarata ta ƙarshe,naje barrack kuma na faɗawa Abbah yace wai dole saina jira wata shekarar na gyarata,nasan da Mulaifah ce ai da yayi magana an barta ta wuce yiiiiihhhihiiiiii"
Kuka take tsakaninta da Allah har ranta.
"Hmmm wlh mommy karki yarda da zancenta,tana sane fah da za'ayi exam É—in amma tayi baccinta a gida,saboda ta saba Abbah yana magana a bata ta gyara,kuma dama tun wancan lokacin Abbah yace inta sake yin sakaci irin wannan bazai sake zuwa ba"
"Mommy karki yarda da itah wlh ba haka bane,ranar fah cikina ne yake ciwo"
"Yanzu dai duk ba wannan ba wanene HOD É—inna ku?"
"Alh sama'ila ne"
Jeki É—akinki ki huta kici abinci zanyi masa magana,yasaka miki gyarannata a first semester da za'a shiga"
"Mommmmmyyyyy........"
"Ya isa haka karki dameni,tunda bakiyi ta ba dole saikin gyara,karkuma ki dameni ki barni da abinda yake gabana"
Dariya anty Maimuna tafara yiwa Fatee wacce tacika kaman zata fashe,da tayi zaton intayi kukan basai ta gyaraba,amma tasan tunda mommy tace zata gyara to sai ta gyara É—in.
"Ke kuma zan fita idan anjima,zan duba miki shari'ar ko kin gano kanta"
"Ahah mommy a dubamin,har yanzu bangano yanda zan bi da itaba"
Gwaliyo tayiwa Fatee lokacin da hajiyah maryam taje kusada ita tana duba abinda yake cikin system É—innata.
Ohhh inda ranka kasha kallo,sudai wannan familyn basa zama waje É—aya kenan suyi shuru.
Ɗakinmu na nufa,ina shiga naji wayata tana ringing,dama jiya nayita ƙiran number Tunga amma bata shiga,ina dubawa kuwa naga shine yake ƙirana..
Da sauri na É—aga tareda yin sallama..
"Hello Tunga ina ka shiga baka É—aga waya?"
"Kiyi hakuri Sumaimah wlh munje sarin dankaline wani lungu jiyan,to basuda network wajen,ga innan dama tunda naga ƙiranki nasan su kike nema"
"Yawwa "
Muryar inna Mairo naji,bansan lokacin dana saki wani ajiyayyen murmushi ba.
"Innaaaa ina wuni ya gidan kuna nan ƙalau"
"Lafiya kalau ƴar nan ya wajen aikin,muna nan ƙalau ƙalau,gamunan ma Tunga ya kawo mana dankali mun dafa muna ci"
"Inna dama kin sani?"
"Nasan me?"
"Goje uhm......."
"Sumaimah ki bar zancennan,nasani amma babu abinda zan iya cemiki a yanzu saidai kiyi haƙuri da rufemiki danayi nasakaki a cikin duhu,amma babu yanda zanyi sai hakan"
"Bakomai inna nasan bazakiyi abinda zai cutar dani ba,amma abinkam akwai É—aure kai sosai,kici gaba dayimin addu'a toh."
"Da yardar Allah kuwa,hakan ba zai gagaraba,nasan kinga abubuwa da dama a rayuwarki na jarabawa,kuma kuma jure kikayi haƙuri,yanzu ma ki ƙara komai zai wuce nan kusa da yardar Allah."
"Ina khadija da Sayyid banjisu ba?"
Na ɗauko wani zancenne saboda kawar da wancan,a tunani na babu amfani naci gaba da faɗamata,tunda nasan hakan ba wani amfani zayyi sosai ba,saima na ƙara tada mata da hankali. A yanda naga abubuwan suke gudana na tabbatar ba laifinta bane na boyemin da tayi,hasalima tayine saboda hakanne kaɗai zabinta.
"Gasunan fah suna jinki,khadija ce ma yanzu tafita kaiwa su gaji É—aukin dankali"
"Ayyah nayi kewarku sosai,Sayyid ya daina kukan?"
"Hhhhhh ya daina mana,kijimin saikace dama ba tafiya kike makaranta ki barshi a gidaba,ya daina kuka yakama abincinsa"
"Shikenan sai anjima inna karna cinye masa katin waya,kucigaba da sakamu a addu'a"
Daga haka nayi sallama dasu na kashe wayar.
.........
Ahmad (POV)
Tun maganar danaji Sameer ya ambata har yanzu bayan na dawo office din ma na gagara aikata komai,gabaɗaya jin ƙwaƙwalwata nake a dagule.
Duk da cewar maganar tasa batada wani ma'ana zai iya yiyuwa wani yagani mai kamada ni,kuma dama gashi lokacin darene,amma nagagara barin zancen ya subuce a cikin kaina..
Abin ya faru a abuja ne,sannan kumadu a abuja na tashi na tsinci kaina. Kai ina dole sai nayi binciken wannan maganar,idan kuwa da gaske a tsawon wannan lokacin nayi aiki dasu,to ina buƙatar wannan memoryn,domin hakan zai bani sauƙin wajen gano inda suke.
Waya na ɗauka na ƙira Eemran akan maganar.
Bayan kaman minti talatin a zaune suke amma nagagara ce musu komai,suma kuma basuce dani ƙala ba.
Sai can bayan na gama yamutsa gashin kan kafin na É—ago na kallesu.
"Eemran da Neelah akwai wani aiki danake so na baku,please ya shafi aikinmu amma yafi shafar rayuwata,dan haka ban yarda kowa yaji ba harsai na gado ainihin mai yake faruwa tukunna.
"Shekara biyu baya na tashi na ganni a asibitin WUSE dake garinnan,inason ku samomin information na su waye suka kaini asibitin?"
Kallon juna suka farayi da alama tambayar tawa ta basu mamaki,tsawon wanna lokacin dana tashi,banama so a É—ago min zancen nayi rayuwa biyar bansani ba,amma yanzu inaso nagano a ina nake"
"Yallabai amma a baya idan akayi zancen bakaso,meyasa yanzu kuma lokaci É—aya.......?"
Neelah ce tayi tambayar amma bata ƙarisa ba,saboda tansan nagane mai take nufi..
"Buƙatar hakance ta taso,har yanzunma bawai na damu nasani ɗin bane,amma tunda har yaci karo da wannan aikin to vanida zabi. Please ku bincika sosai,inta kama ku nuna musu hotona ma,saboda ba lallaine da sunana nake amfani ba a da ɗin"
"To shikenan zamu iya ƙoƙarinmu akan case ɗin"
"Ogah zakaci abinci ne nayi order dakai"
Saida yayi zancen abinci ma na tuna rabona dashi tun jiya da daddare.
"Sure"
"Eh gaskiya kam gwanda ka dunka cin abinci,aiki ciki bai É—auka bama baya tafiyah daidai"
Cikeda zolaya yayi maganar kafin suka fita a tare,hmmm na koma tsohon aikinnawa wato tunani.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Na faÉ—a ina kama kunkumi,gaskiya na dade banyi aiki mai yawa irin wannan ba.
Mopar na É—auka da bokitin ruwan dattin na fita dasu. Dawowa nayi ina kallon gyaran,gaskiya ya burgeni sosai,kalar kitchen É—in ya fito sosai kaman ba shiba.
Saidai ba girki za'ayi a cikiba,dan babu kayan abinci ma a ciki,na faÉ—an ina sunkuyar da kai.
Hanyar sashenmu na nufa nayi domin na tsaftace jikina,ga ƙura ga kuma dama ina son yin wankan..
Rana tayi a lokacin,dan har an fara kiran sallah a wasu masallatan na anguwa.
Hanyar cikin gidan na nufah,anan na haÉ—u da wannan wacce taje sashen Ahmad jiya.
Motarta ta buÉ—e ta fito,hannunta É—auke da key É—in mota tana kakkaÉ—awa..
Murmushi take da alama tana cikin yanayi mai kyau kenan,bata kuladani ba tashige cikin gidan. Nima yafimin,dan tun haÉ—uwar da mukayi jiya haka kawai naji bana sonta.
"Sumaimah ina kika shigane,daga zuwa gyaran sashe ɗaya sai yanzu kika dawo? Kizo to inna ladiyo tana nemanki,an ƙara miki aikin sashen hajiya maryam,mai aikinta bata nan ta tafi gida anyi mata rasuwa,kuma naji ana cewa wai aure zatayi"
"Kai aure kuma,yanzu shikenan aikina ya ƙaru?"
"Ohh da kinace a iya gyaran waccan wajen za'a baki dubu ashirin,nida kika ganni nan bayan wanke wanke ina gyaran sashen Æ´an biyun gidan"
"Suwaye kuma Æ´an biyu ohh sorry ashe inna ladiyo tafaÉ—amin yanda gidan yake da mutanen,wacce tashigo yanzu itace Mulaifah koh?"
Naƙarisa maganar a hankali kar a jiyoni.
"Ehh itace kinga ni inada aikinyi ba surutu ba,maza kije ki kai mata abinci,babban falo ma yana cikin sashenta,ke zaki dunga kulada shi keda Kultum"
"Wacece kuma Kultum?"
"Inkin fara aikin zaki santa ai,tana aikin kulada kaiwa abinci da kuma gyara sashen hajiya Mammah"
Wai da alama fah saina maida hankali,naga alamar bansan abubuwan gidan ba sosai,ta wani bangaren kuma naji daÉ—in yin aiki a sashen hajiyah maryam koba komai zan gano wacece ita..
Falon nata na shiga,babu kowa sai wata mata tana rubutu a system ɗin gabanta,farace kamar mamar tasu,tasa ƙaramin glass a fuskarta,ko ba'a fadaba nasan itace Maimuna,don Fatee itace ƙaramace ba kaman wannan ba,shekarar ƙarshe take a jami'a.
"Barka da rana hajiyah"
NafaÉ—a ina rusunawa,É—agowa tayi ta kalleni tareda yimin murmushi.
"Yawwa barka,amma kidaina cemin wannan hajiyar,anty Maimuna ma ya isa,kece wacce zata ƙarbi Amina kenan?"
Duk da bansan wa take nufi ba amma nasan wacce ta tafi take nufi.
"Eh nice"
"Ayya ki fara aikinki kawai,karki damu dani,amma ki fara da gyara ciki tukunna"
To nace tareda shigewa ciki,nazo buɗe ƙofar kenan naji ana magana sama sama.
"Hmmm kinji wata sabuwa kuma du,wai yanzu abin ya koma kan wa zai aura,aure ma yanzu bai isa yayi ba,saboda hakan matsala zai jawo. Ni na gaji da wannan abun sam"
Cikin masifah take maganar,mutum bazai gane haushin maganar takeji ko kuma haushin shi mai yin auren ba.
"Ta mutu mana ni mai ya shafeni dama yarinyar ba sonta nake ba, tunda ya dawo iya shegenta yafi na da,nakula baya son ita take rawarta take kiÉ—inta...............har yanzu babu wani zance ina gameda akwatinnan?
Gwanda ma da bai bayyana ba,dama banason yashiga wannan shugaba na ukun ballantana kuma hannun ta,to amma a ina kikega yake?........
Uhm mtsw wancan ba? shima so yake ya kawomin ciwon kai........,kedai ki cigaba da kulada abinda yake,nayi tunanin daya dawo zai bar wannan aikin ya kama wani,amma na kula taurin kaine dashi,zanyi magana dashi nayi masa gargaɗi idan yaƙi dainawa kuma bansan me zanyi ba gaba"
Maganganun sun isheni haka,a da inda zare mai baki kala kala,amma bansan a ina suke ba. Yanzu kuma na fara kamo bakin zarurrukan. Babu makawa dasaka hannun hajiyah maryam a dukkan komai dayake faruwa,harma da waccar ƙungiyar duk da saka hannunta a ciki.
A zuciye na tura ƙofar na shiga ɗakin,na manta ma da cewar itace fah mai juya komai.
Juyowa tayi ta sauri tana kallona,nayi saurin sauƙar da kaina ina rarraba ido.
"Ke kuma fah daga ina?"
"Uhm nice sabuwar mai aikin nan sashen"
"Ohh kuma shine kikayimin wannan shigowar tamkar an koroki"
"Kiyi haƙuri hajiyah,uhm barina farada banɗaki"
Cikeda tsoro da roƙon Allah yasa kada tace komai nayi hanyar banɗaki da sauri,saida naga na shige na maida ƙyauren kafin naja ajiyar zuciya,wayyo ni Sumaimah nakawo kaina ga hallaka.
Bayan nagama gyaran na fito kenan daga É—akin naga wata tashigo falon da sauri tana kuka kaman anyi mata mutuwa.
"Mommy mommy wayyo mommy"
Da ƙarfi take maganar,anty Maimuna tunda ta daga ido ta kalleta tacigaba da abinda take,da alama kenan ta saba hakan.
Hajiya maryam ce ta fito daga É—akin tana kallon Fatee.
Tana ganinta kuwa da sauri tazo ta rungumeta tareda ƙara sautin kukanta.
Nidai gefe na koma ina kallon ikon Allah.
"Yau kuma meya faru,ke wai bakya girmane uhm kullum kina cikin rigima?"
"Ba.....bba carry over HOD ɗin mu ya bani ba wai....kuma yana sane fah wannan ce shakarata ta ƙarshe,naje barrack kuma na faɗawa Abbah yace wai dole saina jira wata shekarar na gyarata,nasan da Mulaifah ce ai da yayi magana an barta ta wuce yiiiiihhhihiiiiii"
Kuka take tsakaninta da Allah har ranta.
"Hmmm wlh mommy karki yarda da zancenta,tana sane fah da za'ayi exam É—in amma tayi baccinta a gida,saboda ta saba Abbah yana magana a bata ta gyara,kuma dama tun wancan lokacin Abbah yace inta sake yin sakaci irin wannan bazai sake zuwa ba"
"Mommy karki yarda da itah wlh ba haka bane,ranar fah cikina ne yake ciwo"
"Yanzu dai duk ba wannan ba wanene HOD É—inna ku?"
"Alh sama'ila ne"
Jeki É—akinki ki huta kici abinci zanyi masa magana,yasaka miki gyarannata a first semester da za'a shiga"
"Mommmmmyyyyy........"
"Ya isa haka karki dameni,tunda bakiyi ta ba dole saikin gyara,karkuma ki dameni ki barni da abinda yake gabana"
Dariya anty Maimuna tafara yiwa Fatee wacce tacika kaman zata fashe,da tayi zaton intayi kukan basai ta gyaraba,amma tasan tunda mommy tace zata gyara to sai ta gyara É—in.
"Ke kuma zan fita idan anjima,zan duba miki shari'ar ko kin gano kanta"
"Ahah mommy a dubamin,har yanzu bangano yanda zan bi da itaba"
Gwaliyo tayiwa Fatee lokacin da hajiyah maryam taje kusada ita tana duba abinda yake cikin system É—innata.
Ohhh inda ranka kasha kallo,sudai wannan familyn basa zama waje É—aya kenan suyi shuru.
Ɗakinmu na nufa,ina shiga naji wayata tana ringing,dama jiya nayita ƙiran number Tunga amma bata shiga,ina dubawa kuwa naga shine yake ƙirana..
Da sauri na É—aga tareda yin sallama..
"Hello Tunga ina ka shiga baka É—aga waya?"
"Kiyi hakuri Sumaimah wlh munje sarin dankaline wani lungu jiyan,to basuda network wajen,ga innan dama tunda naga ƙiranki nasan su kike nema"
"Yawwa "
Muryar inna Mairo naji,bansan lokacin dana saki wani ajiyayyen murmushi ba.
"Innaaaa ina wuni ya gidan kuna nan ƙalau"
"Lafiya kalau ƴar nan ya wajen aikin,muna nan ƙalau ƙalau,gamunan ma Tunga ya kawo mana dankali mun dafa muna ci"
"Inna dama kin sani?"
"Nasan me?"
"Goje uhm......."
"Sumaimah ki bar zancennan,nasani amma babu abinda zan iya cemiki a yanzu saidai kiyi haƙuri da rufemiki danayi nasakaki a cikin duhu,amma babu yanda zanyi sai hakan"
"Bakomai inna nasan bazakiyi abinda zai cutar dani ba,amma abinkam akwai É—aure kai sosai,kici gaba dayimin addu'a toh."
"Da yardar Allah kuwa,hakan ba zai gagaraba,nasan kinga abubuwa da dama a rayuwarki na jarabawa,kuma kuma jure kikayi haƙuri,yanzu ma ki ƙara komai zai wuce nan kusa da yardar Allah."
"Ina khadija da Sayyid banjisu ba?"
Na ɗauko wani zancenne saboda kawar da wancan,a tunani na babu amfani naci gaba da faɗamata,tunda nasan hakan ba wani amfani zayyi sosai ba,saima na ƙara tada mata da hankali. A yanda naga abubuwan suke gudana na tabbatar ba laifinta bane na boyemin da tayi,hasalima tayine saboda hakanne kaɗai zabinta.
"Gasunan fah suna jinki,khadija ce ma yanzu tafita kaiwa su gaji É—aukin dankali"
"Ayyah nayi kewarku sosai,Sayyid ya daina kukan?"
"Hhhhhh ya daina mana,kijimin saikace dama ba tafiya kike makaranta ki barshi a gidaba,ya daina kuka yakama abincinsa"
"Shikenan sai anjima inna karna cinye masa katin waya,kucigaba da sakamu a addu'a"
Daga haka nayi sallama dasu na kashe wayar.
.........
Ahmad (POV)
Tun maganar danaji Sameer ya ambata har yanzu bayan na dawo office din ma na gagara aikata komai,gabaɗaya jin ƙwaƙwalwata nake a dagule.
Duk da cewar maganar tasa batada wani ma'ana zai iya yiyuwa wani yagani mai kamada ni,kuma dama gashi lokacin darene,amma nagagara barin zancen ya subuce a cikin kaina..
Abin ya faru a abuja ne,sannan kumadu a abuja na tashi na tsinci kaina. Kai ina dole sai nayi binciken wannan maganar,idan kuwa da gaske a tsawon wannan lokacin nayi aiki dasu,to ina buƙatar wannan memoryn,domin hakan zai bani sauƙin wajen gano inda suke.
Waya na ɗauka na ƙira Eemran akan maganar.
Bayan kaman minti talatin a zaune suke amma nagagara ce musu komai,suma kuma basuce dani ƙala ba.
Sai can bayan na gama yamutsa gashin kan kafin na É—ago na kallesu.
"Eemran da Neelah akwai wani aiki danake so na baku,please ya shafi aikinmu amma yafi shafar rayuwata,dan haka ban yarda kowa yaji ba harsai na gado ainihin mai yake faruwa tukunna.
"Shekara biyu baya na tashi na ganni a asibitin WUSE dake garinnan,inason ku samomin information na su waye suka kaini asibitin?"
Kallon juna suka farayi da alama tambayar tawa ta basu mamaki,tsawon wanna lokacin dana tashi,banama so a É—ago min zancen nayi rayuwa biyar bansani ba,amma yanzu inaso nagano a ina nake"
"Yallabai amma a baya idan akayi zancen bakaso,meyasa yanzu kuma lokaci É—aya.......?"
Neelah ce tayi tambayar amma bata ƙarisa ba,saboda tansan nagane mai take nufi..
"Buƙatar hakance ta taso,har yanzunma bawai na damu nasani ɗin bane,amma tunda har yaci karo da wannan aikin to vanida zabi. Please ku bincika sosai,inta kama ku nuna musu hotona ma,saboda ba lallaine da sunana nake amfani ba a da ɗin"
"To shikenan zamu iya ƙoƙarinmu akan case ɗin"
"Ogah zakaci abinci ne nayi order dakai"
Saida yayi zancen abinci ma na tuna rabona dashi tun jiya da daddare.
"Sure"
"Eh gaskiya kam gwanda ka dunka cin abinci,aiki ciki bai É—auka bama baya tafiyah daidai"
Cikeda zolaya yayi maganar kafin suka fita a tare,hmmm na koma tsohon aikinnawa wato tunani.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem