Sashe 42
Sanadin Caca Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Yau kimanin sati guda kenan da zaman goje a bayan garin,kwana uku nayi ina jinyarsa sosai,dakuma kwana dashi. Dagan nanne ya hanani zama sosai,sai Tunga ne yake kwana dashi.
A iya satin kawai har yasamu sauƙi yana tashi dakans,kasancewar dama jikine yasan wahala.
Yau banje wajensa ba,gyaran ƙofar tasa nakeyi,dan jiya da naje yake cemin yau zai dawo gida.
Inna batasan yana garin ba,ita a zatonta daga can wajen aikin zai dawo,dama kuma bayason tasan halinda yake ciki.
Kayan É—akin na fitar dukka wannan tarkacen,iyah katifarsa na bari sai sallaya da kuma akwatin kayansa,sauran shirgin da baza'ayi amfani dasu ba zubarsu nayi,wasu kuma nakaisu É—akin gefen inna..
Wani kuwa nashashi tun safe nake har rana tayi,dana gama na É—ora girki. Yau ba makarantar safe weekend ne sai islamiyya kaÉ—ai,itakuma banje ba.
Saida na gama abincin rana nayi wanka nayi sallah kafinnasamu na zauna,inna sai sannu take jeramin.
Kursiyyah ce ta shigo ƙofar tamu hannunta ɗauke da ɗa kwano,wanda nasan awara ce.
Bayanta ajiye kwanon abincinsu wanda muke zuba musu ta ɗauka,dan dama sun saba yanzu ko magana basayi ɗauka kawai suke....shuru kowa yana ƙofarsa ta ciki na ciki.
Sai bayan la'asar na ɗauko qur'ani kenan zanyi tilawa naji muryar Tunga shida goje,har yanzu duk sanda naji motsinsa ko kuma muryarsa sai gaba yaɗan buga ɗinnan,wanda bansan menene dalilin ba. Tun da rana nake jiran dawowar tasa,har na haƙura tukunna suka shigo.
Ban tashi daga inda nake ba inaji har suka shigo cikin É—akin innan.
Akan kujerar da take ɗakin ya zauna,yasaka kayansa wanda yatafi dasu baƙaƙe.
Gaisawa suke da inna amma kana ganin kasan yasha wahala a tafiyar da suka iyo É—in,yana daurewa ne kada ya nuna rauninsa.
Shi Tunga tun a tsakar gida ya koma,wanda nasan goje yace masa ya tafin.
Ido muka haÉ—a dashi ya kashemin ido guda É—aya ,É—auke idona nayi tareda ajiye qur'anin nafita daga É—akin.
Kofarsa na nufah nasake gyara komai,ruwa na kai a jug mai sanyi wanda shine dama bankai ba kada yayi É—umi.
Hucin numfashinsa nafara ji a bayana,dan dama najiyo takun sawunsa.
A gadon bayana ya kwantar da kansa tareda saƙalo hannayensa ta cikina,tsayawa nayi daga tashi tsayen ina sauraran numfashinsa wanda yake fitar dashi kaman mutum yayi gudu.
"Kinsan nagaji meyasa kika taho kika barni a ɗakin inna,daƙyar fah na iso wajennan"
"Hhhhh sannu toh,a mashin kukazo ne daga can?"
"Uhmm a gashi duk gonakin mutanene a hanyar,sai jijjiga ni Tunga yake tayi a hanya,wajen ciwo yakemin kaman yanzu nayi raunin"
Jin abinda yafaɗa yasa nafara ƙoƙarin cire hannunsa daga kunkumina,amma kuma sai ya sake riƙeni kaman zai maidani ciki.
"Kace wajen yana ciwo,yakamata a duba kar ko ya buÉ—e,sannan ka haÉ—a gumi yakamata kayi wanka kaci abinci,saika sake shan maganin"
Cikin nuna damuwa nake maganar,ai yayi ƙoƙari ma da nice da wannan ciwo bazan iya tashi ba.
Tashi yayi daga bayannawa ya dawo kan katifa ya zauna,ɗakin yake ƙarewa kallo baki buɗe.
"Wow dama É—akinnan yanada girma kaman haka,ban taba saniba saboda shirginsa,gaskiya kinsha aiki sosai na gyarashi"
Ƴar dariya nayi tareda matsawa na cire masa canvas ɗin ƙafarsa.
"Tohh yanzu abinci zaka faraci kokuma wanka zakayi?"
"Uhm bari naci abincin,dan yunwa nake ji sosai,sannan inason shan magani,saboda tafiyar danayi wajen yana min ciwo sosai"
Yaƙarisa maganar harda lumshe ido yana maida numfashi. Ganin yanda yake bansan lokacin dana kai hannuna ba na bude maballin rigar,wajen da ciwon yake nake kallo,hatta fatar cikinsa ma tayi ja,saidai bayyi jini ba alama yafara kamewa kenan.
"Uhm take it easy mana madam,sauri kike har haka ne?"
Yanayin magana na kulada yanda na É—ora hannayena akan cikinsa,saurin janyewa nayi tareda matsawa baya. Me yake damuna ne haka,yaushe na fara É—aukar taba jikinsa ba komai bane ba.
Dariya yakeyimin tareda ƙarisa cire rigar gabaɗaya ya ajiye a gefe.
"Uhm nagode da kulawarki,hakan yana yimin daÉ—i idan naga kin damuwa da halinda nake ciki,sannan karki damu bazan É—auki komai ba dan kin taba jikina,ya hallata a garekine ba shiyasa kika taba ba uhm?"
Ohh kunya ce takamani naji kaman na nutse a ƙasa,maza fa daman sun iya zarar zance.
"Yawwa yanzu naji kayi turanci dama ka iya ne?"
Nayimasa tambayar dan ya manta da waccar maganar,kaman hakan kuwa yayi tasiri,dannaga ya tafi tunani.
"Turanci kikaji nayi,uhm zai iya yiyuwa,dan wani lokacin mutane kan faÉ—a cewar inayi,ko karanta rubutu danake kawai gani nayi ina rubutawa,amma ban tuno makarantar danayi ba kuma"
"Taya ya hakan zai kasance toh?"
"Uhm ta haka mana,zubamin abincin naci inason shan maganinnan"
Zancenne yaƙare a haka na zuba masa abincin kaman yanda ya buƙata.
Har yashiga wanka ya fito ina zaune a ɗakin,dan cewa yayi kada na tafi na jirashi,daga shi sai gajeran wando ya shigo yana goge kansa da,wani ƙaramin ƙyalle.
ÆŠauke kaina nayi,amma sai naji ya zauna a kusadani har muna gogar juna...ohh wannan sabon hali na goje na kasa gane kansa sam.
Mai yasaka na miƙo masa yafara shafawa,shuru mukayi dagani harshi babu wanda yace komai.
Tashi nayi zan tafi ya riƙo hannuna,
"Ina kuma zakije,ni kaÉ—ai zaki tafi ki bari a É—akin?"
"Uhn zan É—ora girkin dare,Sannan ba kace bacci zakayi ba?"
"Oh na tuna,to ki dunga zuwa kina leƙowa akai akai harna tashi"
"Hhhh to shikenan yanzu na tafi?"
ÆŠaga kai yayi kaman baya so,wai dama wannan bawan Allah haka yake ne,kokuma yanzu ya koyi waÉ—annan abubuwan..
Bayan na fito inna tayi mamakin daÉ—ewata a wajen gojen,amma batace komai ba,nima kuma banyi maganar ba.
Ina cikin jajjaga kayan miya naga ya fito daga ɗakinnasa ya fita,ƙananan kayane a jikinsa yana tafiya normal ba wannan bubbuɗawar. Ko ciwonne yasakashi oho..
Tsayawa nayi daga abinda nake na zubawa bayansa ido yana tafiyar,saida yaje saitin zaure ya juyo muka haÉ—a ido.
Kunya ce ta rufeni ganin yakamani ina kallonsa,da hannu yayi min alama nazo,fuskarsa É—aukeda murmushi.
Zatona wani abu zaicemin,sai kawai ji nayi ya sumbaci goshina,tareda É—allamin yatsarsa kuma a wajen duk lokaci guda.
Shafa wajen nayi tareda turo baki.
"Meyasa dana juyo kika É—auke idonki kaman wacce nakamaki kina laifi?"
"Dama zaka iya fita ne?"
"Silly girl na kula wani lokacin idan bakyason bani amsa saiki yimin tambaya koh"
Hannu yakawo zai sakeyimin É—all amma wannan karon na koma gefe ina dariyah,shima murmushi yayi tareda cewa.
"Zanje wajen su dunga ne karsuga shuru bayan sunsan nadawo"
"Banda bawa mutanen gari tsoro"
NafaÉ—a ina komawa cikin gidan da sauri,yanda nasan bazai dawo ya kamani ba.
__***__
A iya satin kawai har yasamu sauƙi yana tashi dakans,kasancewar dama jikine yasan wahala.
Yau banje wajensa ba,gyaran ƙofar tasa nakeyi,dan jiya da naje yake cemin yau zai dawo gida.
Inna batasan yana garin ba,ita a zatonta daga can wajen aikin zai dawo,dama kuma bayason tasan halinda yake ciki.
Kayan É—akin na fitar dukka wannan tarkacen,iyah katifarsa na bari sai sallaya da kuma akwatin kayansa,sauran shirgin da baza'ayi amfani dasu ba zubarsu nayi,wasu kuma nakaisu É—akin gefen inna..
Wani kuwa nashashi tun safe nake har rana tayi,dana gama na É—ora girki. Yau ba makarantar safe weekend ne sai islamiyya kaÉ—ai,itakuma banje ba.
Saida na gama abincin rana nayi wanka nayi sallah kafinnasamu na zauna,inna sai sannu take jeramin.
Kursiyyah ce ta shigo ƙofar tamu hannunta ɗauke da ɗa kwano,wanda nasan awara ce.
Bayanta ajiye kwanon abincinsu wanda muke zuba musu ta ɗauka,dan dama sun saba yanzu ko magana basayi ɗauka kawai suke....shuru kowa yana ƙofarsa ta ciki na ciki.
Sai bayan la'asar na ɗauko qur'ani kenan zanyi tilawa naji muryar Tunga shida goje,har yanzu duk sanda naji motsinsa ko kuma muryarsa sai gaba yaɗan buga ɗinnan,wanda bansan menene dalilin ba. Tun da rana nake jiran dawowar tasa,har na haƙura tukunna suka shigo.
Ban tashi daga inda nake ba inaji har suka shigo cikin É—akin innan.
Akan kujerar da take ɗakin ya zauna,yasaka kayansa wanda yatafi dasu baƙaƙe.
Gaisawa suke da inna amma kana ganin kasan yasha wahala a tafiyar da suka iyo É—in,yana daurewa ne kada ya nuna rauninsa.
Shi Tunga tun a tsakar gida ya koma,wanda nasan goje yace masa ya tafin.
Ido muka haÉ—a dashi ya kashemin ido guda É—aya ,É—auke idona nayi tareda ajiye qur'anin nafita daga É—akin.
Kofarsa na nufah nasake gyara komai,ruwa na kai a jug mai sanyi wanda shine dama bankai ba kada yayi É—umi.
Hucin numfashinsa nafara ji a bayana,dan dama najiyo takun sawunsa.
A gadon bayana ya kwantar da kansa tareda saƙalo hannayensa ta cikina,tsayawa nayi daga tashi tsayen ina sauraran numfashinsa wanda yake fitar dashi kaman mutum yayi gudu.
"Kinsan nagaji meyasa kika taho kika barni a ɗakin inna,daƙyar fah na iso wajennan"
"Hhhhh sannu toh,a mashin kukazo ne daga can?"
"Uhmm a gashi duk gonakin mutanene a hanyar,sai jijjiga ni Tunga yake tayi a hanya,wajen ciwo yakemin kaman yanzu nayi raunin"
Jin abinda yafaɗa yasa nafara ƙoƙarin cire hannunsa daga kunkumina,amma kuma sai ya sake riƙeni kaman zai maidani ciki.
"Kace wajen yana ciwo,yakamata a duba kar ko ya buÉ—e,sannan ka haÉ—a gumi yakamata kayi wanka kaci abinci,saika sake shan maganin"
Cikin nuna damuwa nake maganar,ai yayi ƙoƙari ma da nice da wannan ciwo bazan iya tashi ba.
Tashi yayi daga bayannawa ya dawo kan katifa ya zauna,ɗakin yake ƙarewa kallo baki buɗe.
"Wow dama É—akinnan yanada girma kaman haka,ban taba saniba saboda shirginsa,gaskiya kinsha aiki sosai na gyarashi"
Ƴar dariya nayi tareda matsawa na cire masa canvas ɗin ƙafarsa.
"Tohh yanzu abinci zaka faraci kokuma wanka zakayi?"
"Uhm bari naci abincin,dan yunwa nake ji sosai,sannan inason shan magani,saboda tafiyar danayi wajen yana min ciwo sosai"
Yaƙarisa maganar harda lumshe ido yana maida numfashi. Ganin yanda yake bansan lokacin dana kai hannuna ba na bude maballin rigar,wajen da ciwon yake nake kallo,hatta fatar cikinsa ma tayi ja,saidai bayyi jini ba alama yafara kamewa kenan.
"Uhm take it easy mana madam,sauri kike har haka ne?"
Yanayin magana na kulada yanda na É—ora hannayena akan cikinsa,saurin janyewa nayi tareda matsawa baya. Me yake damuna ne haka,yaushe na fara É—aukar taba jikinsa ba komai bane ba.
Dariya yakeyimin tareda ƙarisa cire rigar gabaɗaya ya ajiye a gefe.
"Uhm nagode da kulawarki,hakan yana yimin daÉ—i idan naga kin damuwa da halinda nake ciki,sannan karki damu bazan É—auki komai ba dan kin taba jikina,ya hallata a garekine ba shiyasa kika taba ba uhm?"
Ohh kunya ce takamani naji kaman na nutse a ƙasa,maza fa daman sun iya zarar zance.
"Yawwa yanzu naji kayi turanci dama ka iya ne?"
Nayimasa tambayar dan ya manta da waccar maganar,kaman hakan kuwa yayi tasiri,dannaga ya tafi tunani.
"Turanci kikaji nayi,uhm zai iya yiyuwa,dan wani lokacin mutane kan faÉ—a cewar inayi,ko karanta rubutu danake kawai gani nayi ina rubutawa,amma ban tuno makarantar danayi ba kuma"
"Taya ya hakan zai kasance toh?"
"Uhm ta haka mana,zubamin abincin naci inason shan maganinnan"
Zancenne yaƙare a haka na zuba masa abincin kaman yanda ya buƙata.
Har yashiga wanka ya fito ina zaune a ɗakin,dan cewa yayi kada na tafi na jirashi,daga shi sai gajeran wando ya shigo yana goge kansa da,wani ƙaramin ƙyalle.
ÆŠauke kaina nayi,amma sai naji ya zauna a kusadani har muna gogar juna...ohh wannan sabon hali na goje na kasa gane kansa sam.
Mai yasaka na miƙo masa yafara shafawa,shuru mukayi dagani harshi babu wanda yace komai.
Tashi nayi zan tafi ya riƙo hannuna,
"Ina kuma zakije,ni kaÉ—ai zaki tafi ki bari a É—akin?"
"Uhn zan É—ora girkin dare,Sannan ba kace bacci zakayi ba?"
"Oh na tuna,to ki dunga zuwa kina leƙowa akai akai harna tashi"
"Hhhh to shikenan yanzu na tafi?"
ÆŠaga kai yayi kaman baya so,wai dama wannan bawan Allah haka yake ne,kokuma yanzu ya koyi waÉ—annan abubuwan..
Bayan na fito inna tayi mamakin daÉ—ewata a wajen gojen,amma batace komai ba,nima kuma banyi maganar ba.
Ina cikin jajjaga kayan miya naga ya fito daga ɗakinnasa ya fita,ƙananan kayane a jikinsa yana tafiya normal ba wannan bubbuɗawar. Ko ciwonne yasakashi oho..
Tsayawa nayi daga abinda nake na zubawa bayansa ido yana tafiyar,saida yaje saitin zaure ya juyo muka haÉ—a ido.
Kunya ce ta rufeni ganin yakamani ina kallonsa,da hannu yayi min alama nazo,fuskarsa É—aukeda murmushi.
Zatona wani abu zaicemin,sai kawai ji nayi ya sumbaci goshina,tareda É—allamin yatsarsa kuma a wajen duk lokaci guda.
Shafa wajen nayi tareda turo baki.
"Meyasa dana juyo kika É—auke idonki kaman wacce nakamaki kina laifi?"
"Dama zaka iya fita ne?"
"Silly girl na kula wani lokacin idan bakyason bani amsa saiki yimin tambaya koh"
Hannu yakawo zai sakeyimin É—all amma wannan karon na koma gefe ina dariyah,shima murmushi yayi tareda cewa.
"Zanje wajen su dunga ne karsuga shuru bayan sunsan nadawo"
"Banda bawa mutanen gari tsoro"
NafaÉ—a ina komawa cikin gidan da sauri,yanda nasan bazai dawo ya kamani ba.
__***__