← Book details Sanadin Caca Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 47

Sashe 32

Sanadin Caca Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Motocinsa suna shiga gidan na Mrs Aliyu Hamma wato Hajiyah Maryam kuma suna shirin zasu fita daga gidan.
Har an tada motar da take cikin suka tsaya,fitowa tayi daga cikin motar tana kallon A.M aliyu ta cikin farin glass É—in idonta.
Farace tass ƙirar fulani,sannan kuma tanada kamammen jiki,duk da ta ɗan ga jiyah amma jikinta sam bai nuna ba,kana kallonta batayi kama da iyayen da za'a ƙirasu masu sanyin rai ba,dan ko a gidan kowa yasani hatta barrak ɗin,daka shiga shirgin Hajiya Maryam kwanta kaje da kanka ka faɗa hallaka,domin bata barin kota kwana,kowa abinda taga dama take fesa masa,ciki kuwa har shi kansa mijinnata bai isa ba.
Ƴaƴan ta huɗune a gidan Saleem Da Sameer ƴan biyune,saikuma Maimuna da fatima itace ƴar auta. Duk duniya su kaɗai take gani da gashi a rayuwarta,duk da cewar basune kaɗai ƴaƴan A.M Aliyu Hamma ba,yanada wani ɗan Wato Ahmad Aliyu Hamma,shine babban dansa kuma mahaifiyarsa ta rasu. Saidai shima ya rasu sanadiyyar hatsarin mota,shekara biyar dasuka wuce. Wasu sunce a garin ba hatsari bane haɗashi aka akayi,saidai babu wanda ya isa ya ɗago zancen har a yanzu....
Sameer soja ne kaman Ahmad sanda yakesa rai,saidai shi ba'a bangaren bincike yake aiki ba.
Saleem kuma Medical lab scientist ne,yanada sha'awar nazari akan abinda ya shafi bincike,musamman abinda ya haÉ—a da yanayin rayuwar mutane.
Sai kuma Maimuna lawyer ce,saidai ita ba wani cikyakykyiyar lafiya ce da ita ba,tayi aure amma batayi sa'ar miji ba,Allah ya haɗata da shashasha,gata da sanyin hali itada Saleem. Ita kuma fatima wacce ake ƙira da fatee,karatu takeyi,sannan ita halinsu ɗaya da sameer wajen zafin rai,sune suka iyo mahaifiyar tasu wato hajiya Maryam........
Ƙwasƙwas take tafiyah harta iso kusada shi.
"Abban fatee yana ganka ka dawo da wuri haka?"
Shuru yayi baice komai,dan indai abune daya shafi tsaronsa bayayin maganar da itah,saboda shi kansa yasan bai yadda da itah ba sam.Kawar da tambayartata yayi ta hanyar cewa.
"Ina zaki bayan Mammamah batada lafiyah"
"Taro zanje na manyan matan ƙasa,yanada muhimmanci,kar kace komai dan bazan fasa tafiyah ba ma,sai kace kana magana da ƙaramar yarinya,zazzabi ne fah zata iyah kulada kanta ai"
Tana gama faÉ—in hakan bata tsaya tambayar mai ya dawo dashi ba ta yi gaba.
Jijjiga kai yayi ya ƙarisa cikin gidan,shima dama yasan dole sai tayi maganar banza ga mahaifiyar tasa,yarasa meyasa taƙi jinin Mahaifiyarsa,bayan ita kuma kullum cikin son Maryam ɗin take,duk sanda yayi yunƙurin sakinta itace take hanashi har aka kawo wannan lokacin,tun abin yana damunsa har ya daina ma.
Ba sashensa ya nufah ba,sashen mahaifiyar tasa ya nufah,daÉ—in yanada uwa kenan,tunda mata bazatayi aikinta ba....

Sorry amin afuwa kunji labari yayi tsallen kurege ko?? Karku damu zan haÉ—ashi waje É—aya,kuma da sannu zaku gane......

Littafi na É—aya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na É—aya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Shaida kuma ta nan
09035784150

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please

*SANADIN CACA*

Mallakar SADI-SAKHNA

PROFICIENT WRITER ASSOCIATION

*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[21]

Saida A.M Aliyu yaje kusada sashen Mammah kafin ya yiwa masu take masa baya alamar su tsaya,dan tasha faÉ—amasa batasan yana shiga mata da wasu masu tsaron lafiyarsa wajenta.
Tafiyah yake shi kaÉ—ai har ya shiga falonnata na farko,gabaÉ—aya wajen idan mutum yashiga sai ya É—auka cewar a cikin faÉ—ar gargajiya yake,amma ta faÉ—a a gani. Kasancewarta daman ita Æ´ar sarautar Zaria ce.
Hadimai ne suke ta kai kawo wajen ganin wajen ya kasance tsaff kuma mai ƙamshi da daɗin gani.
Tun a wajen ya cire takalmanta yana taka carfet É—in daya shimfiÉ—e wajen har zuwa bakin turakarta.
Mai aikinta ce ta hannun damansa tayi masa iso kafin ya shiga. Dama da itah sukazo gidan tunda akayi aurenta,kusan itace ma tayi rainon A.M Aliyu.
"Ranka ya daÉ—e tace zaka iyah shiga"
ÆŠaga kai yayi daga nan yasaka kai zuwa cikin É—akin,a zaune take da farin mayafi a jikinta ta lullube ko ina da shi,da kaÉ—an kake gano jar doguwar rigar da take jikinnata. Akan sallayah take hannunta É—auke da carbi,da alama lazumi takeyi..
Tsugunnawa yayi a gabanta tareda kama hannunta ya riƙe,yana masifar son mahaifiyar tasa,sannan baya tunanin akwai ranar dazai daina alfahari da ita,kasancewarta mai dattako dakuma tausayin na ƙasa da itah,shi bai san meyasa matarsa takasa godewa Allah da irin wannan suruka data samu ba.
Murmushi tasakar masa mai taushi tareda dafa kansa,duk da kana ganinta kasan dattijuwa ce,amma kuma a yanayin kallonta bazaka ce ta haifi A.M Aliyu ba.
"Mai samu wannan gwarzon jarumin haka?"
"Mammah wannan case ɗin na BC ya dameni,tsawon shekara bakwai tun Ahmad nada rai shima yayi iya ƙoƙarinsa,amma har yanzu abu ya gagara,mun kasa gano sirrinsu da kuma inda suke"
Murmushi tasake sake masa wanda yakesa yaji duk damuwar sa ta kau.
"Karka damu Abban Saleem komai na duniya a sannu ake binsa,sannan da sannu lagonsu zai karye kuyi nasara akan su,naga a labarai wai sun kai hari Local govt É—in gwagwalada koh?"
"Hmmm haka fah,Gen Saeed ne akan aikin,amma da alama shima abun yafara gagararsa,gashi gwamnati na shirin ɗauke case ɗin daga wajenmu ta maidashi ƙarƙashin Civil security,wanda kuma nasan bazasu iya da aikin ba,yanada hatsari sosai"
Cikeda damuwa ya ƙarisa magana,duk da shi jarumine kuma wanda baya juya ƙasa da wuri,amma ga mahaifiyar tasa shi mai raunine dayake buƙatar tallafinta.
Tausarsa ta dungayi da kuma bashi baki har hakan yayi tasiri a ransa.

___***___

[Sumaimah a mahangar gani]

Yau kimanin kwana uku kenan da kaini asibiti da goje yayi,abubuwa da dama sun faru,ciki harda samun sauƙi danayi na hannuna,bana komai a gidan saidai nayi wanka na kwanta. Abinci kuwa kullum sau uku goje yake kawomin a rana,kuma dukka mai daɗi da rai da lafiyah,shikansa na kula shigarsa ta sanja ba kaman ta da ba,yayi kaya da yawa kala kala,mashinɗin daya kaini asibiti dashi ma ashe nasa ne,koda yake siyasa ta zo ai dole su samu kuɗi.
Hannayena sun warke sai sa'ba da sukeyi,kasancewar maganin mai tsada ne da kuma kyau.
A bangaren su gaji kuwa ko kallon rashin arziƙi basa yimin,saboda mungun gargaɗin da goje yayi musu,kullum da safe zan jisu suna faɗa akan wanke wanke,ko leƙasu banayi balle nasan mai sukeyi.
Yanzu ma a zaune nake ina kallon jikina,naƙara ɗan haske da kuma ƙiba,a iya kwana biyu kawai. Ashe dai hutu yanada daɗi,inaga tunda nayi wayo ban taba yin hutu kaman wannan ba.
Ledar dana gama cin indomie na É—auke da kuma kofin na fita da su.
Da gaji muka haÉ—a ido tana É—iban itace a wani fili dayake gefen É—akunan inna mairo.
Harara ta maka min amma batace ƙala ba,nima daga kallo ɗaya bansake kallonta ba na saka ledar a shara na wanke kofina.
Koba komai dai na huta da muguntarta koda na kwana uku ne,dan har yanzu ban daina tunanin wataƙila goje zai daina bani abinci idan na warke.
Tsintsiya na ɗauka na share ɗakin da kuma barandar,har zan tafi wata zuciyar tace da na gyarawa goje sashensa ai tunda na samu sauƙi.
Cikin kasada kuwa na nufi ƙofar tasa,tayi datti kam ba laifi,haka yake rayuwa a ciki,koda yake kanna zo ma ai haka yake,kuma dan ya kulada ni kwana biyu bashi yake saka cewa wai ya shiryu bane daga yanda yake wata zuciyar ta fadamin.
Randarsa kam a cike take da ruwa,kasancewar yanzu hamisu ne ƙanin kursiyyah mai wanann aikin.
Makullin daya bani kwanaki na saka na buÉ—e É—akin,hannu na saka ina kaÉ—e hancina,banda hamamin maza babu abinda É—akin yake.
Uhmm hali zanen dutse.
Na faɗa a raina,wangale windown ɗakin nayi dana ƙofar,kayansa daya zuzzubar a ƙasa na ɗebe na saka su a gefe.
Saidai na fara da gyara fasalin É—akin kafin na share shi,kayan daya 'bata kuma na fito dasu daga É—akin,shin zanyi iya wanki kuwa dana fito dasu.
Tunani nake hannuna a kunkumi ina kallonsu,duk da hannuna ya warke amma bai gama komawa daidai ba,idan nace zan murza kayan wanki toh sai koma baya.
"Dama waye yace kiyi aiki da kika tsaya kina tunani,ko shima salon gulamane kai kice bansan cinki ba ban san shanki ba,ballantana halin da kike ciki"
Zabura nayi na ɗan koma gefe,saboda na bashi damar shigs ɗaƙinnasa,danna tare bakin ƙofar,dama yana bayana tun ɗazu kenan?.
"Kayi haƙuri,kawai naga zan iyah shara ne shiyasa"
"Eh to kuma shi wanki da bazaki iyah ba sainace saikinyi koh?"
"Ahah ..uhmm...."
"ÆŠauresu ki sakasu gefe zan bayar a wanke,sannan kizo ki zauna akwai maganar da zamuyi"
Dumm naji kaina yayi,magana da goje? Uhm
ÆŠaure kayan nayi kaman yanda nace,kana naje gabansa na zauna,idon yana kallon tsakar É—aki,shikuma yana zaune a bakin katifa.
"Tunda yanzu kin warke saiki faÉ—amin dame dame kikeso na kayan abinci,kinsan dai bazan jure kullum in zan zubawa cikina abinci saina haÉ—o dake ba koh?"
ÆŠaga kai nayi alamar ehh,aikuwa naji wata tsawa kamar a sama.
"Nida kai nayi miki magana dabazaki buÉ—e bakinki ba,kodan nayi jinyarki saina zama abin wasanki kai?"
"Ahah kayi haƙuri,ehh na warke zan dunga girkin za'a iyah siyowa,itace ne saikuma kayan abinci,inda abubuwan aiki daban su tukunya"
Kaman mai aljanu jin abinda nace kuma sai ya maida muryarsa yanda take.
"Tom shikenan,zan aiko Tunga ya kawo in anjima,ba lallai yau na dawo ba,sannan inna tace na faɗamiki Yau zata dawo,munyi waya da ita da wayar ƙaninta"
Duk da a razane nake bansan lokacin da murmushi ya kubcemin ba.
"Dan Allah toh shikenan barinje na gyara mata ƙofar sosai"
Tashi nayi zan fitah da sauri,har na manta baice na tafi ba.
Saida naje bakin ƙofa naji maganar sa.
"Na sallameki ne?"
"Au ehh um toh"
Nafara shirin dawowa ina inda inda.
"Jeki kawai"
Yafaɗa yanayin wata ƙaramar tsuka.
Uhm kai kasani dai nafada ina yin sashennamu da saurina.
Chapter 32 · 0% Book details