Sashe 2
Rabon Kwado Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bazan iya tsayawa a gurin ba,ga zuciyata dake zafi hakan yasa nayi tafiyata.
Ina shigo layinmu na hango motar dazu a kusa da uncompleted building din dake layinmu,ban san lokacin da zuciya ta tiqoni ba na nufi motar dan ni kaina bansan idan naje mexanyi ba.
Ina xuwa nayi knocking glass din dan ba'a ganin na ciki.Nafi munti biyu a tsaye dan harna fara tunanin mai motar baya ciki kafin naga an fara sauke glass din qasa.
Saida na fara galla masa harara kafin na fara mgn da fada dan ya kaini bango.
Kai makaho ne da kana ganin ka fallatsawa mutum kwata bazaka iya tsayawa ka bashi hqr ba?ko an fada maka kudi haukane?aikin banxa kawai."nace tare da jan tsaki nayi hanyar gida.
Ina shiga soron gidanmu na fashe da kuka sannan na shiga.da ya fatima naci karo taci kwalliya xata fita ta riqeni.
"Me akai miki auta?fadawa kwata kikayi?"
Duk tmbyoyin da tamin ban amsa ba saima qara sautin kukan da nayi dan Ammina ta jiyo.
Ai kuwa saeda ta fito nayi mgn.
"Ba wani ne a mota ya fallatsamin kwata ba"
"Allah sarki yi hqr qila ma bai sani ba"ya fatima tace tana ciren hijabin.
Jin Ammi taqi mgn yasa na kuma fashewa da kuka😩.
Itadai ya fatima gaba tayi dan tasan halina sai Ammi ta rarrasheni xanyi shiru.
Dakinmu na shiga ya zainab sai bacci take,kanta na fada na cigaba da kukana har bacci ya dauke ni.
Sai magriba na tashi sannan Abbi ya dawo dan haka yana bani tsaraba na ware aka cigaba da hira dani.
Washegari nusaiba tazo itama daqar na kulata dan haka nace itace ta jamin aka zuban kwata.da yake tana da hqr har hqr ta vani sannan muka cigaba da hira.
Ana gobe xamu kama mkrnt na fito raka nusaiba naci karo da ya fatima da wannan mutumin da nayiwa rashin kunya ranar daya xuban kwata a hijabi.
Inaji nusaiba ta gaida shi ni kuwa na maka masa harara nayi gaba abina.
"Kai khadija meyasa baki gaida saurayin ya fatima ba?kinga baxata ji dadi ba"Nusaeba tace.
"Bazan gaida shi dinba,kuma insha allah bazata aureshi ba mugu kawai😏"
Kinsanshi ne?"
"Eh mn shine ya xuba min kwata ranar,bakiga na taho ba?zuwa nayi nayi masa rashin kunya"
Zaro ido nusaiba tayi"a ina kika ganshi?
A...mgnr ce ta maqale sakamakon hango yayan nusaiba da nayi yana nufo inda muke.
kallo na yake yana tahowa nima kuma na kasa dauke ido daga kansa ko meyasa?oho
Saida ya qaraso sannan na iya dauke idona daga kansa.Qasa nayi da idon ina wasa da azurfar dake hannuna.
"Yaya har kun dawo?"nusaiba tace da alama ba'asan ta fito ba.
"Kika qaramin mgn saina bigeki,wuce gida kafin ka Karya ki"
ya sadiq yace.
Sumsum nusaeba ta wuce ko sallamar da muka sabayi idan xan koma mkrnt yau ba muyi ba.
"Ke kuma baki iya gaisuwa ba koh?"najiyo muryarsa.
Har lkcn na kasa dago ido.
Ina yini?"na fada a hankali
"Bazan amsa tunda saida na roqa"
Murmushi kawai nayi dan wata kunyarsa nakeji ban san dalili ba.
Gobe sai scul ko?"naji yace
Daga masa kai kawai nayi alamar eh dan duk a takure nake kodan ban taba tsayuwa da wani haka ba,kuma ga kallona da yake yi duk da ina kallon qasa amma a jikina inajin kallona yake.
"To kimin alqawari xakiyi krt kuma kece Xakiyi first position wannan term din"
Bansan lkcn dana daga idona ba na kalleshi.gyada min kansa yayi alamar haka yake nufi.
"Nayi maka alqawari"nace
"Tom kije gida kinga anfara kiran magriba."
To nagode"nace tare da juyawa na nufi gida.
Ina idar da sallah ya fatima ta kama kunnena na dama.
"Dama jira nake ki idar yarinya,shine dazu kina ganin Abdul kikaqi gaidashi koh?har nusaiba ta gaidashi amma ke kikayi kaga koh?"
"To wai ba shine ya zubamin kwata ranar ba"na fada kamar xanyi kuka sbd har lkcn bata sakar min kunne ba.
"Sbd ya zuba miki kwata sai kiqi gaida shi koh?so kike yace yan gidannan bamu da tarbiyya?"
Aa kiyi hqr zan gaidashi gobe🙁"na fada danta sakarmin kunne na.
Daya fi miki yarinya"tace kafin ta sake ni.
Da dare kwatakwata bacci ya qaurace min,in banda tunanin yan maganganun da mukayi da ya sadiq ba abinda nake.To me hakan ke nufi?
Daqar bacci barawo ya dauke ni.
Washegari da safe Abbi ya lula dani mkrnt cike da kewar yan gida da kuma........
Guess who?
Duk wadda ta fada dai dai Mari uku
💙💙 RABON KWADO..💙💙
Na Er mutan ungogo💋💋
Luv u oll Readers❤❤❤
🅿11-🅿15
Haka na mayar da hankalina akan krt domin ina son na cika alqawarin dana daukarwa ya sadiq duk da damacan ina mai da hankali dan ana sakani sani farko farko a class dinmu,amma wannan term din saina qara jajircewa dan ganin na bawa kowa rata a class dinmu.
Da lokacin visiting tazo naji dadin ranar domin duka yanuwa sunxo wani abin dadinma harda nusaiba.
Haka mukaita zaga mkrnt ina nuna mata abubuwa da kuma mutanen da nake bata lbrnsu.
Da lokacin tapiyarsu yayi kuwa rasa inda xansa kaina nayi dan saida ya aisha taji haushina wai na fiya fitina indai ban nutsuba bazasu qara zuwa ba.
Dan dole na nutsu na goge hawayena amma xuciyata suya kawai takeyi.
Nusaiba ce ta kama hannu na mukai inda ba mutane sosai ta bani wata qaramar leda wai inji ya sadiq😀
Dama yananan?"nace da ita ina murmushi.
"Eh to da ina zaije?kullum ya dameni wai saina bashi lbrnki,yanxu bakiga shirin da mukeyi da shi ba"
"Allah sarki,kice ina gaidashi"
Hararar wasa tayi min"ni yar aikenki ce?"
To shikenan karki fada din"nace ina yin gaba.
Saida muka koma hostel na nutsu sannan na bude ledar.
Kayan zaqi ne akai wrapping a wata leda mai gyalli sai zobe mai kyau da qaramar takarda.
Takardar na bude ina murmushi.
Harna gama karantawa ban fahimci komai ba,kawai dai nasan akwai tunin alqawarin dana daukar masa.
To meyasa ya damu nayi krt?tmbyr danayi tayiwa kaina kenan amma ban samu amsa ba.
Kodai sona yake?Aa bazan yaudari kaina ba nasan ni ba mate dinsa bace,dan nasan bazai rasa budurwa ba.mutumin da ya gama service Yana neman aiki me xaiyi da Er Js 3.
Haka dai na gama tunani na na tattara kayan na ajiye.
Jiya muka dawo daga mkrnt amma allah allah nake naje gidansu nusaeba,abinda da sae ammi tayi ta mita banason fita kullum ni kenan a gida kamar daddawa amma yau nice washegarin da na dawo xan fita.
Dana tambayi ammi xanje gidansu nusaiba saida ta tmby me ake a gidan?nace kawai dai na gaji da zama ne xanje muyi hira.Dama su ya fatima tunda na dawo basa xama wai shirin bikinta ita da wannan mutumin.
A jiyanma dana dawo saida mukai da ita nace mata"wai ya fatima ki rasa wa xaki aura sai wannan mutumin?
Janyo ni tayi"wai dan allah me abdul yai miki kika tsaneshi haka?"
"Kawai mugu ne shiyasa,kuma dan yaga yana da kyau da mota shine yake wulaqanta mutane"
Bata cemin komai ba ta sake ni.
Dan haka ni ba wani shirin bikin da nakeyi dan a zuciyata haka nace dama muna mkrnt xa'ayi,dan yanxu har ya fatiman ma haushinta nakeji.
Na dade a bakin get din gidansu nusaeba na kasa shiga,ni kaina bansan dalili ba.
Ganin qaninta haidar yasa nace yaje yace mata taxo ina kiranta.
Bai dade ba ya dawo wai ya sadiq yace idan bazan shigo ba na koma.
Murmushi kawai nayi na samu wani dutse a qofar gidan na zauna dan na koma gida tmbyoyi xansha a wajen ammi.
Wasa nake da qasa ina rubutu ina gogewa naji tsayuwar mutum a kaina.
Ya sadiq ne tsaye ya xuban mayatattun idanunsa,ba shiri na maida kaina qasa dan gani nayi ya qara wani kyau.
"Gidan surukanki ne shiyasa kk kasa shiga koh?"
Ban dago ba saima qara boye fuskata da nayi cikin hijab.
"Ki tashi ki shiga ciki kinga kowa yazo wucewa saiya kallemin ke"
Maganganun nasa naita juyawa a kwakwalwata "a kalle masa ni?"
Maganarsa ce ta katsen tunani.
"Tunda bazaki shigo ba ki tafi gida"ya tada yana shigewa gida.
A hankali naja qafafuna nayi gida dan ji nake kamar ban kyauta masa ba.
Haka naje gida sukuku nacewa ammi nusaeban batanan.
Washegari inata zuba idon ganin nusaeba shiru har dare.
Tsahon kwana biyu ba nusaiba duk sai naji ba dadi dan nasan haka kawai bazata qi zuwa ba,dazu ammi har tmbyta tayi wai nusaeba nanan kuwa.
"Auta xo ga cingam din biki ki kae gidansu nusaiba"ammi tace tana lissafa cingam.
"Wlh dan gidansu nusaeba ne da bazan kai cingam din bikin mugu ba" na fada ina kallon qofar dakinmu dan nasan ya fatima ta jiyo ni.
Ai kuwa fitowa tayi nawo hanyar waje da gudu ina dariya.
"Ammi ki rabani da yarinyar nan wlh xan zane ta"ya fatima tace.
"Ke yanxu akan saurayin kike wannan abun?ke kuma bansan sakarci xo kije inda na aike ki"ammi tace.
"To Ammi kiyi mata mgn karta dake ni"
Jin anyi min shiru yasa na shigo ina rabe rabe.
Wullo min ledar cingam din tayi na dauka na fice,dama hanyar xuwa gidan nake nema,dan inaso naga nusaeba(nasan wata sai tace na fadi gsk🤣).
Ganin ya sadiq danayi da abokinsa yasa nayi sauri na shige gidan duk a zatona bai ganni ba.
Nusaeba na tarar dana wanke wanke ai kuwa tana ganina ta dafe ni.
"Ke kam nusaeba bakya girma,yanzu sae kin kayar da ita."najiyo muryar umma.
Har qasa na tsugunna na gaida ita na bata saqon kafin mu shige daki nida nusaeba.
"Wai ranar kikazo kikaqi shigowa"
"Ke sauri nake ammi tace karna dade"
"Ba wani nan,gashi kinja yaya yace ya qara ganin qafata a qofar gidanku saeya karya ni"
"Dan allah da gsk?"Nace jikina a sanyaye.
"to da baki ganni a gidan ba washe gari?kindai sanni da son labari"
"To meyasa ya hanaki zuwa?
"Oho masa,ni kinga na qagu ma ya fara aiki yayi aure yabar mana gidan"
Rass!!!naji gaba na ya fadi,amma na qaqalo wani murmushi kawai.
"Kinga tapiya zanyi kinga munata shirin biki"Nace ina miqewa.
"Kai dan allah yanxu baxaki bani lbrn ba"
Ina shigo layinmu na hango motar dazu a kusa da uncompleted building din dake layinmu,ban san lokacin da zuciya ta tiqoni ba na nufi motar dan ni kaina bansan idan naje mexanyi ba.
Ina xuwa nayi knocking glass din dan ba'a ganin na ciki.Nafi munti biyu a tsaye dan harna fara tunanin mai motar baya ciki kafin naga an fara sauke glass din qasa.
Saida na fara galla masa harara kafin na fara mgn da fada dan ya kaini bango.
Kai makaho ne da kana ganin ka fallatsawa mutum kwata bazaka iya tsayawa ka bashi hqr ba?ko an fada maka kudi haukane?aikin banxa kawai."nace tare da jan tsaki nayi hanyar gida.
Ina shiga soron gidanmu na fashe da kuka sannan na shiga.da ya fatima naci karo taci kwalliya xata fita ta riqeni.
"Me akai miki auta?fadawa kwata kikayi?"
Duk tmbyoyin da tamin ban amsa ba saima qara sautin kukan da nayi dan Ammina ta jiyo.
Ai kuwa saeda ta fito nayi mgn.
"Ba wani ne a mota ya fallatsamin kwata ba"
"Allah sarki yi hqr qila ma bai sani ba"ya fatima tace tana ciren hijabin.
Jin Ammi taqi mgn yasa na kuma fashewa da kuka😩.
Itadai ya fatima gaba tayi dan tasan halina sai Ammi ta rarrasheni xanyi shiru.
Dakinmu na shiga ya zainab sai bacci take,kanta na fada na cigaba da kukana har bacci ya dauke ni.
Sai magriba na tashi sannan Abbi ya dawo dan haka yana bani tsaraba na ware aka cigaba da hira dani.
Washegari nusaiba tazo itama daqar na kulata dan haka nace itace ta jamin aka zuban kwata.da yake tana da hqr har hqr ta vani sannan muka cigaba da hira.
Ana gobe xamu kama mkrnt na fito raka nusaiba naci karo da ya fatima da wannan mutumin da nayiwa rashin kunya ranar daya xuban kwata a hijabi.
Inaji nusaiba ta gaida shi ni kuwa na maka masa harara nayi gaba abina.
"Kai khadija meyasa baki gaida saurayin ya fatima ba?kinga baxata ji dadi ba"Nusaeba tace.
"Bazan gaida shi dinba,kuma insha allah bazata aureshi ba mugu kawai😏"
Kinsanshi ne?"
"Eh mn shine ya xuba min kwata ranar,bakiga na taho ba?zuwa nayi nayi masa rashin kunya"
Zaro ido nusaiba tayi"a ina kika ganshi?
A...mgnr ce ta maqale sakamakon hango yayan nusaiba da nayi yana nufo inda muke.
kallo na yake yana tahowa nima kuma na kasa dauke ido daga kansa ko meyasa?oho
Saida ya qaraso sannan na iya dauke idona daga kansa.Qasa nayi da idon ina wasa da azurfar dake hannuna.
"Yaya har kun dawo?"nusaiba tace da alama ba'asan ta fito ba.
"Kika qaramin mgn saina bigeki,wuce gida kafin ka Karya ki"
ya sadiq yace.
Sumsum nusaeba ta wuce ko sallamar da muka sabayi idan xan koma mkrnt yau ba muyi ba.
"Ke kuma baki iya gaisuwa ba koh?"najiyo muryarsa.
Har lkcn na kasa dago ido.
Ina yini?"na fada a hankali
"Bazan amsa tunda saida na roqa"
Murmushi kawai nayi dan wata kunyarsa nakeji ban san dalili ba.
Gobe sai scul ko?"naji yace
Daga masa kai kawai nayi alamar eh dan duk a takure nake kodan ban taba tsayuwa da wani haka ba,kuma ga kallona da yake yi duk da ina kallon qasa amma a jikina inajin kallona yake.
"To kimin alqawari xakiyi krt kuma kece Xakiyi first position wannan term din"
Bansan lkcn dana daga idona ba na kalleshi.gyada min kansa yayi alamar haka yake nufi.
"Nayi maka alqawari"nace
"Tom kije gida kinga anfara kiran magriba."
To nagode"nace tare da juyawa na nufi gida.
Ina idar da sallah ya fatima ta kama kunnena na dama.
"Dama jira nake ki idar yarinya,shine dazu kina ganin Abdul kikaqi gaidashi koh?har nusaiba ta gaidashi amma ke kikayi kaga koh?"
"To wai ba shine ya zubamin kwata ranar ba"na fada kamar xanyi kuka sbd har lkcn bata sakar min kunne ba.
"Sbd ya zuba miki kwata sai kiqi gaida shi koh?so kike yace yan gidannan bamu da tarbiyya?"
Aa kiyi hqr zan gaidashi gobe🙁"na fada danta sakarmin kunne na.
Daya fi miki yarinya"tace kafin ta sake ni.
Da dare kwatakwata bacci ya qaurace min,in banda tunanin yan maganganun da mukayi da ya sadiq ba abinda nake.To me hakan ke nufi?
Daqar bacci barawo ya dauke ni.
Washegari da safe Abbi ya lula dani mkrnt cike da kewar yan gida da kuma........
Guess who?
Duk wadda ta fada dai dai Mari uku
💙💙 RABON KWADO..💙💙
Na Er mutan ungogo💋💋
Luv u oll Readers❤❤❤
🅿11-🅿15
Haka na mayar da hankalina akan krt domin ina son na cika alqawarin dana daukarwa ya sadiq duk da damacan ina mai da hankali dan ana sakani sani farko farko a class dinmu,amma wannan term din saina qara jajircewa dan ganin na bawa kowa rata a class dinmu.
Da lokacin visiting tazo naji dadin ranar domin duka yanuwa sunxo wani abin dadinma harda nusaiba.
Haka mukaita zaga mkrnt ina nuna mata abubuwa da kuma mutanen da nake bata lbrnsu.
Da lokacin tapiyarsu yayi kuwa rasa inda xansa kaina nayi dan saida ya aisha taji haushina wai na fiya fitina indai ban nutsuba bazasu qara zuwa ba.
Dan dole na nutsu na goge hawayena amma xuciyata suya kawai takeyi.
Nusaiba ce ta kama hannu na mukai inda ba mutane sosai ta bani wata qaramar leda wai inji ya sadiq😀
Dama yananan?"nace da ita ina murmushi.
"Eh to da ina zaije?kullum ya dameni wai saina bashi lbrnki,yanxu bakiga shirin da mukeyi da shi ba"
"Allah sarki,kice ina gaidashi"
Hararar wasa tayi min"ni yar aikenki ce?"
To shikenan karki fada din"nace ina yin gaba.
Saida muka koma hostel na nutsu sannan na bude ledar.
Kayan zaqi ne akai wrapping a wata leda mai gyalli sai zobe mai kyau da qaramar takarda.
Takardar na bude ina murmushi.
Harna gama karantawa ban fahimci komai ba,kawai dai nasan akwai tunin alqawarin dana daukar masa.
To meyasa ya damu nayi krt?tmbyr danayi tayiwa kaina kenan amma ban samu amsa ba.
Kodai sona yake?Aa bazan yaudari kaina ba nasan ni ba mate dinsa bace,dan nasan bazai rasa budurwa ba.mutumin da ya gama service Yana neman aiki me xaiyi da Er Js 3.
Haka dai na gama tunani na na tattara kayan na ajiye.
Jiya muka dawo daga mkrnt amma allah allah nake naje gidansu nusaeba,abinda da sae ammi tayi ta mita banason fita kullum ni kenan a gida kamar daddawa amma yau nice washegarin da na dawo xan fita.
Dana tambayi ammi xanje gidansu nusaiba saida ta tmby me ake a gidan?nace kawai dai na gaji da zama ne xanje muyi hira.Dama su ya fatima tunda na dawo basa xama wai shirin bikinta ita da wannan mutumin.
A jiyanma dana dawo saida mukai da ita nace mata"wai ya fatima ki rasa wa xaki aura sai wannan mutumin?
Janyo ni tayi"wai dan allah me abdul yai miki kika tsaneshi haka?"
"Kawai mugu ne shiyasa,kuma dan yaga yana da kyau da mota shine yake wulaqanta mutane"
Bata cemin komai ba ta sake ni.
Dan haka ni ba wani shirin bikin da nakeyi dan a zuciyata haka nace dama muna mkrnt xa'ayi,dan yanxu har ya fatiman ma haushinta nakeji.
Na dade a bakin get din gidansu nusaeba na kasa shiga,ni kaina bansan dalili ba.
Ganin qaninta haidar yasa nace yaje yace mata taxo ina kiranta.
Bai dade ba ya dawo wai ya sadiq yace idan bazan shigo ba na koma.
Murmushi kawai nayi na samu wani dutse a qofar gidan na zauna dan na koma gida tmbyoyi xansha a wajen ammi.
Wasa nake da qasa ina rubutu ina gogewa naji tsayuwar mutum a kaina.
Ya sadiq ne tsaye ya xuban mayatattun idanunsa,ba shiri na maida kaina qasa dan gani nayi ya qara wani kyau.
"Gidan surukanki ne shiyasa kk kasa shiga koh?"
Ban dago ba saima qara boye fuskata da nayi cikin hijab.
"Ki tashi ki shiga ciki kinga kowa yazo wucewa saiya kallemin ke"
Maganganun nasa naita juyawa a kwakwalwata "a kalle masa ni?"
Maganarsa ce ta katsen tunani.
"Tunda bazaki shigo ba ki tafi gida"ya tada yana shigewa gida.
A hankali naja qafafuna nayi gida dan ji nake kamar ban kyauta masa ba.
Haka naje gida sukuku nacewa ammi nusaeban batanan.
Washegari inata zuba idon ganin nusaeba shiru har dare.
Tsahon kwana biyu ba nusaiba duk sai naji ba dadi dan nasan haka kawai bazata qi zuwa ba,dazu ammi har tmbyta tayi wai nusaeba nanan kuwa.
"Auta xo ga cingam din biki ki kae gidansu nusaiba"ammi tace tana lissafa cingam.
"Wlh dan gidansu nusaeba ne da bazan kai cingam din bikin mugu ba" na fada ina kallon qofar dakinmu dan nasan ya fatima ta jiyo ni.
Ai kuwa fitowa tayi nawo hanyar waje da gudu ina dariya.
"Ammi ki rabani da yarinyar nan wlh xan zane ta"ya fatima tace.
"Ke yanxu akan saurayin kike wannan abun?ke kuma bansan sakarci xo kije inda na aike ki"ammi tace.
"To Ammi kiyi mata mgn karta dake ni"
Jin anyi min shiru yasa na shigo ina rabe rabe.
Wullo min ledar cingam din tayi na dauka na fice,dama hanyar xuwa gidan nake nema,dan inaso naga nusaeba(nasan wata sai tace na fadi gsk🤣).
Ganin ya sadiq danayi da abokinsa yasa nayi sauri na shige gidan duk a zatona bai ganni ba.
Nusaeba na tarar dana wanke wanke ai kuwa tana ganina ta dafe ni.
"Ke kam nusaeba bakya girma,yanzu sae kin kayar da ita."najiyo muryar umma.
Har qasa na tsugunna na gaida ita na bata saqon kafin mu shige daki nida nusaeba.
"Wai ranar kikazo kikaqi shigowa"
"Ke sauri nake ammi tace karna dade"
"Ba wani nan,gashi kinja yaya yace ya qara ganin qafata a qofar gidanku saeya karya ni"
"Dan allah da gsk?"Nace jikina a sanyaye.
"to da baki ganni a gidan ba washe gari?kindai sanni da son labari"
"To meyasa ya hanaki zuwa?
"Oho masa,ni kinga na qagu ma ya fara aiki yayi aure yabar mana gidan"
Rass!!!naji gaba na ya fadi,amma na qaqalo wani murmushi kawai.
"Kinga tapiya zanyi kinga munata shirin biki"Nace ina miqewa.
"Kai dan allah yanxu baxaki bani lbrn ba"