Sashe 2
Matar Uncle Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Sai shegen girman kai wlh ki rage izzar nan tunda kede ba saraki ba ce bare a ce bazata dainu ba “Kin kulata Ayda tayi saboda suna gab da motar da kansa ya fito tare zagayowa ya bude mata daga kallon gayen kaga jinin sarauta saidai akwai nuna karyar kudi a yayinda jawahid ta shiga gidan baya ta na cewa.
“Saraki manya Waziri yau kune a kasar’”Murmushin ya yi ya na bin Ayda da mayataccen kallo mai Cike da so da kauna Wanda ta Kauda Kai ta na yatsina fuska ya ce “saukata kasar jiya na amsa kiran gimbiya kinsan ko daga Chan maracco ta ke son gani na dole na bar kome nake ta taho”
“Haba Babe duba time fa driver na jira na a school salon ya tafi Ummy tayi fad’a “Sorry gimbiya tuba na ke kinsan na dawo ne Cike da kewar ki kinga ko dole na tsaya na karewa kyakyawar fuskar nan kallo “
“tab’e Baki tayi ta na kauda kai a ranta ta ce shegen zuba kamar radio da wani hancinsa kamar na bunsuru”Jan motar Yayi Yayinda ta juya ta kalli jawahid ta ce.
“Don Allah mu wuce gidanmu tare nasan Mamy ba ta dawo ba su aunty hasana kuma hidimar biki suna gyaran jiki na San waccen alhudu-hudun kuma nasan bata missing lectures ko d’aya yau sai an ganta ”
Dariya Jawahid tayi tare da cewa”kin Raina mufedah wlh ba zan biki ba gaskiya Abbana na gida fad’a zaiyi na fada musu yau ai da wuri zan dawo ki Bari next time na je”
“Ta na had’e fuska ta ce “naji zan Rama kema sai ranar da momy bata nan Abba baya nan Kice na rakaki “
”Toh ai babe idan munje ba tafiya zanyi ba zan iya jiranki ma har su ummyn su dawo kinsan nayi kewarki da yawa “”Cewar waziri da ya tsoma musu baki jawahid ta ce”shikenanma waziri ka fansheni”Ayda ta ce “Driver ai zai karasa da ni gida”Ai gidan zan biku “ya fad’a Kai tsaye ta gefe ta Galla mai harara ba tare da ya gani ba.
Alqalam university Kai tsaye suka nufa inda suka saba parking ya tsaya Wanda nan ta hango driver ta sa Yayi parking nesa dashi kafin suyi sallama da niyyar zasuyi waya suka nufi driver suna hira ba tare da ta Bari ya ga an sauke ta ba inda jawahid ke cewa”Nima driver ki zai saukeni gida yau ban fito da mota ba”.
Koda isarsu gida bayan sauke jawahid a gidansu kasantuwar ba nisa tsakaninsu Chan ta samu waziri harabar gidan bata biye masa ya jata da hira ba ta sallamesa don a gajiye ta ke.
Sosai na karewa gidan kallo ya had’u ba k’arya tankamamen gida ne mai matukar girman gaske sai shukoki da ke matukar daukar hankali alamun suna matuk’ar Shan gyara,komai ya yi kama da na manyan masu kud’i domin bene ma kanshi hawa biyu ne sai wani tsararren flat part da ke gefen hagu kusan sai ince ni ya ma fi yimun kyau da d’aukar ido domin wasu irin kawatatun shukokine suke zagaye da gidan ga fentin part din kanshi kamar yau akayi sa decoration din b’angaren ma na musamman ne domin sai a tsirarrun gidajen masu kud’i aka fiya samun irin hakan domin wasu irin glass-glass din da aka kawata part dinma kad’ai abun kallo ne.
ba Wanda ta samu a palour hakan ya sanyata saurin haurawa sama tare da bude bedroom Dinsu ta shige,
rage Kayan jikinta tayi tare da fad’awa toilet ta yi Wanka salla tayi tare da sanya kananun Kaya masu taushi kasantuwar yanayin zafin garin alamun hadari ne dukda sanyin ac da ke ratsata.
hayewa gado tayi tare da janyo wayarta ganin missed call Din yaya Faruq sama da ashirin ne kuma duk kusan tattare saboda ta bar wayar silent ya sanya gabanta fad’uwa idan ka ga ya na mata irin wannan kiran to da dalili ga bacci ne a idonta dukda yamma ta yi sosai,
kashe wayar tayi tare da tashi ta sanyawa dak’inta key ta san zai iya biyota nan d’inma ba tsira tayi ba ga ba kowa a gidan ga shi bata San ta’kamaimai laifin da tayi masa ba don tasan tabbas kirannan idan tayi laifi yake yi mata.
k’ara gudun ac tayi kafin ta koma gado ta kwanta ta na kashe wayarta gaba d’aya don gwara tayi bacci koma me zai mata ya mata bayan ta huta.
Ba jimawa bacci me dadi ya dauk’eta Wanda barcinta har ya fara nisa cikin bacci take jin buga k’ofar da karfi Cike da masifa ta tsinkayi muryarsa da cewa “wallahi Ko ki bude kofar da kanki ko kuma in b’allata da kaina na shigo na ci uwarki second hamsin na Baki………..✍🏾
Toh fa ya kukaji salon🧐mu hade a comment section idan na ji comment din da ya gamsheni gobe zaku jini Insha Allah idan na jiku shiru Nima zaku jini shiru🙅🏾♀️
07026166536 domin Neman Karin bayani ko shiga group🪱
Share fisabillah🦇🦅
_*Miss hajo ce*_✍🏾
♠️♣️ *MATAR UNCLE*♣️♠️
```MALLAKAR```
*HAJARA L SADEQ*
(Miss Hajo✍🏾)
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*Marubuciyar*
👇🏾
Auren wata Tara
Ni da yaya arman
Khadijatul sabren
Ribar so
Najmat abiy
Mata tace
Komai mukaddari ne
And now
*MATAR UNCLE*
🅿️……………………….*2*
Cikin Dakiya Ayda ta tashi duk da yanda gabanta ke faduwa hakan bai hanata aro jarumta ba wajen hade fuska tamau ta na mikewa ta nufi kofar tare da budewa saurin ja baya tayi ganin yanda ya fado dak’in kamar wani zaki
“Da uban waye kike waya jiya har karfe d’ayan dare?Daram gabanta ya bada cikin zuciyarta tace “Toh amma waya fada masa bayan jiyan da nake waya Banga missed call dinsa ba wata zuciyar ta bata amsa da cewa “tabbas sauya layi ya yi ya dinga kiranta don lokacin ta ga wata number na kiranta!
“Zan daukeki da Mari Ina miki magana kin tsareni da wannan shaggun idanun naki kamar na mage “ya fad’a a zafafe!
kamar mai Shirin fashewa da kuka ta ce “Yaya faruq Jawahid ce fa ba wani ba”
Kallon Kin Raina mun hankali ya yi tare da nufota gadan gadan da niyyar dauketa da Mari ta yi baya tare da fadawa gado Tana kife kanta da gwuiwa ta sa kuka don tasan yau me rabata da shi sai Allah tunda ummi bata nan ba kowa gidan dole ta lallab’asa su rabu lafiya cikin kuka ta ce “Don Allah yaya faruq karka dakeni ka ga ummi ta hanaka dukana”
Cike da masifa ya ce”bani wayar ki”bata San sanda ta d’ago ba tare da zazzare ido alamun rashin gaskiya ta ce.
“Wayata kuma yay…..”Eh wayarki don ubanki ba ni kafin na sauya maki kamanni cikin kakkarwa ta janyo wayar tare da mik’a masa ya amsa,
ganin hankalinshi na kan wayar ya sanyata saurin rugawa a guje tayi waje da gudu daidai lokacin ummi na shigowa,
Da gudu ta ruga tare da boyewa bayan ummi Tana sauke wahalalliyar ajiyar zuciya”Lafiya Ayda meya faru na ganki haka a firgice?”
Kafin Ayda ta bata amsa ta hango faruq na saukowa daga sama cikin bala’i fuskarsa har ta sauya Kala ya nufosu ummi ta kareta ta na had’e fuska tamau ta ce “me kuma ta maka yau ?Bai ba ummi amsa ba sai mik’a mata wayar ya yi tare da cewa,
“Bud’e securityn munafuka saboda tsabar rashin gaskiya shiyasa kika sauya bud’e Toh kafin wlh na sassauya miki halittu yanda ko naman daji bazasuyi sha’awar cin ki ba”
Kuka ta sanya tare da makalewa bayan ummi ta ce”Don Allah yaya faruq kayi hakuri ni wlh ba da saurayi nake waya ba na fad’a maka jawahid ce “
“Uwar jawahid don uwarki D’an iska zaki maidani ki shafe sama da awa d’aya da rabi kina waya kice mun wata jawahid don kin d’aukeni sakarai ”
“Faruq faruq faruq”Sau nawa na Kira sunanka?
Ummi ta fada da ranta ya soma b’aci don ta gaji da masifar faruq Akan Ayda “ummi don Allah karki shiga maganar nan ki barni da ita’”
Anki a barka da itan nace anki a barka da ita ko haihuwarta kayi”ko ko auren ta ka ke?.
“Ni mijinta ne tunda ba ta da wani miji a duniya bayan ni don haka dole in dinga bibiyar rayuwarta wlh ummi yarinyar nan cin amanata take samari take tarawa kawai ta maidani sakarai tun farko sai da na ce ban yarda Ayda ta shiga university ba amma kuka nace nace a bani matata na sakata karatun bayan munyi aure amma kuka k’iya to bazan yarda ba sai ta bar school dinnnan tunda duk ita ta ke Kara bude mata ido kuma ni kawai na gaji a azo a d’aura mana aure kawai!
Wani banzan kallo ummi ta watsa masa tare da cewa”da Allah wuce ka ba mutane guri marar kunyar gida kawai ai dai ka Bari a d’aura tukwana ta zama matar taka da Baka da aiki kullum sai fad’a da mace Akan saurayi kaji kunya wlh har bakasan yanda zakayi ka janye hankalinta ta daina kule kulen samarin,ko angaya maka wannan hayayagar da zafin ran da kake shi zaisa ta daina abunda ta ke wai ma haka ake soyayya!faruq?
“toh idan Baka sani ba ka sani ita mace tamkar kid’a ce bazata tab’a Baka dad’in sauti ba sai ka San yanda ake buga kid’anta a kwakwalwar zuciyarta mace bata son hantara da kyara daga wajen masoyinta bare har akai ga duka Faruq kar ka fusatani na yi abunda ranka zai b’aci wlh ka k’ara Kai hannunka jikin Ayda da niyyar duka ko kaine Autan maza bazaka aure ta ba tunda kai na lura kullum abunka k’ara gaba yake ba baya ba “
“Saraki manya Waziri yau kune a kasar’”Murmushin ya yi ya na bin Ayda da mayataccen kallo mai Cike da so da kauna Wanda ta Kauda Kai ta na yatsina fuska ya ce “saukata kasar jiya na amsa kiran gimbiya kinsan ko daga Chan maracco ta ke son gani na dole na bar kome nake ta taho”
“Haba Babe duba time fa driver na jira na a school salon ya tafi Ummy tayi fad’a “Sorry gimbiya tuba na ke kinsan na dawo ne Cike da kewar ki kinga ko dole na tsaya na karewa kyakyawar fuskar nan kallo “
“tab’e Baki tayi ta na kauda kai a ranta ta ce shegen zuba kamar radio da wani hancinsa kamar na bunsuru”Jan motar Yayi Yayinda ta juya ta kalli jawahid ta ce.
“Don Allah mu wuce gidanmu tare nasan Mamy ba ta dawo ba su aunty hasana kuma hidimar biki suna gyaran jiki na San waccen alhudu-hudun kuma nasan bata missing lectures ko d’aya yau sai an ganta ”
Dariya Jawahid tayi tare da cewa”kin Raina mufedah wlh ba zan biki ba gaskiya Abbana na gida fad’a zaiyi na fada musu yau ai da wuri zan dawo ki Bari next time na je”
“Ta na had’e fuska ta ce “naji zan Rama kema sai ranar da momy bata nan Abba baya nan Kice na rakaki “
”Toh ai babe idan munje ba tafiya zanyi ba zan iya jiranki ma har su ummyn su dawo kinsan nayi kewarki da yawa “”Cewar waziri da ya tsoma musu baki jawahid ta ce”shikenanma waziri ka fansheni”Ayda ta ce “Driver ai zai karasa da ni gida”Ai gidan zan biku “ya fad’a Kai tsaye ta gefe ta Galla mai harara ba tare da ya gani ba.
Alqalam university Kai tsaye suka nufa inda suka saba parking ya tsaya Wanda nan ta hango driver ta sa Yayi parking nesa dashi kafin suyi sallama da niyyar zasuyi waya suka nufi driver suna hira ba tare da ta Bari ya ga an sauke ta ba inda jawahid ke cewa”Nima driver ki zai saukeni gida yau ban fito da mota ba”.
Koda isarsu gida bayan sauke jawahid a gidansu kasantuwar ba nisa tsakaninsu Chan ta samu waziri harabar gidan bata biye masa ya jata da hira ba ta sallamesa don a gajiye ta ke.
Sosai na karewa gidan kallo ya had’u ba k’arya tankamamen gida ne mai matukar girman gaske sai shukoki da ke matukar daukar hankali alamun suna matuk’ar Shan gyara,komai ya yi kama da na manyan masu kud’i domin bene ma kanshi hawa biyu ne sai wani tsararren flat part da ke gefen hagu kusan sai ince ni ya ma fi yimun kyau da d’aukar ido domin wasu irin kawatatun shukokine suke zagaye da gidan ga fentin part din kanshi kamar yau akayi sa decoration din b’angaren ma na musamman ne domin sai a tsirarrun gidajen masu kud’i aka fiya samun irin hakan domin wasu irin glass-glass din da aka kawata part dinma kad’ai abun kallo ne.
ba Wanda ta samu a palour hakan ya sanyata saurin haurawa sama tare da bude bedroom Dinsu ta shige,
rage Kayan jikinta tayi tare da fad’awa toilet ta yi Wanka salla tayi tare da sanya kananun Kaya masu taushi kasantuwar yanayin zafin garin alamun hadari ne dukda sanyin ac da ke ratsata.
hayewa gado tayi tare da janyo wayarta ganin missed call Din yaya Faruq sama da ashirin ne kuma duk kusan tattare saboda ta bar wayar silent ya sanya gabanta fad’uwa idan ka ga ya na mata irin wannan kiran to da dalili ga bacci ne a idonta dukda yamma ta yi sosai,
kashe wayar tayi tare da tashi ta sanyawa dak’inta key ta san zai iya biyota nan d’inma ba tsira tayi ba ga ba kowa a gidan ga shi bata San ta’kamaimai laifin da tayi masa ba don tasan tabbas kirannan idan tayi laifi yake yi mata.
k’ara gudun ac tayi kafin ta koma gado ta kwanta ta na kashe wayarta gaba d’aya don gwara tayi bacci koma me zai mata ya mata bayan ta huta.
Ba jimawa bacci me dadi ya dauk’eta Wanda barcinta har ya fara nisa cikin bacci take jin buga k’ofar da karfi Cike da masifa ta tsinkayi muryarsa da cewa “wallahi Ko ki bude kofar da kanki ko kuma in b’allata da kaina na shigo na ci uwarki second hamsin na Baki………..✍🏾
Toh fa ya kukaji salon🧐mu hade a comment section idan na ji comment din da ya gamsheni gobe zaku jini Insha Allah idan na jiku shiru Nima zaku jini shiru🙅🏾♀️
07026166536 domin Neman Karin bayani ko shiga group🪱
Share fisabillah🦇🦅
_*Miss hajo ce*_✍🏾
♠️♣️ *MATAR UNCLE*♣️♠️
```MALLAKAR```
*HAJARA L SADEQ*
(Miss Hajo✍🏾)
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*Marubuciyar*
👇🏾
Auren wata Tara
Ni da yaya arman
Khadijatul sabren
Ribar so
Najmat abiy
Mata tace
Komai mukaddari ne
And now
*MATAR UNCLE*
🅿️……………………….*2*
Cikin Dakiya Ayda ta tashi duk da yanda gabanta ke faduwa hakan bai hanata aro jarumta ba wajen hade fuska tamau ta na mikewa ta nufi kofar tare da budewa saurin ja baya tayi ganin yanda ya fado dak’in kamar wani zaki
“Da uban waye kike waya jiya har karfe d’ayan dare?Daram gabanta ya bada cikin zuciyarta tace “Toh amma waya fada masa bayan jiyan da nake waya Banga missed call dinsa ba wata zuciyar ta bata amsa da cewa “tabbas sauya layi ya yi ya dinga kiranta don lokacin ta ga wata number na kiranta!
“Zan daukeki da Mari Ina miki magana kin tsareni da wannan shaggun idanun naki kamar na mage “ya fad’a a zafafe!
kamar mai Shirin fashewa da kuka ta ce “Yaya faruq Jawahid ce fa ba wani ba”
Kallon Kin Raina mun hankali ya yi tare da nufota gadan gadan da niyyar dauketa da Mari ta yi baya tare da fadawa gado Tana kife kanta da gwuiwa ta sa kuka don tasan yau me rabata da shi sai Allah tunda ummi bata nan ba kowa gidan dole ta lallab’asa su rabu lafiya cikin kuka ta ce “Don Allah yaya faruq karka dakeni ka ga ummi ta hanaka dukana”
Cike da masifa ya ce”bani wayar ki”bata San sanda ta d’ago ba tare da zazzare ido alamun rashin gaskiya ta ce.
“Wayata kuma yay…..”Eh wayarki don ubanki ba ni kafin na sauya maki kamanni cikin kakkarwa ta janyo wayar tare da mik’a masa ya amsa,
ganin hankalinshi na kan wayar ya sanyata saurin rugawa a guje tayi waje da gudu daidai lokacin ummi na shigowa,
Da gudu ta ruga tare da boyewa bayan ummi Tana sauke wahalalliyar ajiyar zuciya”Lafiya Ayda meya faru na ganki haka a firgice?”
Kafin Ayda ta bata amsa ta hango faruq na saukowa daga sama cikin bala’i fuskarsa har ta sauya Kala ya nufosu ummi ta kareta ta na had’e fuska tamau ta ce “me kuma ta maka yau ?Bai ba ummi amsa ba sai mik’a mata wayar ya yi tare da cewa,
“Bud’e securityn munafuka saboda tsabar rashin gaskiya shiyasa kika sauya bud’e Toh kafin wlh na sassauya miki halittu yanda ko naman daji bazasuyi sha’awar cin ki ba”
Kuka ta sanya tare da makalewa bayan ummi ta ce”Don Allah yaya faruq kayi hakuri ni wlh ba da saurayi nake waya ba na fad’a maka jawahid ce “
“Uwar jawahid don uwarki D’an iska zaki maidani ki shafe sama da awa d’aya da rabi kina waya kice mun wata jawahid don kin d’aukeni sakarai ”
“Faruq faruq faruq”Sau nawa na Kira sunanka?
Ummi ta fada da ranta ya soma b’aci don ta gaji da masifar faruq Akan Ayda “ummi don Allah karki shiga maganar nan ki barni da ita’”
Anki a barka da itan nace anki a barka da ita ko haihuwarta kayi”ko ko auren ta ka ke?.
“Ni mijinta ne tunda ba ta da wani miji a duniya bayan ni don haka dole in dinga bibiyar rayuwarta wlh ummi yarinyar nan cin amanata take samari take tarawa kawai ta maidani sakarai tun farko sai da na ce ban yarda Ayda ta shiga university ba amma kuka nace nace a bani matata na sakata karatun bayan munyi aure amma kuka k’iya to bazan yarda ba sai ta bar school dinnnan tunda duk ita ta ke Kara bude mata ido kuma ni kawai na gaji a azo a d’aura mana aure kawai!
Wani banzan kallo ummi ta watsa masa tare da cewa”da Allah wuce ka ba mutane guri marar kunyar gida kawai ai dai ka Bari a d’aura tukwana ta zama matar taka da Baka da aiki kullum sai fad’a da mace Akan saurayi kaji kunya wlh har bakasan yanda zakayi ka janye hankalinta ta daina kule kulen samarin,ko angaya maka wannan hayayagar da zafin ran da kake shi zaisa ta daina abunda ta ke wai ma haka ake soyayya!faruq?
“toh idan Baka sani ba ka sani ita mace tamkar kid’a ce bazata tab’a Baka dad’in sauti ba sai ka San yanda ake buga kid’anta a kwakwalwar zuciyarta mace bata son hantara da kyara daga wajen masoyinta bare har akai ga duka Faruq kar ka fusatani na yi abunda ranka zai b’aci wlh ka k’ara Kai hannunka jikin Ayda da niyyar duka ko kaine Autan maza bazaka aure ta ba tunda kai na lura kullum abunka k’ara gaba yake ba baya ba “