← Book details Matar Uncle Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 27

Sashe 18

Matar Uncle Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“to ai Ayda tun farko laifinki ne ke da kika amsa gaban mahaifinsa”Ayda na Jan tsaki ta ce”idan na San hakane har na amsa wlh banyi tunanin abunda zasuyi ba ni yanzu ku bani solution ta ya zan sillewa Auren nan”

jawahid ta ce”na tambayeki mana Ayda?ta ce Ina jinki”bakya son faruq”Saida ta ja numfashi kafin ta sauke ajiyar zuciya ta ce”wlh Ina sonsa Jawahid amma sharrin da Yayi mana da abunda ya faru bantabajin ragin soyayyar da nake masa ba amma yanzu wlh ta ragu kuma na fara tsoron aurensa”

“Hmmm ai tun wuri abunda ake jiye maki saida wuri ya Kure kawai kiyi Adduar zabin alkhairi muma mu tayani”

Khairat ta ce “idan kuma kinga da gaske auren za ayi kawai sai ki gudu wlh bayan lokacin Auren ki dawo tunda ga ma wajen momynki Lagos kuma kinga bata son Auren tsaf za ta Goya maki baya”

“Ayda ta ce”Allah kiyaye na tafi agolanci kawai sai na bita gidan mijinta ni ga Marar kishin Kai ni bantaba zuwa ba kuma bazanje ba yaransa har su Raina ni”

Ruky ta ce”wannan ba shawara ba ce khairat ba inda zata ta hakura tayi aurenta kawai ni shawarar da zan bata tunda ta na sonsa ya na sonta karkisa wata damuwa a ranki”

Jawahid ta ce”Baki fahimtar matsalar Auren ne ruky”ta ce”ta barwa Allah zab’i”

Ayda ta ce”shikenan fa ya aureni na zama kulle samari na na rabu da su ba damar kula wasu ba shakatawa ba komai shi fa ko irin fita dakai yawo bayayi Ina waje ma ba ya fitar da ni ko inaga na auresa shikenan tawa ta kare wlh Bazaiyu ba ni tsari na sai na gama karatu ta fada ta na lafta uban tagumi “

“jawahid ta ce “kiyi Adduar zabin alkhairi kawai ki cire komai a ranki sai kuma ki Kama kanki a wajensa”

ubaida ta ce “ni fa abunda yafi damuna wlh faruq ya auri Ayda rabamu zaiyi da ita tunda kinga sharrin da aka mana wajensa ko ba shi ba ma daman baya son tarenmu”

Khairat ta ce”kede Bari wlh ga munshaku kamar y’an uwa kuma Allah be isa ba don dole muje gidan ko ya hanata fita mu sai munje”

”Ayda ta ce”karku wani damu Yama isa ai wlh me rabamu se mutuwa ai bama zai fara ba mun taso tun j s s one d’in shekara bakwai muna tare Banda jawahid da tun bamu mallaki hankalin kanmu ba muke tare ai abunda Bazaiyu ba ne”

Ruky ta ce”kunsan daman ba nace karkuje birthday d’in wannan ba wlh nasan shine aka fad’a masa “ Ubaida ta ce”

“Toh meye a ciki kuma ma to shima a sa alamar tambaya a Kansa ya na ma zuwa hotel din kenan tunda har ya ganmu kuma fa ko 10 minutes bamuyi ba muka fito ina basa gift dinsa nabar wajen ko hoto ba mu Bari anyi ba muka tafi “ Jawahid ta ce”

“mudaman a mota ma muka jiraku keda Ayda ne kuka shiga kinsan ba na zuwa irin wajajen nan dady sai ya kusa kasheni ya ce ina son b’ata masa suna ranar da muka je hotunan nan ran muka Kama d’aki yini guda wata salla saida na yi jinya da ya gano“

Ayda ta ce “Toh muma zuwan muke da zakiyi wannan ai gwara ni ma akanku don ko lokacin ku kad’ai kukayi abunku ba da ni ba “

Jawahid ta ce”ai dai duk inda zamu tare muke zuwa ba wani Harkan banza muke ba kuma wlh ya sake mana sharri ya ce mana y’an iska manta alak’ar da ke tsakaninku zamuyi muyi maganinsa”

Ruky ta ce”tsaya Malama da Baku bada k’ofa ba an zargeku don haka maganar nan ta wuce mu koma maganar exams don ita ke d’aga mun hankali”

Ayda ta ce”ke ta ke d’agawa hankali ko ni da bansan tsiyar komai ba a semester nan lectures din da nayi attending ba tayi 5 ba suma d’in ba sauraron lectures din na ke ba.
Ubaida ta ce”ni wlh tsoroma nake kar a koremu mu shiga ukku C’0 sunyi mana yawa 4 garan fa a first semester farkon shigowarmu lokacin ma ba laifi muna shiga Aji Ina ga yanzu ke gwara ke ma Ayda me biyu”
Khairat ta ce”idan munga Kaya sunyi mana yawa kawai mu samu dabarar da mukayiwa iyayenmu su ciremu mu koma ma Maryam Abatcha kano kawai don Alllah garin nan duk ya fita a Raina”

Ayda na tura Baki gaba ta ce”ni nasan Ko Ina gaban ummi ba inda zata kaini Duka Matan a gabanta suke karatu ba ta yarda Ana zuwa wani garin kuma wlh Baku isa ba ku barni kawai mu hakura next mu dage mu gygyara Wanda garemu “

“kafin su koma cigaba da tattaunawa Akan exams sai da ta daidaici lokacin tashi suka koma sch a motar jawahid.

Ba jimawa driver ya ja suka nufa gida a parking space ta ci karo da motar faruq fake ya hard’e kafafu jikin motar ya na Danna waya hakanan taji gabanta ya fad’i “to me ya zo ya ce mata?………✍️

07026166536 domin Neman Karin bayani

*KWALISA!!!!!KWALISA!!!!!KWALISA*
*INA MATA Y’AN KWALISA MASU JI DA GAYU HAFSAT COLLECTION TA MUSAMMAN CE WAJEN ZAKULO MABANBANTA HADAD’D’UN KAYA NA GAYU TUNDAGA KAN NA SAKAWA,KITCHEN, K’AWATA D’AKI DA SAURANSU ADO DA KWALLIYA SHINE CIKAR MACEN DA TASAN KANTA BA TA WASA DA KAYAN GAYU MUSAMMAN DA SUKA KASANCE NA DABAN DAGA FITACCIYAR Y’AR KASUWAR DA TA YI FICE A WANNAN FANNIN UWA UBA GA SAUKIN FARASHI BABU INDA BA TA AIKA KAYAN TA KUMA CIKIN YARDA DA AMINCI KAR KI BARI A BAKI LABARI Y’AR UWA DOMIN DUK MACEN DA TASAN KANTA BA TA WUCE HAFSAT COLLECTION BA TA NA SAYAR DA,
ATAMFA
LACE
CAMPY GWON
BAGS
SHOES
KITCHEN VTENSILS AND MORE
KAI TSAYE ZA KU SAMETA A ADDRESS D’INTA KAMAR HAKA
*KANO STATE KURNA LAYIN KUNYA STORE*
KO KUMA NUMBER WAYARTA KAMAR HAKA
*08131850861*

_*Miss hajo ce_*🤙🏿

♠️♣️ *MATAR UNCLE* ♣️♠️

```MALLAKAR```

*HAJARA L SADEQ*
Miss Hajo✍🏾

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*Marubuciyar*
👇🏾
Auren wata Tara
Ni da yaya arman
Khadijatul sabren
Ribar so
Najmat abiy
Mata tace
Komai mukaddari ne
And now
MATAR UNCLE

*KWALISA!!!!!KWALISA!!!!!KWALISA*
*INA MATA Y’AN KWALISA MASU JI DA GAYU HAFSAT COLLECTION TA MUSAMMAN CE WAJEN ZAKULO MABANBANTA HADAD’D’UN KAYA NA GAYU TUNDAGA KAN NA SAKAWA,KITCHEN, K’AWATA D’AKI DA SAURANSU ADO DA KWALLIYA SHINE CIKAR MACEN DA TASAN KANTA BA TA WASA DA KAYAN GAYU MUSAMMAN DA SUKA KASANCE NA DABAN DAGA FITACCIYAR Y’AR KASUWAR DA TA YI FICE A WANNAN FANNIN UWA UBA GA SAUKIN FARASHI BABU INDA BA TA AIKA KAYAN TA KUMA CIKIN YARDA DA AMINCI KAR KI BARI A BAKI LABARI Y’AR UWA DOMIN DUK MACEN DA TASAN KANTA BA TA WUCE HAFSAT COLLECTION BA TA NA SAYAR DA,
ATAMFA
LACE
CAMPY GWON
BAGS
SHOES
KITCHEN VTENSILS AND MORE
KAI TSAYE ZA KU SAMETA A ADDRESS D’INTA KAMAR HAKA
*KANO STATE KURNA LAYIN KUNYA STORE*
KO KUMA NUMBER WAYARTA KAMAR HAKA
*08131850861*

🅿️……………………….*15*

Fuska ta yi tamkar ba ita ba ta fito ran nan had’e tunda ta fito faruq ya zuba mata idanu ganin irin had’e fuskar da tayi ne ya sanyasa shima had’e tasa bayan isarta wajensa ya ce.

”meye kike ta wani harhad’e rai”ta na kallon gefe ta ce”bakomai “ya ce”daman haka muka Saba da ke ba gaisuwa ba komai kinzo kinmun tsaye k’ik’am “

har lokacin bata kallesa ba ta ce”Ina yini”ya ce “lafiya qlau daga Ina kike”makaranta”kai tsaye ta basa amsa”da izininwa kika tafi kin fad’a mun”?

karo na farko da ta d’ago tare da zuba masa idanu ta ce”daman sai na fada maka nake zuwa”?

ya ce”da da yanzu ba d’aya ba ne yanzu duk inda zaki sai kin sanar mun saboda wata ukku kamar haka kin zama mallakina”

ta yi shiru bata ce komai ba ya ce”ko bakiji ba”Cike da gajiya da maganar ta ce”na ji”

daga shi ba Wanda ya k’ara cewa uffan ya kula yau sabon iskanci take ji hakan ya sanyashi Jan tsaki inma wasu ke zugata zata dawo saiti ba d’aukar iskanci zaiyi ba”

ita dai bata ce k’ala ba sai part d’in Uncle da ta k’urawa ido lokacin da yake fitowa sanye cikin shigar kananun Kaya sosai Yayi masifar kyau dukda nisan da ke taakaninsu bai hanata jiyo daddad’an kamshin turarensa ba ko kallon inda suke baiyi ba ganin ya shiga mota tare da tadawa ya na Dannawa mai gadi horn ne ya sanyata jan doguwar ajiyar zuciya .

Faruq shima da hankalinshi na ga Adnan bai kula shi take kallo ba itama wani dogon tsaki ya ja ya ce”

“inma gani kike ko Marin da wancen sakaran mutumin yayimun a gabankine ban Rama ba kike wani shashshan magani to ba karfi na yafi ba wlh da yanzu haka yana asibiti na karairayasa darajar mahaifiyarsa kawai ya ci na kyalesa fatan kin gane ai”ta ce”Eh”

“Shiru ya yi itama ta yi shiru gani yake ta koma masa wata sabuwa kamar ba aydar sa da ya sani ba”Anjima zan kawo maki waya”

ta ce”Ummi ta ce ta ce anjima na je na zab’a”ya ce”ai ba hurumin ta ba ne nawa ne anjima ki shirya ko 11 ce a samo maki”

a ranta ta ce”sai shegen son abun duniya uban me zanyi da wata 11 ai darajara da ta sauko ko ni sai inyi kyautarta wlh “

a fili kuwa cewa tayi”ai yaya faruq da ka barta ka k’ara hidimar biki kaga akwai hidindimu gabanka”

murmushi ya yi ya ce”kuma fa hakane my love dad’ina da ke wani gamun akwai tunani in kikayi wani abun kamar me hankali”murmushin yak’e kawai ta yi,

ya ce”na ga kamar ma da yunwa kika dawo ko?ta ce”Eh “ya ce”to shikenan jeki huta gobe na dawo”ta ce”Allah kaimu”

harta shige ya na Binta da kallo saida ta bacewa ganinsa kafin ya sauke ajiyar zuciya ya ce”Alhmdulillah Allah na gode maka daka mallakamun wannan zukekiyar matsayin mata wlh nikam ko a haka an sallameni a duniya (Astagfurillah🤣)

Da dare ummi ta sanya driver ya kai Ayda ta zab’o iPhone 16pro kamar yanda ta fada zo kuga farinciki gurin Ayda kamar ba itace ta shiga damuwa kwana biyu ba “
Chapter 18 · 0% Book details