← Book details Ƙazamin Miji Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 44 OF 44

Sashe 44

Ƙazamin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

"Waye bawansa, ni? Allah sawaƙe, kin ga wannan klin ɗin Aminu ne zai zo yau sai ya wanje kayan nan duka tasss, ya ɗauraye ya shanya, wannan askar kuma wallahi yau sai na tattale wannan gashin kan nasa mai kwarkwata, na mayar da shi tanƙwal (Ƙwal uwar kwabo) Sannan sheba ɗin nan sai na aske masa wannan gashin hammatar da na mararsa, soson ƙarfen nan da shi zan saɓa jikin Aminu sau goma, don yadda yake sati ko fiye da hakan babu wanka na tabbata dauɗa tana nan nannage a fatarsa, sannan ya wanke kaushin wannan na ƙafarsa" Ta faɗa tana riƙe da ƙugu. Tsabar mamaki Saddiqa ta rasa abin cewa, hatta Zulaiha mamakin ƙarfin halin amaryar take don tana window tana ganin komai. Bata jira Saddiqa ta ce wani abu ba ta ɗora da faɗin

"Sai na zamewa Aminu ciwon ido a gidan nan, zai san ya auro gamonsa wallahi, sai na saka Aminu ya ƙyamaci ƙazanta da kansa ba don son ransa ba sai don dole uwar naƙi, Zulaiha ganin abin ba na wasa bane sai ta fito tsakar gida tana son ganin yadda wasan zai fara.

Ɗaki amarya ta koma, wata vest ta sako da wani shegen burgujejen wando tiri kwata, wanda ya bayyana asalin ƙibarta, da wayarta ta fito ta dokawa Aminu kira, Aminu yana surutu ya ga kiran amarya ya ɗauka sai ya tsinci maganarta cikin bada umarni tana cewa

"Ka zo gidan nan yanzun nan ina son ganinka" Zulaiha da Saddiqa suna jin yadda ya dirirce a wayar yana ta ambaton gashin nan zuwa.

Ba a jima ba sai suka ji ƙaran buɗe ƙofa, buguzum-buguzum Aisha ta wuce shi ya bi ta da kallo, kafin ya gama tunanin inda za ta je sai ya ji ta bankama sakata a ƙofar gida sakatar sama da ƙasa. Kamar an ce ya juya ya yi wa idanunsa masauki a kan gabaɗaya kayan da ta ajiye a tsakar gidan, don ganinsu ya bayyana masa dukkan aikin kayan saboda ya fahimta, idanu ya shiga gwalewa ya ɗaga kai ya sauke a kan fuskar Zulaiha wacce da alama dariyar ƙeta ce shimfiɗe a fuskarta, da sauri ya mayar da akalar ganinsa zuwa kan fuskar Saddiqa wacce hatta haƙoranta sun bayyana a dariyarta marar sauti, tun da ta baro Nihal tana bacci, yanzu kallon wasan da za a buga ya rage su ne masu gani.

Ƙaran takun dawowar Aisha shi ya sanya Aminu waigawa, gabansa yana dukan uku-uku.

*A NAN MUKA KAWO ƘARSHEN BOOK 1 WANDA NA BAKU A FREE, KU NUNA KULAWARKU DA SOYAYYARKU GA MARUBUCIYARKU MAMAN AFRAH, WAJEN SAYAN WANNAN LITTAFIN BOOK 2*

*DA NAIRA 500 KACAL ZA KI MORE KARATUN ƘAZAMIN MIJI HAR ƘARSHE, DON JIN YA ZA TA KAYA, ANYA AMINU ZAI YARDA A YI WANKAN NAN, A WANKE ƘAFA A ASKI MASA GASHIN DA TAKE JI DA SHI, A SANYA SHI YIN WANKIN DOLE, SHIN AISHA BATA ƊAKKO DA ZAFI BA*

*YA CAKWAKIYA ZA TA KASANCE TSAKANIN AMINA DA YAYA SULE GA KUMA SALAHA A GEFE, SHIN GASHI DAI SALAHA BATA SAN YANA DA MATA BA HAKA ITA MA AMINA BATA SAN DA AUREN SALAHA BA*

*ZA A BIYA KUÆŠIN KARATU 500 TA ASUSUN FAIZA ABUBAKAR 9030283375 OPAY SHAIDAR BIYA TA 09025576222*
Chapter 44 · 0% Book details