Sashe 40
Ƙazamin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BOOK 1
PAGE 18
*END OF BOOK 1*
*YAYA SULE*
Saurin saita kansa ya yi daga duniyar rashin gaskiyar da ya bayyana daga gare shi, ɓaro-ɓaro yana sakin wani murmushi ya ce
"Kai typin error ma bai yj ba, wai fa Abokiyata zan rubuta, shi ne na rubuta abokina" Ya faÉ—a yana kafe Salaha da idanu don ganin yadda za ta É—auki maganar. Shiru ta É—an yi tana nazartar maganar kafin ta ce
"Kai dama abokiya kake son saka mini, dama wani saurayin ƙawata ne suna hira sai ta karɓi wayarsa ta kira shi da wayarta, a take sunan GARZALI ya bayyana ɓaro-ɓaro, to da ta bani labari shi ne ni ma na ce zan gwada shi ne na ga ni kuma ABOKINA aka yi saving" Ƙoƙarin saita kansa ya yi ya ce
"Haba Baby ni ya za a yi ma in yi saving numberki da wani suna da ban wataƙila shi ma wancan saurayin ƙawar taki ko yana da aure ne, ba ya so matarsa ta gani... Tun kan ya kai ƙarshen maganar ta yi saurin katse shi da faɗin
"Kenan maza masu aure ne suke yin haka?" Da sauri ya ce
"Ba haka bane yawanci dai an fi samun hakan" Baki ta taɓe ta ce
"Ni fa shi ya sa kwata-kwata namiji mai mata ba ya birgeni" Wani yawu ya haÉ—iye sannan ya ce
"Ai dama ku mata bakwa son kishiya" Kallonsa ta yi ta ce
"Yo mai za a yi da auren mijin wata?" Yana ƙoƙarin danne abin da ya ji ya ce
"Kenan za ki iya bari a auri naki mijin? Na wata ne ba za ki bari ki aura ba... Ranta a ɓace ta ce
"Ka ga Sule ni fa ba na son irin wannan wasan, idan na shiga gidanka babu wacce za ta shigo" Galala yake kallonta a zuciyarsa ya ce
'Akwai cakwakiya, tabbas iska tana yawo da mai kayan kara, wannan ai shi ake nufi da rana zafi inuwa ƙuna' A fili kuma ya ce
"Ai babu ma wacce ta isa ta shigo" Daga haka suka cigaba da hirar soyayyarsu.
Soyayya ta cigaba da wakana babu kama hannun yaro, a inda Amina duk inda ta ji wata ƙawa ko da a ce ƙawar-ƙawarta ce mijin zai ƙara aure sai ta je ta ga ƙwaƙwaf, shi kuma Yaya Sule sai ya iya takunsa yanzu duk lokacin da zai shigo gidan sai ya sanya wayarsa airplane mode domin ya gwammace kar kiran kowa ya shigo wayarsa a kan rigimar Amina. Ai kuwa hakan da ya yi ba ƙaramin shakku ya cire mata ba, saboda yanzu ganin babu wani mai suna namiji da yake kiransa sai abin ya daina ɗarsa mata zarginsa, a inda shi kuma yake cin karensa babu babbaka.
A ɓangaren Salaha kuwa ko da ta masa ƙorafin ta nemi wayarsa bata samu ba, sai ya ce yanzu bai san mai ya sa idan ba waje ya fito ba, sai network ɗin wayarsa yake ɗaukewa, da hakan ya kuɓuta daga nata ƙotafi.
A ranar da ya samu Baba da maganar cewa, yana son ya ƙara aure, Baban farinciki ya yi, tun da shi al'adar Baba babu ruwansa da hana ɗansa ƙarin aure matsawar ɗan yana da halin riƙe matan nasa, domin a ganinsa hana ɗa ƙara aure tamar tauye masa haƙƙi ne, kuma bayan hakan halal ne kuma dai a nasa ganin hana hanzari a kan ƙara auren zai iya jefa yaron a halaka, sai dai abu ɗaya ne zai sanar da kai shi ne ka yi adalci.
Umma da ta ji hakan ba ƙaramin ranta ne ya ɓaci ba, a nata ganin ita indai namiji ya samu mace ta gari suna zaune lafiya ai ba a bar shi ya ƙara aure ba, tun da wani auren ƙarinsa fitina zai zama tun da duk namijin da ya haɗa mace sama da ɗaya to tabbas dole ya fuskanci ƙalubale, idan kuwa ya haɗu da mata mararsa imani da tsoron Allah, a nan kowacce saboda kishi za ta baje hajarta gaban malamai da bokaye shikenan fa, sai ka ga ya koma wani sha ka tafi, kowacce tana ƙoƙarin ta maido da hankalinsa kanta ta zama ita ce tauraruwa kuma ta sha gaban abokiyar zamanta a wajen miji, daga haka sai ya koma kamar wani zararre saboda an rikita masa ƙwaƙwalwa.
Baba ne ya dakatar da Umma a kan maganar, kamar yadda ya taka mata birki lokacin da Aminu ya zo da nasa batun ƙara auren, har yana nuna mata cewa Aminu ma shi ne ƙarami kuma bai daɗe da yin auren fari ba ya ƙara aure, sannan yanzu zai yi ta uku, bare kuma Sule da dake shi ne babba kuma har yana da yara biyu, don shi a tsarin Baba ko rana ɗaya ka ce za ka auri mace biyu ba zai hanaka ba.
Addu'a Umma ta yi da fatan zaman lafiya, wannan ya sanya Baba ya ce
"Haka ya dace iyaye su dawwama wajen yi wa ƴaƴansu fatan alkairi, a duk abin da suka sanya gaba su basu ƙwarin gwiwa, matsawar bai saɓawa Allah ba, duk abin da Allah ya halatta bai kamata a tauyewa wani ba" Ya faɗa yana kallonta, nuna masa ta yi ta gamsu da hakan, saboda ta lura Baba gani yake kamar don tana mace ne kishi ne yake sakawa take nuna rashin amincewarta idan yaran za su ƙara aure.
A nan Baba ya ya ce za su je nema masa auren, bayan ya gabatar musu da iyayen da unguwar su yarinya, sai Baban ya ce da zarar ya gama bincika wace ce yarinyar da nagartarta da ta iyayenta za su nema masa aurenta. Cikin wasa ma Baban ya kalli Yaya Sule ya ce
"Saura Malam Shafi'u kuma, tun da na san matsawar ya ƙyalla ido ya ganku da matan shi ma zai ce zai ƙara" Gabaɗaya suka yi dariya har Umma daga nan ya musu sallama ya tafi, bayan ya bayyanawa Umma a kan cewa yana son komai ya kasance a ɓoye, da ta tuhume shi ma a kan dalilin da zai ɓoyewa matarsa zai ƙara auren, sai ya fito mata da manufa da halayyar Aminar a kan kishiya, jin hujjojinsa ya sanya iyayen suka amince tun da Baba ya ce ita fitina kwantar da ita ake yi, musamman ma da Yaya Sulen ya sanar da su ba a gida ɗaya zai haɗa su ba, haya zai kamawa Salahar kafin Allah ya hore masa in yana da halin gina babban gida sai su tare.
Sun gansu kuma sun amince.
Tun da Baba ya yi bincike ya gano gidan su Salaha ƴan mutunci ne da dattako ga tarbiya, sai ya yi farinciki a inda aka je neman auren Yaya Sulen aka sanya daidai da ranar na Aminu, kasancewar ɓangaren amarya sun gama shirye -shirye.
Kwanaki suka shuɗe, suka rikiɗe suka zama satika, inda satika suka zama watanni, har ya rage saura sati biyu a ɗaura auren Yaya Sule, a inda har lokacin Amina bata da labari, don ko Sumayya bata faɗa mata ba, tun da Yaya Shafi'u ya gargaɗe ta a kan cewa ba a so ta sani, ita ma kuwa sai ta ja nata bakin ta yi shiru, idan Amina ta je wani bikin dannar ƙirji ta dawo tana ɗaga kai tana murna da nuna jin daɗin na yadda ta ga uwar gidan da ta je dannar ƙirjin cikin damuwa, sai ta zo tana bada labari tana dariya, Sumayya a zuciyarta ta ce
'Ke ma taki tana tafe, wannan shi ake kira rashin sani ya fi dare duhu'
Gidan da Yaya Sule ya kama ciki da falo ne, sai ɗaki ɗaya da bayi a ciki akwai wani a waje sai kuma kicin, irin gidan da ake yi wa laƙabi da gidan mace ɗaya.
Salaha har yau Sule bai sanar da ita yana da mata ba, daga ya yi yunƙurin faɗa mata, sai ya fahimci za ta iya fasa aurensa, su kuma su Baba sun ɗauka ya sanar da ita shinya sa ma ko da suka je neman auren basu faɗa musu ba. Tun da a nasu ganin duk inda aka yi soyyayya har ta kai ga an amincewa juna za a yi aure haƙiƙa an sanar da komai har hakan ya sanya yarda da amincewa na ƙulla auratayyar.
Ana saura sati ɗaya biki, lokacin har su Saddiqa sun tashi daga gidan, Yaya Sule ya shigo da wasu manyan shaddodi da ya ɗinka, set biyar ne, dama a satin Amina ta faɗa masa za ta je wani bikin dannar ƙirjin wata ƙawar, ƙawarta, tana faɗa masa ma bikin na yi ne don su Yusuf ma da Albani gjdansu za ta kai su, wannan dalilin ne ya sanya ya haɗu da wasu shaddodi guda biyu ɗinkakku da less ɗinkakke, duk shi ya bada aka ɗinka, Yusuf kala biyu Albani ma kala biyu.
Lokacin da ya shigo bai san mai ya sa ba, da ta amsa masa sallamar sai ya ji gabansa ya faÉ—i kawai sai yake ganin kamar za ta hango jirginsa, amma duba da yadda ya gama tsara maganar da zai faÉ—a mata sai ya ji É—an dama-dama.
"To fa yau kuma Abban Yusuf ledoji riƙi-riƙe haka mai muka samu" Ta ce tana linke kayan yaran da ta kwaso daga shanya. Ƴar dariyar ƙarfin hali ya yi gabansa don faɗuwa yake amma haka ya dake ya ce
"Ke dai bari cikin wasu kuɗaɗe da na samu, na mana ɗinkuna, kin san satin nan muna da bikin abokinmu, ga kuma ɗaurin auren Aminu, kuma ke ma na ji kin ce za ku yi bikin dannar ƙirji" Ya faɗa lokacin da ya samu waje ya zauna don tun kan ya zauna ne suke wannan maganar. Kayan ta ajiye ta fasa linkin ta ce
"Inyeee lallai shagali wan duna, gaskiya ka faranta mini, don dama ina son yin shigar kece raini yadda zan nunawa duk masu kishiya ni matar mijin mace ɗaya ce" Ta ce tana matsowa wajenta. Yadda ya ga tana rawar kai sai da dariya ta kusa kufce masa don har ya hango dirama da bidirin da za ta yi in ta ji shi ma auren zai yi, ya san tabbas har ƙaramar hauka sai ta yi. Cewa ya yi
PAGE 18
*END OF BOOK 1*
*YAYA SULE*
Saurin saita kansa ya yi daga duniyar rashin gaskiyar da ya bayyana daga gare shi, ɓaro-ɓaro yana sakin wani murmushi ya ce
"Kai typin error ma bai yj ba, wai fa Abokiyata zan rubuta, shi ne na rubuta abokina" Ya faÉ—a yana kafe Salaha da idanu don ganin yadda za ta É—auki maganar. Shiru ta É—an yi tana nazartar maganar kafin ta ce
"Kai dama abokiya kake son saka mini, dama wani saurayin ƙawata ne suna hira sai ta karɓi wayarsa ta kira shi da wayarta, a take sunan GARZALI ya bayyana ɓaro-ɓaro, to da ta bani labari shi ne ni ma na ce zan gwada shi ne na ga ni kuma ABOKINA aka yi saving" Ƙoƙarin saita kansa ya yi ya ce
"Haba Baby ni ya za a yi ma in yi saving numberki da wani suna da ban wataƙila shi ma wancan saurayin ƙawar taki ko yana da aure ne, ba ya so matarsa ta gani... Tun kan ya kai ƙarshen maganar ta yi saurin katse shi da faɗin
"Kenan maza masu aure ne suke yin haka?" Da sauri ya ce
"Ba haka bane yawanci dai an fi samun hakan" Baki ta taɓe ta ce
"Ni fa shi ya sa kwata-kwata namiji mai mata ba ya birgeni" Wani yawu ya haÉ—iye sannan ya ce
"Ai dama ku mata bakwa son kishiya" Kallonsa ta yi ta ce
"Yo mai za a yi da auren mijin wata?" Yana ƙoƙarin danne abin da ya ji ya ce
"Kenan za ki iya bari a auri naki mijin? Na wata ne ba za ki bari ki aura ba... Ranta a ɓace ta ce
"Ka ga Sule ni fa ba na son irin wannan wasan, idan na shiga gidanka babu wacce za ta shigo" Galala yake kallonta a zuciyarsa ya ce
'Akwai cakwakiya, tabbas iska tana yawo da mai kayan kara, wannan ai shi ake nufi da rana zafi inuwa ƙuna' A fili kuma ya ce
"Ai babu ma wacce ta isa ta shigo" Daga haka suka cigaba da hirar soyayyarsu.
Soyayya ta cigaba da wakana babu kama hannun yaro, a inda Amina duk inda ta ji wata ƙawa ko da a ce ƙawar-ƙawarta ce mijin zai ƙara aure sai ta je ta ga ƙwaƙwaf, shi kuma Yaya Sule sai ya iya takunsa yanzu duk lokacin da zai shigo gidan sai ya sanya wayarsa airplane mode domin ya gwammace kar kiran kowa ya shigo wayarsa a kan rigimar Amina. Ai kuwa hakan da ya yi ba ƙaramin shakku ya cire mata ba, saboda yanzu ganin babu wani mai suna namiji da yake kiransa sai abin ya daina ɗarsa mata zarginsa, a inda shi kuma yake cin karensa babu babbaka.
A ɓangaren Salaha kuwa ko da ta masa ƙorafin ta nemi wayarsa bata samu ba, sai ya ce yanzu bai san mai ya sa idan ba waje ya fito ba, sai network ɗin wayarsa yake ɗaukewa, da hakan ya kuɓuta daga nata ƙotafi.
A ranar da ya samu Baba da maganar cewa, yana son ya ƙara aure, Baban farinciki ya yi, tun da shi al'adar Baba babu ruwansa da hana ɗansa ƙarin aure matsawar ɗan yana da halin riƙe matan nasa, domin a ganinsa hana ɗa ƙara aure tamar tauye masa haƙƙi ne, kuma bayan hakan halal ne kuma dai a nasa ganin hana hanzari a kan ƙara auren zai iya jefa yaron a halaka, sai dai abu ɗaya ne zai sanar da kai shi ne ka yi adalci.
Umma da ta ji hakan ba ƙaramin ranta ne ya ɓaci ba, a nata ganin ita indai namiji ya samu mace ta gari suna zaune lafiya ai ba a bar shi ya ƙara aure ba, tun da wani auren ƙarinsa fitina zai zama tun da duk namijin da ya haɗa mace sama da ɗaya to tabbas dole ya fuskanci ƙalubale, idan kuwa ya haɗu da mata mararsa imani da tsoron Allah, a nan kowacce saboda kishi za ta baje hajarta gaban malamai da bokaye shikenan fa, sai ka ga ya koma wani sha ka tafi, kowacce tana ƙoƙarin ta maido da hankalinsa kanta ta zama ita ce tauraruwa kuma ta sha gaban abokiyar zamanta a wajen miji, daga haka sai ya koma kamar wani zararre saboda an rikita masa ƙwaƙwalwa.
Baba ne ya dakatar da Umma a kan maganar, kamar yadda ya taka mata birki lokacin da Aminu ya zo da nasa batun ƙara auren, har yana nuna mata cewa Aminu ma shi ne ƙarami kuma bai daɗe da yin auren fari ba ya ƙara aure, sannan yanzu zai yi ta uku, bare kuma Sule da dake shi ne babba kuma har yana da yara biyu, don shi a tsarin Baba ko rana ɗaya ka ce za ka auri mace biyu ba zai hanaka ba.
Addu'a Umma ta yi da fatan zaman lafiya, wannan ya sanya Baba ya ce
"Haka ya dace iyaye su dawwama wajen yi wa ƴaƴansu fatan alkairi, a duk abin da suka sanya gaba su basu ƙwarin gwiwa, matsawar bai saɓawa Allah ba, duk abin da Allah ya halatta bai kamata a tauyewa wani ba" Ya faɗa yana kallonta, nuna masa ta yi ta gamsu da hakan, saboda ta lura Baba gani yake kamar don tana mace ne kishi ne yake sakawa take nuna rashin amincewarta idan yaran za su ƙara aure.
A nan Baba ya ya ce za su je nema masa auren, bayan ya gabatar musu da iyayen da unguwar su yarinya, sai Baban ya ce da zarar ya gama bincika wace ce yarinyar da nagartarta da ta iyayenta za su nema masa aurenta. Cikin wasa ma Baban ya kalli Yaya Sule ya ce
"Saura Malam Shafi'u kuma, tun da na san matsawar ya ƙyalla ido ya ganku da matan shi ma zai ce zai ƙara" Gabaɗaya suka yi dariya har Umma daga nan ya musu sallama ya tafi, bayan ya bayyanawa Umma a kan cewa yana son komai ya kasance a ɓoye, da ta tuhume shi ma a kan dalilin da zai ɓoyewa matarsa zai ƙara auren, sai ya fito mata da manufa da halayyar Aminar a kan kishiya, jin hujjojinsa ya sanya iyayen suka amince tun da Baba ya ce ita fitina kwantar da ita ake yi, musamman ma da Yaya Sulen ya sanar da su ba a gida ɗaya zai haɗa su ba, haya zai kamawa Salahar kafin Allah ya hore masa in yana da halin gina babban gida sai su tare.
Sun gansu kuma sun amince.
Tun da Baba ya yi bincike ya gano gidan su Salaha ƴan mutunci ne da dattako ga tarbiya, sai ya yi farinciki a inda aka je neman auren Yaya Sulen aka sanya daidai da ranar na Aminu, kasancewar ɓangaren amarya sun gama shirye -shirye.
Kwanaki suka shuɗe, suka rikiɗe suka zama satika, inda satika suka zama watanni, har ya rage saura sati biyu a ɗaura auren Yaya Sule, a inda har lokacin Amina bata da labari, don ko Sumayya bata faɗa mata ba, tun da Yaya Shafi'u ya gargaɗe ta a kan cewa ba a so ta sani, ita ma kuwa sai ta ja nata bakin ta yi shiru, idan Amina ta je wani bikin dannar ƙirji ta dawo tana ɗaga kai tana murna da nuna jin daɗin na yadda ta ga uwar gidan da ta je dannar ƙirjin cikin damuwa, sai ta zo tana bada labari tana dariya, Sumayya a zuciyarta ta ce
'Ke ma taki tana tafe, wannan shi ake kira rashin sani ya fi dare duhu'
Gidan da Yaya Sule ya kama ciki da falo ne, sai ɗaki ɗaya da bayi a ciki akwai wani a waje sai kuma kicin, irin gidan da ake yi wa laƙabi da gidan mace ɗaya.
Salaha har yau Sule bai sanar da ita yana da mata ba, daga ya yi yunƙurin faɗa mata, sai ya fahimci za ta iya fasa aurensa, su kuma su Baba sun ɗauka ya sanar da ita shinya sa ma ko da suka je neman auren basu faɗa musu ba. Tun da a nasu ganin duk inda aka yi soyyayya har ta kai ga an amincewa juna za a yi aure haƙiƙa an sanar da komai har hakan ya sanya yarda da amincewa na ƙulla auratayyar.
Ana saura sati ɗaya biki, lokacin har su Saddiqa sun tashi daga gidan, Yaya Sule ya shigo da wasu manyan shaddodi da ya ɗinka, set biyar ne, dama a satin Amina ta faɗa masa za ta je wani bikin dannar ƙirjin wata ƙawar, ƙawarta, tana faɗa masa ma bikin na yi ne don su Yusuf ma da Albani gjdansu za ta kai su, wannan dalilin ne ya sanya ya haɗu da wasu shaddodi guda biyu ɗinkakku da less ɗinkakke, duk shi ya bada aka ɗinka, Yusuf kala biyu Albani ma kala biyu.
Lokacin da ya shigo bai san mai ya sa ba, da ta amsa masa sallamar sai ya ji gabansa ya faÉ—i kawai sai yake ganin kamar za ta hango jirginsa, amma duba da yadda ya gama tsara maganar da zai faÉ—a mata sai ya ji É—an dama-dama.
"To fa yau kuma Abban Yusuf ledoji riƙi-riƙe haka mai muka samu" Ta ce tana linke kayan yaran da ta kwaso daga shanya. Ƴar dariyar ƙarfin hali ya yi gabansa don faɗuwa yake amma haka ya dake ya ce
"Ke dai bari cikin wasu kuɗaɗe da na samu, na mana ɗinkuna, kin san satin nan muna da bikin abokinmu, ga kuma ɗaurin auren Aminu, kuma ke ma na ji kin ce za ku yi bikin dannar ƙirji" Ya faɗa lokacin da ya samu waje ya zauna don tun kan ya zauna ne suke wannan maganar. Kayan ta ajiye ta fasa linkin ta ce
"Inyeee lallai shagali wan duna, gaskiya ka faranta mini, don dama ina son yin shigar kece raini yadda zan nunawa duk masu kishiya ni matar mijin mace ɗaya ce" Ta ce tana matsowa wajenta. Yadda ya ga tana rawar kai sai da dariya ta kusa kufce masa don har ya hango dirama da bidirin da za ta yi in ta ji shi ma auren zai yi, ya san tabbas har ƙaramar hauka sai ta yi. Cewa ya yi