Sashe 37
Ƙazamin Miji Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Saddiqa ki taso ki kawo mini ɗauki, in kuma abu ya gagare ki ki tafi ɓangaren su Yaya Shafi'u su kawo agaji kar ta lahantani a banza, domin gabaɗaya ni na san riƙon da ta yi wa wajen nan mai daraja yadda kika san ta damƙo wuyan tinkiya" Wani ɓoyayyan tsaki Saddiqa ta saki don yanzu daga Aminu har Zulaiha haushi suke bata, kwata-kwata lamarinsu babu jan aji tamkar basu taɓa zaunawa aji da sunan ɗaukan karatu ba.
Zulaiha kuwa jin yana cewa a kira ƴan uwansa, sai ta ƙara ƙaimi wajen jansa, saboda so take sai ya jigata kafin ta ƙyaleshi in ya so daga yau zai daina raina mata hankali. Aminu kuwa jiran amsar Saddiqa yake jin bata ce komai ba ya fara magana da cewa
"Shikenan dama an ce na shiga ban ɗauka ba, bata fidda ɓarawo, shikenan ni kuma sai yadda hali ya yi ɓarawo a hannun mata" Zulaiha ɗan sunkuyawa ta yi kamar mai jan abin da ya fi ƙarfinta, Aminu jin za ta lahanta shi ya shiga roƙonta, ko ta kansa bata bi ba ta fisge shi sai kuwa ya daina ja baya son ya ga za ta masa lahani a zuciyarsa ya ce
'Ɗakin Saddiqar nan dai ko ɗakin gwal ne, gwara in haƙura da kwanan yau, in ba haka ba sai dai a zo ana mini jaje, ko dai ta mayar da ni mata maza ko ta cisge mini mafitsarae ma ta sa in shiga uku, sai dai in ga ana aure ni kuwa da nake da niyyar sai na rufe ƙofa, wato mata huɗu' Ya faɗana ransa yana daina togewa daga jan da take masa, a haka suka fita bar ƙofar ɗakin Saddiqa, suna tafiya Zulaiha tana jaye da hantsar wandon, yana ji yana gani sai waiwayen ɗakin Saddiqa yake bayan ya san ya gama shawo kanta ta amince da shi amma Zulaiha ta kawo cikas.
Suna dab da ƙarasawa ɗakin Zulaiha wata dibara ta faɗowa Aminu, tunani ya yi a kan ya damƙi gashin Zulaiha tun da ya san tsawon lokacin nan bata yi kitso ba kuma ba mai take shafawa ta taje ta gyara ba, ya san kuwa dole ta ji ciwo, Zulaiha ta juya tana jansa hankali kwance a ranta tana jin daɗin ta raba shi da ɗakin Saddiqa tana ƙudurtar yanzu ta fara yin hakan, duk da gargaɗin da Saddiqa ta mata ya ɗan razanata, amma dai a nata ganin ta samu lagon Aminu da za ta ƙwace shi ya koma hannunta, Saddiqa ta zama ƴar kallo.
Tana murmushin jin daɗin a ranta sai ta ji kamar daga sama an damƙi gashinta, wani ƙara ta saki don sosai ya damƙa yadda za ta ji a jikinta, zafin da ya ziyarce ta sai ta manta da riƙon da ta yi wa Aminu don tuni ta sake shi, bai saka mata ba sai da ya bari ta sakankance ya saki.
Hannunta duka biyu ta kai ta dafe kan nata, kafin ƙiftawar ido Aminu ya fita da gudu, zai koma ɗakin Saddiqa don yau kawai hango shi yake ya kasance da ita. Sai lokacin Zulaihanta lura da abin da ya yi ta kuwa take masa baya, Aminu yana dab da faɗawa ɗakin Saddiqa a nufinsa yana shigewa zai saka sakata, sai dai mai kusan ƙarasowarsa ya yi daidai da tashin Saddiqa wacce ta burmawa ƙofar ɗakinta sakatar sama da ƙasa. Don haka Aminu gwaram ya bugu da jikin ƙofa, wanda hakan ya yi daidai da zuwan ƴar aljanna tana zuwa a maimakon ta damƙi hantsar sai ta kamo tsantsar wandon wato ƙugun ƙiiiii ta shiga jansa da baya, sai rafka salati yake jin tana jansa da ƙarfi kuma sai taka duwatsun tsakar gidan yake, tana zuwa ta tura shi cikin ɗakin ta garƙama sakata, daga shi har ita suka shiga mayar da numfashi kowa yana aikawa ɗan uwansa harara kamar idanunsa za su faɗo.
Banza ta masa ta zauna bakin gado tana ɗan taɓa kanta, don yanzu gabaɗaya kanta ma ciwo yake sanadin gashin da Aminu ya ja mata. Shi kuwa a tsakar ɗakin ya zauna yana buga tagumi hannu bibbiyu, Zulaiha kallo ɗaya ta masa ta taɓe baki ta ce
"Ai ko zinariya ce wannan matar taka, dole ka haƙura sai kwanaki bakina ya ƙare sannan" Tamkar ya saki kuka haka ya ji, yana ciro hannu ɗaya daga tagumin da ya buga ya kai hantsar wandon nasa ya taɓo jikinsa, yana son tabbatar da cewa Zulaiha bata yi masa illa ba, yana ɗauke hannun daga wajen ya kai ƙugun wandon wanda Zulaiha ya janyo shi baya ta saka hantsar kasancewar wandon ya ci uban tsufan shi ya sa jan da ta yi masa ya taɓe don yanzu har zamewa yake yi ma ba ya zama a jikinsa.
Idanu ya runtse yana jin daman bai auro Zulaiha ba don ta sanya shi a rijiyar matsala mai gaba dubu. Jin tafiya a cikin gashin kansa gabansa ya faɗi, don duk a tunaninsa yadda ya wanke kansa da klin ya taje to kwarkwatar ta fita amma wani ƙaiƙayi da ya ziyarce shi ya hau susa da hannu biyu.
Kallon Zulaiha ya yi wacce take susa tun ƙarfi kamar zai yi kuka ya ce
"Wallahi Zulai kin cuceni," Bata daina susar na ta masa kallon sheƙeƙe ta ce
"Da na maka me?" A ƙufule yana susa ya ce
"Da kika kwasa mini kwarkwata mana" Baki ta taɓe ta sosa tsakiyar kan nata, tare da dunƙule hannun ta ranƙwashi kan nata inda ta ji ƙaiƙan ya fi yawa ta ce
"Muka kwasawa juna dai, ni fa ba na jin ma cikin gashin nan naka za a rasa kyankyasai, don na san tsabar datti da wari kyankyaso zai ɗauka masai ne ya shige maka kai... Tsaye ya miƙe yana muzurai ya ce
"Wallahi Zulai kin ga makwancina da yawa, amma tun da kin rainanj zan fara banbance miki aya da tsakuwa don bana ɗaukan raini, Saddiqa sai yadda na yi da ita sai abin da na ce mata, kuma bata taɓa faɗa miki magana a kan ƙazanta don ta tozartani ko ci mini mutunci ba, amma ke kin zo da sabon salo kiran sallah da usur, ke irin kawaicin nan ma na farkon zuwa da amare suke yi baki yi ba... Dariyar da ta kwashe da ita ne ya dakatar da Aminu daga banbamin faɗan da ya ɗauka, sai da dariyar ta tsagaita mata ta ce
"Saddiqa ka ce, an faɗa maka kowace mace ce mai haƙuri ko kawar da kai, da can baka san abin da take maka ba sai da ka rufe ido ka rambaɗo mata kishiya, sai yanzu ne ka san halaccin da ta maka, ku dama maza ai bakwa gane halaccin mace a wajenku, to ni ba zan ɗauki duk wani soki burutsu ba, kuma da kkae batun bata maka cin fuska a kan ƙazanta wannan ita ta ga dama, kuma wallahi Aminu aurenka kaɗai ma sai dai in ce Allah ya sa kaffara ne" Ta faɗa tana tafa cinya.
Bai ji zai ita furta komai ba shi yanzu lamarin Zulaiha ya fara wuce masa makaÉ—i da rawa, yanzu tunaninsa ma É—aya yadda ta je ta janyo shi, ba don Allah ya sa cikin dare bane gida ba su kaÉ—ai ba ai da ta gama kunce masa zani a kasuwa.
Yana ji tana ta nasifar ya fara gudunta tun ba a cinye amarci ba, don munafurci yana ƙulafucin uwar gidansa. Zuwa ya yi zai canja wandon tun da ta taɓa ƙugun wandon nasa, amma sai ya tarar ashe duka ya kwashe kayan ya mayar ɗakin Saddiqa. Can gefe ya raɓe ya kwanta, zuwa can ita ma ta shiga zabga doguwar hamma, hakan ya sa ta kwanta a kusa da shi, da ya ƙyalla ido ya bucan kanta wanda babu hula bare ɗankwali a kusa da nasa kan, sai da ya bari bacci ya sure ta ya lallaɓa ya maida kansa wajen ƙafarta wato suka yi kai da ƙafa. Ashe ba nisan bacci ba ta yi, sai ji tashinta ya yi hakan ya sanyabya fara sakin munsharin ƙarya, bata bj ta kan munsharinsa ba sai ji ya yi ƙiii ta ja ƙafafunsa duka biyu, ta juya shi kamar wata waina a tanda, ta mayar masa da kansa inda ya ɗauke wato suka koma ga kanta ga nashi, kowa hannu a ka yana susa a haka bacci ya sure su.
A haka sai da Aminu ya ƙarasa ragowar kwanaki ukun nan na sari biyun Zulaiha, don addabarsa ta yi da masifa, zuwa wannan kwanakin kwanukan Zulaiha duk suna baje a kicin kaca-kaca don har ranar ko kwanunkan da baƙin Aminu suka ci abinci bata wanke ba. Abin da ya fara ci wa Saddiqa tuwo a ƙwarya kenan, ita gashi bata ƙaunar ƙazanta sai kuma ta haɗu da miji ƙazami kishiyar ma ƙazama. Har bata son zuwa kicin saboda yadda ƙudaje suke safa da marwa a kan kwanukan Zulaiha, farantina food flaks cokula tukwane babu wanda babu ta lodosu abinta, idan za ta yi amfani da kwano, saboda baƙar ganda da ƙazanta ba za ta ɗauka cikin mararsa wankin ta wanke, sai dai ta ƙara buɗe wani sabo fil ta yi amfani da shi. Ga rashin iya girkin da bata yi ba sai ta yi abincin wajen sau nawa, wani lokacin sai ta dafa shinkafa kusan sau uku kafin ta samu wacce za ta ci wata ta ƙone wata ta yi ɗanya-ɗanya wata kuma gata nan dai to ta hakan yake ɓata kwanuka masu yawa, ko mai za ta soya sai ya ƙone duk kayan garar da aka kawo musu ta ci ƙarfinsu.
Zulaiha kuwa jin yana cewa a kira ƴan uwansa, sai ta ƙara ƙaimi wajen jansa, saboda so take sai ya jigata kafin ta ƙyaleshi in ya so daga yau zai daina raina mata hankali. Aminu kuwa jiran amsar Saddiqa yake jin bata ce komai ba ya fara magana da cewa
"Shikenan dama an ce na shiga ban ɗauka ba, bata fidda ɓarawo, shikenan ni kuma sai yadda hali ya yi ɓarawo a hannun mata" Zulaiha ɗan sunkuyawa ta yi kamar mai jan abin da ya fi ƙarfinta, Aminu jin za ta lahanta shi ya shiga roƙonta, ko ta kansa bata bi ba ta fisge shi sai kuwa ya daina ja baya son ya ga za ta masa lahani a zuciyarsa ya ce
'Ɗakin Saddiqar nan dai ko ɗakin gwal ne, gwara in haƙura da kwanan yau, in ba haka ba sai dai a zo ana mini jaje, ko dai ta mayar da ni mata maza ko ta cisge mini mafitsarae ma ta sa in shiga uku, sai dai in ga ana aure ni kuwa da nake da niyyar sai na rufe ƙofa, wato mata huɗu' Ya faɗana ransa yana daina togewa daga jan da take masa, a haka suka fita bar ƙofar ɗakin Saddiqa, suna tafiya Zulaiha tana jaye da hantsar wandon, yana ji yana gani sai waiwayen ɗakin Saddiqa yake bayan ya san ya gama shawo kanta ta amince da shi amma Zulaiha ta kawo cikas.
Suna dab da ƙarasawa ɗakin Zulaiha wata dibara ta faɗowa Aminu, tunani ya yi a kan ya damƙi gashin Zulaiha tun da ya san tsawon lokacin nan bata yi kitso ba kuma ba mai take shafawa ta taje ta gyara ba, ya san kuwa dole ta ji ciwo, Zulaiha ta juya tana jansa hankali kwance a ranta tana jin daɗin ta raba shi da ɗakin Saddiqa tana ƙudurtar yanzu ta fara yin hakan, duk da gargaɗin da Saddiqa ta mata ya ɗan razanata, amma dai a nata ganin ta samu lagon Aminu da za ta ƙwace shi ya koma hannunta, Saddiqa ta zama ƴar kallo.
Tana murmushin jin daɗin a ranta sai ta ji kamar daga sama an damƙi gashinta, wani ƙara ta saki don sosai ya damƙa yadda za ta ji a jikinta, zafin da ya ziyarce ta sai ta manta da riƙon da ta yi wa Aminu don tuni ta sake shi, bai saka mata ba sai da ya bari ta sakankance ya saki.
Hannunta duka biyu ta kai ta dafe kan nata, kafin ƙiftawar ido Aminu ya fita da gudu, zai koma ɗakin Saddiqa don yau kawai hango shi yake ya kasance da ita. Sai lokacin Zulaihanta lura da abin da ya yi ta kuwa take masa baya, Aminu yana dab da faɗawa ɗakin Saddiqa a nufinsa yana shigewa zai saka sakata, sai dai mai kusan ƙarasowarsa ya yi daidai da tashin Saddiqa wacce ta burmawa ƙofar ɗakinta sakatar sama da ƙasa. Don haka Aminu gwaram ya bugu da jikin ƙofa, wanda hakan ya yi daidai da zuwan ƴar aljanna tana zuwa a maimakon ta damƙi hantsar sai ta kamo tsantsar wandon wato ƙugun ƙiiiii ta shiga jansa da baya, sai rafka salati yake jin tana jansa da ƙarfi kuma sai taka duwatsun tsakar gidan yake, tana zuwa ta tura shi cikin ɗakin ta garƙama sakata, daga shi har ita suka shiga mayar da numfashi kowa yana aikawa ɗan uwansa harara kamar idanunsa za su faɗo.
Banza ta masa ta zauna bakin gado tana ɗan taɓa kanta, don yanzu gabaɗaya kanta ma ciwo yake sanadin gashin da Aminu ya ja mata. Shi kuwa a tsakar ɗakin ya zauna yana buga tagumi hannu bibbiyu, Zulaiha kallo ɗaya ta masa ta taɓe baki ta ce
"Ai ko zinariya ce wannan matar taka, dole ka haƙura sai kwanaki bakina ya ƙare sannan" Tamkar ya saki kuka haka ya ji, yana ciro hannu ɗaya daga tagumin da ya buga ya kai hantsar wandon nasa ya taɓo jikinsa, yana son tabbatar da cewa Zulaiha bata yi masa illa ba, yana ɗauke hannun daga wajen ya kai ƙugun wandon wanda Zulaiha ya janyo shi baya ta saka hantsar kasancewar wandon ya ci uban tsufan shi ya sa jan da ta yi masa ya taɓe don yanzu har zamewa yake yi ma ba ya zama a jikinsa.
Idanu ya runtse yana jin daman bai auro Zulaiha ba don ta sanya shi a rijiyar matsala mai gaba dubu. Jin tafiya a cikin gashin kansa gabansa ya faɗi, don duk a tunaninsa yadda ya wanke kansa da klin ya taje to kwarkwatar ta fita amma wani ƙaiƙayi da ya ziyarce shi ya hau susa da hannu biyu.
Kallon Zulaiha ya yi wacce take susa tun ƙarfi kamar zai yi kuka ya ce
"Wallahi Zulai kin cuceni," Bata daina susar na ta masa kallon sheƙeƙe ta ce
"Da na maka me?" A ƙufule yana susa ya ce
"Da kika kwasa mini kwarkwata mana" Baki ta taɓe ta sosa tsakiyar kan nata, tare da dunƙule hannun ta ranƙwashi kan nata inda ta ji ƙaiƙan ya fi yawa ta ce
"Muka kwasawa juna dai, ni fa ba na jin ma cikin gashin nan naka za a rasa kyankyasai, don na san tsabar datti da wari kyankyaso zai ɗauka masai ne ya shige maka kai... Tsaye ya miƙe yana muzurai ya ce
"Wallahi Zulai kin ga makwancina da yawa, amma tun da kin rainanj zan fara banbance miki aya da tsakuwa don bana ɗaukan raini, Saddiqa sai yadda na yi da ita sai abin da na ce mata, kuma bata taɓa faɗa miki magana a kan ƙazanta don ta tozartani ko ci mini mutunci ba, amma ke kin zo da sabon salo kiran sallah da usur, ke irin kawaicin nan ma na farkon zuwa da amare suke yi baki yi ba... Dariyar da ta kwashe da ita ne ya dakatar da Aminu daga banbamin faɗan da ya ɗauka, sai da dariyar ta tsagaita mata ta ce
"Saddiqa ka ce, an faɗa maka kowace mace ce mai haƙuri ko kawar da kai, da can baka san abin da take maka ba sai da ka rufe ido ka rambaɗo mata kishiya, sai yanzu ne ka san halaccin da ta maka, ku dama maza ai bakwa gane halaccin mace a wajenku, to ni ba zan ɗauki duk wani soki burutsu ba, kuma da kkae batun bata maka cin fuska a kan ƙazanta wannan ita ta ga dama, kuma wallahi Aminu aurenka kaɗai ma sai dai in ce Allah ya sa kaffara ne" Ta faɗa tana tafa cinya.
Bai ji zai ita furta komai ba shi yanzu lamarin Zulaiha ya fara wuce masa makaÉ—i da rawa, yanzu tunaninsa ma É—aya yadda ta je ta janyo shi, ba don Allah ya sa cikin dare bane gida ba su kaÉ—ai ba ai da ta gama kunce masa zani a kasuwa.
Yana ji tana ta nasifar ya fara gudunta tun ba a cinye amarci ba, don munafurci yana ƙulafucin uwar gidansa. Zuwa ya yi zai canja wandon tun da ta taɓa ƙugun wandon nasa, amma sai ya tarar ashe duka ya kwashe kayan ya mayar ɗakin Saddiqa. Can gefe ya raɓe ya kwanta, zuwa can ita ma ta shiga zabga doguwar hamma, hakan ya sa ta kwanta a kusa da shi, da ya ƙyalla ido ya bucan kanta wanda babu hula bare ɗankwali a kusa da nasa kan, sai da ya bari bacci ya sure ta ya lallaɓa ya maida kansa wajen ƙafarta wato suka yi kai da ƙafa. Ashe ba nisan bacci ba ta yi, sai ji tashinta ya yi hakan ya sanyabya fara sakin munsharin ƙarya, bata bj ta kan munsharinsa ba sai ji ya yi ƙiii ta ja ƙafafunsa duka biyu, ta juya shi kamar wata waina a tanda, ta mayar masa da kansa inda ya ɗauke wato suka koma ga kanta ga nashi, kowa hannu a ka yana susa a haka bacci ya sure su.
A haka sai da Aminu ya ƙarasa ragowar kwanaki ukun nan na sari biyun Zulaiha, don addabarsa ta yi da masifa, zuwa wannan kwanakin kwanukan Zulaiha duk suna baje a kicin kaca-kaca don har ranar ko kwanunkan da baƙin Aminu suka ci abinci bata wanke ba. Abin da ya fara ci wa Saddiqa tuwo a ƙwarya kenan, ita gashi bata ƙaunar ƙazanta sai kuma ta haɗu da miji ƙazami kishiyar ma ƙazama. Har bata son zuwa kicin saboda yadda ƙudaje suke safa da marwa a kan kwanukan Zulaiha, farantina food flaks cokula tukwane babu wanda babu ta lodosu abinta, idan za ta yi amfani da kwano, saboda baƙar ganda da ƙazanta ba za ta ɗauka cikin mararsa wankin ta wanke, sai dai ta ƙara buɗe wani sabo fil ta yi amfani da shi. Ga rashin iya girkin da bata yi ba sai ta yi abincin wajen sau nawa, wani lokacin sai ta dafa shinkafa kusan sau uku kafin ta samu wacce za ta ci wata ta ƙone wata ta yi ɗanya-ɗanya wata kuma gata nan dai to ta hakan yake ɓata kwanuka masu yawa, ko mai za ta soya sai ya ƙone duk kayan garar da aka kawo musu ta ci ƙarfinsu.