Sashe 41
Gudun Aure Part 5 Hausa Novel · about 7 min read
Na so a ce a ranar girkina na yi wa maigidan godiya ta mussaman domin duk abinda nake ji a zuciyata game dashi ya yi abinda lallai dole a yaba masa. Ko bai fad'a ba duniya ta sheda hakan ba yayin kyautar fariya ko ta ganin ido. A baka hannun hagu bai san an bayar ba. Ka zo yau a yi maka gobe ma ka dawo a yi maka ba za a ce an baka jiya ba. Baya ta'ba alheri ya fad'a sai dai duniya ta fad'a.
Washe gari da safe dana daidaici Hauwa ta sauko daga saman tunda dama koda ba ni da girki na kan hau mu gaisa Wani sa'in ko shi ya biyo ni d'aki. Sai da laulayin nan ya tsananta ne ya sanya ni b'akincikin hawa saman nasa domin idan na kalleshi haka kawai sai na ji haushinsa ya kamani. Duk kuwa da kokarin lallabani da yake yi gudun kada cikin ya samu matsala ya zube kamar na baya. Baya yi mini abinda zai ba ni haushi duk abinda na ce ba na so zai bari duk son sa da ya kusance ni idan na nuna a a sai kawai ya ha'kura ya shiga wata sabgar shiyasa ganina da sassafe ya ba shi mamaki ya shirya tsaf cikin manyan kaya har da nad'i a saman jar darar da take kansa ya yi kyau ainun cikin shadda wagambari mai kalar sararin samaniya babbar rigar tasha aiki kafafunshi sanye da ba'kar safa yayin da takalmansa sahu ciki suke gefe sai kyalli suke yi. Gabad'aya d'akin ya game da kamshin turaransa wanda ya riga ya gama zaunawa a jikinsa. Na kàrasa a nutse na zauna a gefansa. Ya dinga kallona kamar ya ga sabuwar hallita ya ma kasa d'aura agogon da yake hannunsa kawai ya 'kura mini idanuwansa da suke cike da tambayoyi.
[12/26, 7:56 PM] bintaumarabbale: *123*
Agogon da yake ri'ke a hannunsa na kar'ba na ri'ke tsintsinyar hannunsa na dama wanda anan na lura yake daura a gogo na fara daura masa a tsanake zuciyata na kara yin sanyi da lamarinsa. Tabbas na yarda d'an adam tara yake bai cika goma ba. Kuma ko na'ki ko na so wannan mutumin tarin alheransa sun rinjayi sharrinsa ya yawa. Domin da wahala na ji suka da zambu a kansa ta ko'ina sai yabo da fatan alheri. Bai ce mini komai ba har na gama daura masa agogon yana kallona na kai hannun bakina na sumbuta kafin na dube shi fuskata a sake na ce." Barka da asubahi Babanmu."
Yana k'ayatattacen murmushi ya amsa da "Barkanmu dai Aminatu my princess." Na dariya kawai ina kallonsa kafin na gyada kaina na ce." Da gaske?"
Ya ce." Kwarai kuwa ai babu wata sarauniya a birnin zuciyata sai ke." Ban ce komai ba kawai na ri'ke hannunsa tare da had'e yatsunmu wuri d'aya.
Ya sauke sanyayyar ajiyar zuciya yana kallona ya ce." Amma ni ba babanki ba ne Amina, kin manta ni duniyarki ne fa, ni ne mai k'urewa jin dadinki lamba mai yasa za ki kira ni da baba."
Na danne kunyar da ta taso mini na dube shi da 'yar dariya na ce." Na rasa da wane suna ka dace ina ganin kiranka da Baba shine karshen mutuntawa."
Yana murmushi ya dubi agogon dana daura masa ya gyada kansa yana fad'in." Yau ni dake kamar wasu sabbin masoya, kina so ki shagaltar da ni, jirginmu ya kusa tashi bakwai da minti goma yanzu takwas daidai za mu tashi in sha Allahu kuma yau zan dawo sai mu kàrasa soyayyar don na ga alama addu'ata ce ta kar'bu a kanki."
Na dube shi a hankali haka kawai sai wani tausayinsa ya rufe ni, wai aka ce sai da so ake kishi da tausayi to amma in ba haka ba ai wannan mutumin ba abin tausayi ba ne, mutumin da Allah ya wadata da suttura da jin dadi na gidan duniya.
Hannuna na kai fuskarsa ina dan jan gemunsa da ya yi 2colors fari da baki ya kwanta sosai ya kuma k'awata masa fuskarsa. Na furta." Ka yi kyau sosai, kamar ango."
Ya kanne idonsa yana fad'in." Shine ai ba ki ga na yi gayu ba."
Murmushi na yi tare da fad'in." Haba da Nabilan kenan?"
Ya daga kansa yana kallon yanayina. Na ce." Mai yasa ka boye mini abinda lallai kasan ba zai 'boyu ba."
Ya yi jim yana kallona, sai na girgiza kaina ina ko'karin mayar da k'wallar da take ko'karin zubowa na furta." Jiya Kamalu ya kira ni a waya ya gaya mini abinda ka 'boye mini. Ba ni da bakin godiya Baba, Allah Ya saka da alheri, Ubangiji Allah yadda ka dubi marayun yaran nan ina ro'kon Allah Ya dubi naka abinda ka yi na alheri Allah Ya sanya maka a mizani, na gode na god....! Ban kàrasa ba kukan da nake dannewa ya kufce. Da saurin gaske ya janyo ni jikinsa ya rike ni sosai yana d'an dukan bayana a hankali cikin sigar rarrashi yake fad'in."Daina kuka Amina, ai bake na yi wa ba kaina na taimaka, bakin san da cewa hakkin yaranki a kaina yake ba ai a musulce ni ubansu ne tunda ina auranki, babu buk'atar godiya a tsakaninmu. Yaranki da wani namijin ki ajiye a ranki kamar da ni ne, ai Aminu Salihi da k'arfi da lafiyarsa muka hadu muka nemi dukiyar tare don haka don na sake yin wani abu akan yaran nan ki ce za ki yi mini godiya ko ki yi kuka ni ma na sauke hakki ne, na kuma gode da kyawawan addu'oinki, Allah Ya shirya mini ku bakidaya.
Ri'ke shi na yi sosai a ajikina ina sauke ajiyar zuciya amma hawayen dake zuba daga idona sun kasa tsayuwa.
Ya dago ni yana duban fuskata ya sanya tafin hannunsa yana goge mini a d'an sanyaye ya furta." Ya isa na ce, ki yi shiru humm!, yawwa ko kefa, ki yi mini murmushi nan kin ji tawan"
Murmushi na yi irin mai tafe da kuka na sake rungume shi a jikina kam kukan da k'arfi ya k'wace mini.
Ya diririce sosai yana ta jijjigani "Menene haka Amina na gaya miki akwai abinda yake gabana, kukan na menene haka?"
Na dago kaina Ina kallonsa cikin kukan na ce." Don Allah ka yi hakuri da abinda na dinga yi maka ka ji."
Ya ce." Ni ba ki yi mini komai ba kuma ban ta'ba rikonki ba, ai ni ne zan ce ku yafe mini."
Na ce." Mune dai za ka yafe wa tunda aljannar mu tana kasan kafafunka don Allah ni ma koda na mutu ka dinga yabona kana fad'in alherina irin na Momi."
Ya b'ata rai yana fad'in." Me ya kawo zancen mutuwa kuma?"
Na yi shiru ban ce komai ba domin ni ma jin maganar kawai na yi ta fito daga bakina.
Ya tashi yana gyara babbar rigarsa ni ma na tashi Ina kallonsa yanayinsa ya canza. Na ce." Ka na son ka auri Nabila ko?"
Wani irin duba ya yi mini kafin ya gyada kansa ya mik'a hannu ya debi wayoyinsa dake zube a gadon ya kama hanya zai fita.
Na bi shi da sauri Ina fad'in." Ka tsaya ka ji."
Ya ja ya tsaya yana dan hararata kafin ya ce." Ke ba a fara magana dake a kare lafiya Amina, wanene ya sako Nabila a cikin maganar mu?"
Na ce." Dama zan ce ne na amince idan kana sonta ka aureta wallahi."
A hanzarce ya furta." Ai dama can ku ba ku isa ku hana ni auranta ba idan ina da ra'ayi. Nabila ta bi ta hanyoyi da yawa domin kamun kafa ta had'a kai da su Salim ta nemi Hajiya Ayya mahaifiyar abokina Alhaji Amadu duk akan tana so ta maye gurbin 'yar uwarta na ce a a saboda wasu dalilina. Ba wai tsoronku ne ya hana ni auranta ba."
A sanyaye na ce." To shikkenan, Allah Ya bata wani."
Ya amsa da "Amin yana ko'karin bud'e 'kofar d'akin
Tare muka sauka kasa wanda ya yi daidai da fitowar Hauwa daga dakinta cikin shiri. Ganinsa a shirye da shirin tafiya ya sanya ta ce." Da gaske dai ba za ka yi breakfast din ba kenan?"
Ya ce." Idan na je gidan Hajja sai na yi na gode da kokarinki."
Daga haka sai ya nufi kofar fita a d'an gurguje. Muka had'a baki wurin fad'in." Allah Ya tsare hanya a gaishe da Hajja." Ba tare da ya juyo ba ya amsa da "Za ta ji in sha Allahu rabbi."
Washe gari da safe dana daidaici Hauwa ta sauko daga saman tunda dama koda ba ni da girki na kan hau mu gaisa Wani sa'in ko shi ya biyo ni d'aki. Sai da laulayin nan ya tsananta ne ya sanya ni b'akincikin hawa saman nasa domin idan na kalleshi haka kawai sai na ji haushinsa ya kamani. Duk kuwa da kokarin lallabani da yake yi gudun kada cikin ya samu matsala ya zube kamar na baya. Baya yi mini abinda zai ba ni haushi duk abinda na ce ba na so zai bari duk son sa da ya kusance ni idan na nuna a a sai kawai ya ha'kura ya shiga wata sabgar shiyasa ganina da sassafe ya ba shi mamaki ya shirya tsaf cikin manyan kaya har da nad'i a saman jar darar da take kansa ya yi kyau ainun cikin shadda wagambari mai kalar sararin samaniya babbar rigar tasha aiki kafafunshi sanye da ba'kar safa yayin da takalmansa sahu ciki suke gefe sai kyalli suke yi. Gabad'aya d'akin ya game da kamshin turaransa wanda ya riga ya gama zaunawa a jikinsa. Na kàrasa a nutse na zauna a gefansa. Ya dinga kallona kamar ya ga sabuwar hallita ya ma kasa d'aura agogon da yake hannunsa kawai ya 'kura mini idanuwansa da suke cike da tambayoyi.
[12/26, 7:56 PM] bintaumarabbale: *123*
Agogon da yake ri'ke a hannunsa na kar'ba na ri'ke tsintsinyar hannunsa na dama wanda anan na lura yake daura a gogo na fara daura masa a tsanake zuciyata na kara yin sanyi da lamarinsa. Tabbas na yarda d'an adam tara yake bai cika goma ba. Kuma ko na'ki ko na so wannan mutumin tarin alheransa sun rinjayi sharrinsa ya yawa. Domin da wahala na ji suka da zambu a kansa ta ko'ina sai yabo da fatan alheri. Bai ce mini komai ba har na gama daura masa agogon yana kallona na kai hannun bakina na sumbuta kafin na dube shi fuskata a sake na ce." Barka da asubahi Babanmu."
Yana k'ayatattacen murmushi ya amsa da "Barkanmu dai Aminatu my princess." Na dariya kawai ina kallonsa kafin na gyada kaina na ce." Da gaske?"
Ya ce." Kwarai kuwa ai babu wata sarauniya a birnin zuciyata sai ke." Ban ce komai ba kawai na ri'ke hannunsa tare da had'e yatsunmu wuri d'aya.
Ya sauke sanyayyar ajiyar zuciya yana kallona ya ce." Amma ni ba babanki ba ne Amina, kin manta ni duniyarki ne fa, ni ne mai k'urewa jin dadinki lamba mai yasa za ki kira ni da baba."
Na danne kunyar da ta taso mini na dube shi da 'yar dariya na ce." Na rasa da wane suna ka dace ina ganin kiranka da Baba shine karshen mutuntawa."
Yana murmushi ya dubi agogon dana daura masa ya gyada kansa yana fad'in." Yau ni dake kamar wasu sabbin masoya, kina so ki shagaltar da ni, jirginmu ya kusa tashi bakwai da minti goma yanzu takwas daidai za mu tashi in sha Allahu kuma yau zan dawo sai mu kàrasa soyayyar don na ga alama addu'ata ce ta kar'bu a kanki."
Na dube shi a hankali haka kawai sai wani tausayinsa ya rufe ni, wai aka ce sai da so ake kishi da tausayi to amma in ba haka ba ai wannan mutumin ba abin tausayi ba ne, mutumin da Allah ya wadata da suttura da jin dadi na gidan duniya.
Hannuna na kai fuskarsa ina dan jan gemunsa da ya yi 2colors fari da baki ya kwanta sosai ya kuma k'awata masa fuskarsa. Na furta." Ka yi kyau sosai, kamar ango."
Ya kanne idonsa yana fad'in." Shine ai ba ki ga na yi gayu ba."
Murmushi na yi tare da fad'in." Haba da Nabilan kenan?"
Ya daga kansa yana kallon yanayina. Na ce." Mai yasa ka boye mini abinda lallai kasan ba zai 'boyu ba."
Ya yi jim yana kallona, sai na girgiza kaina ina ko'karin mayar da k'wallar da take ko'karin zubowa na furta." Jiya Kamalu ya kira ni a waya ya gaya mini abinda ka 'boye mini. Ba ni da bakin godiya Baba, Allah Ya saka da alheri, Ubangiji Allah yadda ka dubi marayun yaran nan ina ro'kon Allah Ya dubi naka abinda ka yi na alheri Allah Ya sanya maka a mizani, na gode na god....! Ban kàrasa ba kukan da nake dannewa ya kufce. Da saurin gaske ya janyo ni jikinsa ya rike ni sosai yana d'an dukan bayana a hankali cikin sigar rarrashi yake fad'in."Daina kuka Amina, ai bake na yi wa ba kaina na taimaka, bakin san da cewa hakkin yaranki a kaina yake ba ai a musulce ni ubansu ne tunda ina auranki, babu buk'atar godiya a tsakaninmu. Yaranki da wani namijin ki ajiye a ranki kamar da ni ne, ai Aminu Salihi da k'arfi da lafiyarsa muka hadu muka nemi dukiyar tare don haka don na sake yin wani abu akan yaran nan ki ce za ki yi mini godiya ko ki yi kuka ni ma na sauke hakki ne, na kuma gode da kyawawan addu'oinki, Allah Ya shirya mini ku bakidaya.
Ri'ke shi na yi sosai a ajikina ina sauke ajiyar zuciya amma hawayen dake zuba daga idona sun kasa tsayuwa.
Ya dago ni yana duban fuskata ya sanya tafin hannunsa yana goge mini a d'an sanyaye ya furta." Ya isa na ce, ki yi shiru humm!, yawwa ko kefa, ki yi mini murmushi nan kin ji tawan"
Murmushi na yi irin mai tafe da kuka na sake rungume shi a jikina kam kukan da k'arfi ya k'wace mini.
Ya diririce sosai yana ta jijjigani "Menene haka Amina na gaya miki akwai abinda yake gabana, kukan na menene haka?"
Na dago kaina Ina kallonsa cikin kukan na ce." Don Allah ka yi hakuri da abinda na dinga yi maka ka ji."
Ya ce." Ni ba ki yi mini komai ba kuma ban ta'ba rikonki ba, ai ni ne zan ce ku yafe mini."
Na ce." Mune dai za ka yafe wa tunda aljannar mu tana kasan kafafunka don Allah ni ma koda na mutu ka dinga yabona kana fad'in alherina irin na Momi."
Ya b'ata rai yana fad'in." Me ya kawo zancen mutuwa kuma?"
Na yi shiru ban ce komai ba domin ni ma jin maganar kawai na yi ta fito daga bakina.
Ya tashi yana gyara babbar rigarsa ni ma na tashi Ina kallonsa yanayinsa ya canza. Na ce." Ka na son ka auri Nabila ko?"
Wani irin duba ya yi mini kafin ya gyada kansa ya mik'a hannu ya debi wayoyinsa dake zube a gadon ya kama hanya zai fita.
Na bi shi da sauri Ina fad'in." Ka tsaya ka ji."
Ya ja ya tsaya yana dan hararata kafin ya ce." Ke ba a fara magana dake a kare lafiya Amina, wanene ya sako Nabila a cikin maganar mu?"
Na ce." Dama zan ce ne na amince idan kana sonta ka aureta wallahi."
A hanzarce ya furta." Ai dama can ku ba ku isa ku hana ni auranta ba idan ina da ra'ayi. Nabila ta bi ta hanyoyi da yawa domin kamun kafa ta had'a kai da su Salim ta nemi Hajiya Ayya mahaifiyar abokina Alhaji Amadu duk akan tana so ta maye gurbin 'yar uwarta na ce a a saboda wasu dalilina. Ba wai tsoronku ne ya hana ni auranta ba."
A sanyaye na ce." To shikkenan, Allah Ya bata wani."
Ya amsa da "Amin yana ko'karin bud'e 'kofar d'akin
Tare muka sauka kasa wanda ya yi daidai da fitowar Hauwa daga dakinta cikin shiri. Ganinsa a shirye da shirin tafiya ya sanya ta ce." Da gaske dai ba za ka yi breakfast din ba kenan?"
Ya ce." Idan na je gidan Hajja sai na yi na gode da kokarinki."
Daga haka sai ya nufi kofar fita a d'an gurguje. Muka had'a baki wurin fad'in." Allah Ya tsare hanya a gaishe da Hajja." Ba tare da ya juyo ba ya amsa da "Za ta ji in sha Allahu rabbi."