← Book details Gudun Aure Part 5 Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 43

Sashe 3

Gudun Aure Part 5 Hausa Novel · about 8 min read

Shiru na yi Ina sauraransa har ya gama maganganunsa. Na ce dalili ne mai karfi ya sanya ni kiranka a daran nan, kuma ni kaina zan ji dadin zuwanka domin ka gyara abinda yake faruwa Kamalu ne da Salim....... Duk abinda yake faruwa na zayyane masa. Ya jima yana nanata maganar da mamaki mai yawa a tare dashi ya ce." Yaushe Salim ya lalace haka, kuma abu ya faru tunda kuruciya saboda rashin hankali ka tara abokai kana gaya musu criminal?" Ya sake maimaita kalmar tabbacin hakan ya bashi mamaki.
Na ce." Kamalu ya ce zai koma kano da zama can wurin Hamusu."
Gyaran murya ya yi tare da cewa." Wannan kuma abinda yake cikin ranki ne shekara da shekaru shine ki ka samu mafaka dalilin wannan matsalar. Na gaya miki Amina idan har Kamalu zamansa zai koma kano to Yusi ma zai bi shi. Nusaiba da Salim Adam amana ne a hannuna. Haka zalika tunda Ina auranki yaranki ma amana ne a hannuna koda ubansu yana raye to balle kuma baya raye. Idan har kina ganin za ki yi iko da abinki ni ban iya ba sai na ce Allah Ya taimaka."
Na ce." To yanzu ya kake so a yi? Kasan dai cigaba da zaman Kamalu a gidan Momi akwai matsala watarana za su iya yin abinda bai da ce ba."
"Babu abinda zai faru, ki kyaleni da yaran dukkaninsu tunda kin gaya mini kin gama aikinki."
Jiki babu karsashi na ce." Shikkenan sai da safe." Sai kawai na kashe wayar domin kuwa jikina yana ba ni kamar ba zai d'auki tsatstsauran mataki ba.
Da lamarin na kwana na kuma wayi gari dashi dalilin da sanya kenan na kasa barin abin iyakacinmu. Na kira anti Yagana na gaya mata halin da ake ciki. Sosai kuwa ranta ya 'baci ta dinga fad'a tana cewa babu lallai babu dole muddin da cin zarafi da cin mutuncin da kuma tozarci Kamal dole ya bar gidan. Arziki ai ba hauka ba ne.
Na ce." Anti Yagana tun farko fa ni dama abinda na guda kenan, shiyasa da matar nan ta bukaci zaman Kamalu a wurinta na dinga gocewa. Karin abin kuma maigidan ya'ki ya fahimceni, wai muddin Kamalu zai bar gidan sai dai su tafi da Yusi wanda na tabbatar da cewar hakan matsala ce babba. Da ya zauna mun yi magana da fahimta tuntuni da tun farko wannan matsalar bata kunno kai ba. Abu na biyu kuma ga yanayin bayanin da Kamalu ya yi mini yadda na fahimta shine shi Salim yana adawa da yadda Allah ya d'aukaka Kamalu fiye dashi, ai nasan yaron yana da kirki tun kafin ya tafi karatu dawowarsa al'amura suka lalace kishi ne shi mai yasa Allah bai yi masa ba."
Ta ce." Wannan kuma Ubangiji zai kalubalanta. Wace irin wahala da gwagwarmaya ce Kamalu bai sha ba. Yanzu kuma Ubangiji Allah Ya d'aukaka darajarsa wannan duka ba dabararmu ba ce ikonsa nd, gaskiya a wannan ga'bar ni ma bana goyan bayan mijinki Kamalu dole ya tafi ya bar musu gidansu idan sun ce ba haka ba sai ya dawo hannunki shine karshen magana.

Na ce." Anti Yagana ni na fi so fa ya koma kanon ko ya dawo nan wurinku hankalina zai fi kwanciya gaskiya, domin ai ko yana gidana ba a kashe matsalar ba tunda duk lokacin da ya fita zai iya yin karo da Salim din kin ga matsalar ai bata mutu ba."
"To ni da kaina zan kira Yallabai din a waya na bashi shawara yadda za a yi.
Jin haka ya sanya na ce." Kada ki kira shi yanzu anti Yagana mu bari ya zo mu ga hukuncin da zai yanke idan babu adalci sai ki yi masa magana."
Ta ce." Shikkenan haka za a yi in sha Allah, na manta ma ban gaya miki ba shekaran jiya amaryar Babandi matar da ya aura ta uku ta haihu." A takaice na ce.'' A yi masa barka Allah Ya raya, domin ni yanzu ko lambarsa ma ba ni da ita yadda maigidan ya tsaneshi haka ya tsani mutuwarsa shiyasa na goge lambarsa daga wayata a gabad'aya duk domin a zauna lafiya.

**
Bayan sati biyu al'amura suna cigaba da tafiya da dad'i babu dad'i. Har zuwa lokacin Salim bai kyale Kamalu ba. Kusan kullum da b'acin rai yake shigo mini duk da yana ko'karin daurewa amma ina fahimta. Ha'kurina yana daf da k'arewa domin tun ranar da na kira maigidan a waya na gaya masa abinda yake faruwa bai sake nema na da maganarba duk kuwa da cewa kusan kullum sai mun yi bidiyon call. Ni ma ban sake tayar da maganar ba na bari ne kamar yadda ya ce mu jira zuwansa. Amma koyaushe idan na dubi Kamalu na ga yadda ya rage walwala da kuzari zuciyata takan yi zafi. Ina dalili haka kawai saboda gudun b'acin ran wani a 'kuntata zuciyar yaro. Babu lallai fa babu dole muddin ba zai d'auki mataki ba wallahi sai Kamalu ya tafi ya bar garin da gidan gabad'aya.
Ranar litinin da yamma suka sauka shi da Hauwa. Baiwar Allah ta kuma samo wani cikin domin yanayinta kadai ya tabbatar mini da cewa laulayi take yi ta yi mugun haske dama idan tana da ciki d'ashewa take yi. Macace mai kwainika Minal na da wata goma sha takwas. Allah Ya sa tana da san girma, tana yawo da kafafunta da yake abincin gwangwani take ci a can ta zama rusheshiya kataf-kataf haka take yawo uban yana tsokanarta da 'yar sukuta. Wai na washeta har ta fi su Hassana girma jiki tunda su jikin irin nasa ne. Kwana biyu da zuwansu na fahimci rashin jituwa a tsakaninsu. Kamar ma basa magana da juna. Na yi dai shiru ina kallon ikon Allah. Ita yini ma take yi a d'aki sai yamma take fitowa falo shi kuma har ya yi kwana biyunsa a wajena bai ce mini komai ba.
Na cika da mamaki sosai. Lallai ma wannan mutumin wato maganar tabi shanun sarki kenan Salim ya yi daidai babu kuskure akan abinda yake yi.
Ba zan lamunta ba domin kuwa har yanzu a cikin matsalar ake sai abinda ma ya yi gaba. Kamalu bai rasa madogara ba hakama Yusi idan har ba zai gyara abinda yake faruwa ba to na yarda ya ba ni yarana su kuma can hannun Babansu Hamusu.
Cikin wannan nazarin Hauwa ta shigo d'akina ta same ni. Ta zauna gefan gado tana fad'in." Ko jikin ne?" Na tashi zaune Ina fad'in." A, a ni kam ai na warware na bar miki Hauwa."
Kwafa ta yi tare da cewa." Ban ji dad'in shigar cikin nan ba wallahi.''
Na dubeta a tsanake tare da cewa." Mai yasa Hauwa ki godewa Allah da fatan samun masu albarka."
"Humm!" abinda ta ce kenan kafin ta ce." Ban shigo domin na tunzuraki ko tayar da husuma ba. Idan kin lura da yanayin yadda muka zo da ni maigidan babu dadi don wallahi mugun haushinsa nake ji."
Na ce." Menene kuma ya kamata ki manta da matsalar matar nan Hauwa, ki yi ta kanki haihuwa ta uku za ki yi da mutumin nan duk abinda zai yi ya je ya yi haka ya ga zai iya."

"Wallahi Amina ko kaffara ba zan yi ba matar nan ba haka ta bar mutumin nan ba."
"Mai yasa ki ka ce haka Hauwa, zato zunubi ne fa Koda ya kasance gaskiya ne?"
[12/16, 7:43 PM] bintaumarabbale: 102
"Amina maganar gaskiya zan gaya miki na gaji da zaman nan da muke yi na rashin 'yanci da kaskanci wallahi tallahi ba zan jiya jure ba, wannan shine dalilin ma da ya sanya ki ka ji na ce ina b'akinciki da takaicin samuwar wannan cikin na jikina, in banda ina gudun sa'bawa Allah wallahi da sai na zubar da shi."
Da mamaki mai yawa a tare da ni na ce." Hauwa mai ya yi zafi haka, ha'kuri fa ya zame miki dole na farko mutumin nan d'an uwanki ne kuma mijinki uban yaranki, idan kin rabu dashi ki auri wa kenan, ke ce ya kamata ki zauna dashi Hauwa saboda haduwar jini da kuma zuri'ar da take tsakaninku."
Cike da takaici ta furta." Shi ai baya ganin yadda muke yin hakuri Amina, a ce mutum bashi da wani mutunci da daraja. Shikkenan sai ka ajiye mata uku ka za'bi daya ka fifita saboda wata banzar hujja."
Dariya na yi na gane dama duk wannan hayaniyar da take yi akan Momi ne, har yanzu ita ta kasa d'auke kanta daga sha'aninsu. Na ce." Hauwa da za ki d'auki shawarata wallahi da kin daina girmama al'amarin nan kin sanya shi a ranki, ki yi abinda yake gabanki kawai ki rabu da duk abinda zai yi, ai duk wanda ya gyara ya sani kuma duk wanda ya 'bata ya sani."

Shiru ta yi tana kallona kafin ta gyada kanta ta ce." Idan kuwa har ina da hakki to Allah Ya isa ban yafe ba wallahi, domin ni don ba yadda zan yi ne na ha'kura da wannan sintirin haka kawai sai ta toge da ri'ke mana yara ita tana kamile a waje daya saboda shafaffiyace da mai."
Na ce." Ai kin fi ta samun ladan aure Hauwa, don Allah maganar nan ta mutu haka haba."
"Magana ba za ta mutu ba Amina, ba ni na haifi Kamalu ba amma zahiri sai inda karfina ya kare a kan sharrin da yaron nan Salim ya yi masa."
Na dubeta a nutse." Wane irin sharri kuma Hauwa?"
Shiru ta yi tana kallona da yanayi na damuwa sai ta gyada kanta cike da b'acin rai ta ce." Abin da akwai daure kai Amina, nasan kuma ba zai gaya miki ba saboda yadda ya nuna kamar ya yarda da maganar yaron. Nuna masa hakan ba daidai ba ne ya yi aiki da maganar mutum d'aya sai ya janyo mana rikici shine fa muke ta yi har yanzu ba ma ga miciji"
Chapter 3 · 0% Book details