Sashe 40
Gudun Aure Part 5 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Satinsa hud'u ya dawo a cikin kwanakin bai fi sau hud'u muka yi waya ba. Ya dawo a tsananin bukace lokacin ni kuma laulayi ya lafkar da ni domin abinda nake zargi ya tabbata ya kuma bayyana kansa domin mai azaba ne da son kad'aici na tsiri zaman d'aki da rashin son hayaniya da k'unci. Sai masifar son abinda ya danganci yaji da manja. Koda ya tabbatar da cewa ciki ne da ni ya yi murna sosai ya fito da farincikinsa kowa ya sheda hakan. Kuma ya rage takura mini a duk ranar girkina saboda ya fahimci ba ni son damu abin ma gabad'aya baya ba ni sha'awa. Sai ya zamana bai fi sau biyu yake kwanciya da ni a sati ba.
Laulayi sosai ya tisa ni a gaba har da su karin ruwa kusan sau uku. Anti Yagana ta ce mini za ta zo dubani domin da muka yi bidiyo call ta tsorata da ganin yadda na zabge. Na ce ta yi zamanta ba sai ta zo ba tunda itama tana tare da mai juna biyun Fadila tunda watan haihuwar ya tsaya a ka dawo da ita gida tunda ta fari ce. Hatta da Sahura ba ta san ina da ciki ba, itama anti Yagana yawan yin bidiyon call din da muke yi ne ta fahimta shine babu yadda na iya na gaya mata.
Wataran alhamis da yamma ina kwance a d'aki da busheshshiyar agwalima a bakina ina tsotsa wata masifa ta ciki gari na waye wa da bushshiyar agwalima nake farawa kafin nasa komai a cikina ina nan da su a bushe da yawa bata yanke mini tunda akai-akai nake aika Masa'udu ya sayo mini.
Kamalu ya kira ni a waya muka gaisa sosai cikin Kamala da nutsuwa na ji ya ce." Mama amma dai za ki zo walimar bude makarantar da Baba ya gina mini ko."
Da mamaki a tare da ni na ce." Makaranta kuma Kamalu yaushe aka yi hakan ai ban sani ba ."
Ya d'an yi murmushi kafin ya ce." Ai dama tun da na ji ba ki yi magana ba na ce wata'kila ba ki sani ba. Mama Baba ne ya gina mini babbar makarantar islamiyya da massalaci a hade anan unguwar Kadawa gobe Juma'a in sha Allahu za a yi bikin bud'ewa."
Na yi shiru ina mamaki ko da wasa bai ta'ba gaya mini ba, nasan dai da maganar tafiyarsa Kano gobe amma bai ce mini ga dalili ba
Na ce " wallahi ban sani ba Kamalu don bai gaya mini ba, na ta ya ka murna sosai kuma na yi addu'a Ubangiji Allah Ya yi maka jagoranci
Ya amsa cikin jin dadi ya cigaba da cewa." Ai yana jin dadin irin yadda yake ganin bidiyona yana yawo a kafafan sadarwa. Ya ce mini har wasu daga cikin abokanansa suna tura masa tare da taya shi murna. Da ya tambayeni menene burina a duniya na gaya masa makaranta islamiyya da massalacin da zan cigaba da yad'a da'awata da sauran koyarwar addinin musulunci."
Na gyad'a kaina ina mamaki duk yadda aka yi hakan ban sani ba na ce." Da yake ni social media bata dame ni ba yanzu kuma dai ba'a ta'ba gaya mini ga wani bidiyonka ba. Kwanaki can dai Sahura ta ce mini Maigidanta ya ganka tare da wannan malamin shaik ma'kari a lokacin da ya zo gaisuwar ta'aziyya. Daga sannan dai ban sake jin wani labari ba."
Ya ce." Mama ai adduarki ta kar'bu alhamdulillahi. Mutane sun fara kar'bar abinda muke yi kuma suna mubayaa sannu a hankali za mu fara shiga kauyika domin wattanin da suka shige mun yi wa shaik Abdullahi G kaya rakiya zuwa gombe can wani kauye da arna suka yawaita wallahi ni kaina mama na musuluntar da mutum sama da ashirin a kauyen."
Cike da farinciki na ce." Alhamdulillahi! lallai kana tare da nasara da d'aukaka Kamalu ka dage ka yi aiki tukuru ka kuma kula sosai kada ka shiga rigar da ba taka ba. Kada na ji ana fad'a da kai akan addini. Ka yi iya yinka kamar yadda annabin rahama ya fad'a shiriya ta Allah ce."
Ya ce." In sha Allahu rabbi Mama zan kula sosai kuma yanzu zan turo miki irin bidiyon da nake yi ina sanyawa a shafukana na social media YouTube fecebook TikTok Instagram Whasap."
Na ce." To ka turo mini na k'alla, Ubangiji Allah Ya sanya albarka Kamalu Allah Ya sa kafi haka."
Ya amsa da "Amin Ya Allah "
Na tashi zaune sosai a lokacin da ya turo mini tarin bidiyos din ta whasap na dinga bud'ewa ina kalla. Na farko yana koya yadda ake yin alwala na biyu yana koya yadda ake yin temama ga matafiya. Na uku yana koya yadda ake wankan janaba dana haila. Na uku yana koya yadda ake yin sallah tun daga kabbara tsayuwa ruku'u sujjada zaman tahiyya. Na dinga maimaita kallon bidiyos din hawaye suna silalowa a kuncina. Ni kaina na rasa hawayen menene na farinciki ne. Kamalu na ya zama gwani ya zama alarama kur'ani izifi sittin akan shi da ka yake d'auko aya ya dire ta. Na daga hannu sama ina kuka ina fad'in."Allah na gode maka, lallai kai ne masananin abinda yake boye. Na gode maka da ba ka sanya ni kaucewa hanya akan wannan bawa naka ba. Allah Yadda ka shirya mini yarona Kamalu ina ro'konka ka shirya sauran yaran al'ummarka."
Laulayi sosai ya tisa ni a gaba har da su karin ruwa kusan sau uku. Anti Yagana ta ce mini za ta zo dubani domin da muka yi bidiyo call ta tsorata da ganin yadda na zabge. Na ce ta yi zamanta ba sai ta zo ba tunda itama tana tare da mai juna biyun Fadila tunda watan haihuwar ya tsaya a ka dawo da ita gida tunda ta fari ce. Hatta da Sahura ba ta san ina da ciki ba, itama anti Yagana yawan yin bidiyon call din da muke yi ne ta fahimta shine babu yadda na iya na gaya mata.
Wataran alhamis da yamma ina kwance a d'aki da busheshshiyar agwalima a bakina ina tsotsa wata masifa ta ciki gari na waye wa da bushshiyar agwalima nake farawa kafin nasa komai a cikina ina nan da su a bushe da yawa bata yanke mini tunda akai-akai nake aika Masa'udu ya sayo mini.
Kamalu ya kira ni a waya muka gaisa sosai cikin Kamala da nutsuwa na ji ya ce." Mama amma dai za ki zo walimar bude makarantar da Baba ya gina mini ko."
Da mamaki a tare da ni na ce." Makaranta kuma Kamalu yaushe aka yi hakan ai ban sani ba ."
Ya d'an yi murmushi kafin ya ce." Ai dama tun da na ji ba ki yi magana ba na ce wata'kila ba ki sani ba. Mama Baba ne ya gina mini babbar makarantar islamiyya da massalaci a hade anan unguwar Kadawa gobe Juma'a in sha Allahu za a yi bikin bud'ewa."
Na yi shiru ina mamaki ko da wasa bai ta'ba gaya mini ba, nasan dai da maganar tafiyarsa Kano gobe amma bai ce mini ga dalili ba
Na ce " wallahi ban sani ba Kamalu don bai gaya mini ba, na ta ya ka murna sosai kuma na yi addu'a Ubangiji Allah Ya yi maka jagoranci
Ya amsa cikin jin dadi ya cigaba da cewa." Ai yana jin dadin irin yadda yake ganin bidiyona yana yawo a kafafan sadarwa. Ya ce mini har wasu daga cikin abokanansa suna tura masa tare da taya shi murna. Da ya tambayeni menene burina a duniya na gaya masa makaranta islamiyya da massalacin da zan cigaba da yad'a da'awata da sauran koyarwar addinin musulunci."
Na gyad'a kaina ina mamaki duk yadda aka yi hakan ban sani ba na ce." Da yake ni social media bata dame ni ba yanzu kuma dai ba'a ta'ba gaya mini ga wani bidiyonka ba. Kwanaki can dai Sahura ta ce mini Maigidanta ya ganka tare da wannan malamin shaik ma'kari a lokacin da ya zo gaisuwar ta'aziyya. Daga sannan dai ban sake jin wani labari ba."
Ya ce." Mama ai adduarki ta kar'bu alhamdulillahi. Mutane sun fara kar'bar abinda muke yi kuma suna mubayaa sannu a hankali za mu fara shiga kauyika domin wattanin da suka shige mun yi wa shaik Abdullahi G kaya rakiya zuwa gombe can wani kauye da arna suka yawaita wallahi ni kaina mama na musuluntar da mutum sama da ashirin a kauyen."
Cike da farinciki na ce." Alhamdulillahi! lallai kana tare da nasara da d'aukaka Kamalu ka dage ka yi aiki tukuru ka kuma kula sosai kada ka shiga rigar da ba taka ba. Kada na ji ana fad'a da kai akan addini. Ka yi iya yinka kamar yadda annabin rahama ya fad'a shiriya ta Allah ce."
Ya ce." In sha Allahu rabbi Mama zan kula sosai kuma yanzu zan turo miki irin bidiyon da nake yi ina sanyawa a shafukana na social media YouTube fecebook TikTok Instagram Whasap."
Na ce." To ka turo mini na k'alla, Ubangiji Allah Ya sanya albarka Kamalu Allah Ya sa kafi haka."
Ya amsa da "Amin Ya Allah "
Na tashi zaune sosai a lokacin da ya turo mini tarin bidiyos din ta whasap na dinga bud'ewa ina kalla. Na farko yana koya yadda ake yin alwala na biyu yana koya yadda ake yin temama ga matafiya. Na uku yana koya yadda ake wankan janaba dana haila. Na uku yana koya yadda ake yin sallah tun daga kabbara tsayuwa ruku'u sujjada zaman tahiyya. Na dinga maimaita kallon bidiyos din hawaye suna silalowa a kuncina. Ni kaina na rasa hawayen menene na farinciki ne. Kamalu na ya zama gwani ya zama alarama kur'ani izifi sittin akan shi da ka yake d'auko aya ya dire ta. Na daga hannu sama ina kuka ina fad'in."Allah na gode maka, lallai kai ne masananin abinda yake boye. Na gode maka da ba ka sanya ni kaucewa hanya akan wannan bawa naka ba. Allah Yadda ka shirya mini yarona Kamalu ina ro'konka ka shirya sauran yaran al'ummarka."