Sashe 2
Gudun Aure Part 5 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mama ba zan rufe miki ba, tunda Salim ya dawo daga karatu yake yi mini wasu abubuwa na rashin kyautawa da nuna k'yama. Ba zai ci abinci tare da ni ba, ba zai kwanta d'akin da nake ba, haka zalika a cikin kwana biyun nan baya bina jam'in sallah a massalaci, ina kallonsa ya ke tafiya wani massalacin na daban. Ban san menene dalili ba, Mama amma kuma baya nunawa Yusi k'yama, wannan dalilin ya sanya ni yanke shawarar barin gidan gabad'aya domin ba na so watarana na kasa jurewa muddin a haka zamu dinga tafiya dashi babu kyakykyawar ala'ka, babu musabaha da girmama juna sai k'yama, zuciyata ba zata iya jurewa ba, Ina jin tsoron mu yi fad'a hakan ya ta'ba zumuncinku da zamantakewarku. Kin ga Momi babu komai a tsakanina da ita sai alheri Ina sonta sosai wallahi irin yadda nake sonki Mama, amma ba na so mu yi abinda duka zai bata muku rai shine dalilana."
Nasan dama ruwa baya tsami banza. Amma kuma sanin da na yi wa yaron a baya kafin ya tafi karatun ba haka yake ba. Yaro ne mai nutsuwa da son mutane irin d'an uwansa Adam ga barkwanci. Nusaiban dai ce mara fuska.
Na daure ban nuna b'acin raina a fili ba na ce." Kenan ba ku taba magana ba tunda ya dawo?"
Ya ce." Idan na mik'a masa hannu domin musabaha baya kar'ba. D'azu da safe a gaban Momi ya yi. Hakan ya 'bata mata rai sosai ta yi masa fad'a. Shine ya tashi ya fita bai dawo ba har na fito, wallahi mama kada ki so ki ga yadda hankalinta ya tashi, shine take cewa kada na gaya miki."
Shiru na yi ina nazarin al'amarin. Kamalu bai yi lefi ba domin kuwa anan ya yi aiki da hankali da kuma iliminsa. Na kuma ji dad'in abinda ya yi da har ya iya danne zuciyarsa bai biye masa ba. Shawarar da ya yanke itace mafita muddin kuwa ana son zaman lafiya. Idan har Salim bai gane abinda yake yi kuskure ba ne, to babu mamaki wataran gagarimar matsala ta faru tunda ni nasan wanene Kamalu a fagen zuciya.
Amma yadda zan yi na sanar da maigidan halin da ake ciki shine matsalata. Na riga nasan rikice ne akwance domin kuwa baya d'aukar abinda ya shafi matarsa da wasa. Maganarsa daya amanarsa ce 'ya'yanta ma amana ne, a wannan ga'bar kuwa ya zame masa dole ya bincika domin tabbatar da gaskiyar abinda yake faruwa ya kuma gyara matsalar kafin ta yi nisa.
[12/16, 7:43 PM] bintaumarabbale: 101
Na ce." Abinda za a yi yanzu shine ka d'an daure kad'an, ai ni ka burgeni sosai da har ka yi irin wannan tunanin wannan ya sake nuna mini cewa Kamaluna ya bambamta sosai da wanda na sani a baya. Ka cigaba da yi masa magana kada ka biye masa ni kuma zan yi magana da Baban nasan dai haka kawai ai ba zaka kirkiri karya don jin dadi ka gaya mini ba ko?''
"Wallahi Mama babu karya cikin maganata gaskiyar abinda yake faruwa na gaya miki, menene ribata idan na yi k'aryar kuma me ya yi mini da zan 'bata shi."
Na ce." To kada nunawa Momi damuwarka a fuska ka daure ka ji ko."
Ya ce." In sha Allah Mama.
Daga haka sai muka bar maganar muka shiga wata ina d'an jansa da wasa duk domin ganin ya manta abinda yake damunsa. Amma zahiri ni a can 'kasan zuciyata cike nake da fargabar yadda zan tunkari maigidan da maganar. Wala'ala ya fahimceni, wala'ala kuma ya juya mini manufa, amma dai tun yanzu ya kamata a ce ayi wa tufkar hanci kafin lamarin ya yi tsamari rayuka su zo suna 'baci.
Daf da magriba ya tashi ya fita da zummar shirin shiga massalaci.
Bayan kwana biyu ina cikin nazari domin har yanzu na kasa tsayar da abinda nake ganin shine daidai. Ba na so na yi magana ne a ce na goyi da bayan yarona wata'kila shi kansa zai iya ganin haka shiyasa hankalina bai kwanta ba har yanzu sai dai na gaza daurewa na sanar da Baba Tabawa abinda yake faruwa domin kuwa macace mai tsinkaye da nisan tunani.
Ta jima tana jimantawa kafin ta ce." Ai shurun ba shine mafita ba, gwara ki gaya masa tunda shine jagoran kowa a gidan ya yi wa tufkar hanci kada lamari ya yi k'wari hatsaniya ta tashi ya ce mai yasa ba a gaya masa ba. Ina ganin duk wanda zai ce kin so kanki da zummar kawo gyara to ya zalinceki domin kuwa abinda ki ka yi shine daidai, ai ba ki za'bi Kamalu kin fifita akan Salim ba, duka naki ne kamar yadda itama Momin take nunawa, to ya kamata a ce wannan 'barakar da take ko'karin kunnowa an yi maganinta.
Ajiyar zuciya na sauke bayan duk na gama sauraran maganganunta. Na ce." Shikkenan Baba, in sha Allah zan sanar da shi halin da ake ciki duk kuma yadda muka yi aki ji."
Ta ce." To shikkenan, Allah Ya maganta."
To daddare ina d'aki a kwance misalin takwas da rabi ya shigo mini cikin tsananin b'acin rai. Na tashi zaune da sauri gabana na fad'uwa. Ya zauna samar kujerar madubi na ce." Kai lafiya Kamalu."
"Mama barka da dare." Da abinda ya fara kenan. Na amsa a takaice na ce." Menene?"
Duk dauriyarsa sai da muryarsa ta yi rawa ya ce." Mama ba zan iya ba, ba zan iya jurewa ba, zan tafi kano gobe domin kuwa Salim baya neman zaman lafiya da ni."
"Mai ya yi maka kuma?" Na tambayeshi jikina sanyi kalau domin kuwa wani yanayi na shiga na tsananin tausayin yaron ba komai ne ya janyo hakan ba sai maraici da rashi domin kuwa duk abinda Salim yake yi yana yi ne domin ya ga a cikin rigar arziki sa yake.
"Salim tare da abokansa suke yi mini dariya har na ji daya daga cikinsu yana kirana da 'kolo, dayan kuma yana cewa mini criminal." Sai hawaye suka fara kasa tsare a kumatunansa.
Zuba masa ido na yi Ina kallo a yayin da hawayen ke ta zarya a dakalin fuskarsa bai goge ba, ni ma kuma ban ce masa ya yi shiru ba sanin da na yi cewar kukan shine zai sassauta masa takaicin abinda aka yi masa.
Idan an kira shi da 'kolo ai ba damuwa ba ne, ni na ji dad'i ma da ya zama 'kolon mahaddaci kuma marubucin al'kur'ani. Kalmar criminal din ce ta hargitsa dukkanin lissafina, Salim abin har ya kai haka. Abinda ya faru shekaru kusan shida yaro ya samu nutsuwa ya zama mutum shine yanzu za a tayar da shi.
Cikin jan ajiyar zuciya ya ce." Mama Salim na b'akinciki da yadda Allah ya yi mini jama'a a area nan, sannan yana kishi sosai ya ga na bude massalaci manya mutane na bina sallah suna gaisawa da ni. Wannan na ji da kunnena yana fad'in duk wanda ya bi b'arawo sallah shi ma bashi da maraba da 'barawo, Mama yaushe wannan sunan zai goge a tarihin kuruciyata."
Na ji kwalla ta ciko mini ido. Na daure ban yadda ta zuba ba, na ce." To share hawayenka ka daina kuka ka ajiye abinda yake faruwa a matsayin cigaba, domin kuwa haka siddin ba zaka cimma wata nasara ba tare da kalubale ba. Ita hassadar ai itace matakin komai. Kada ma ka damu, kuma ina mai tabbatar maka da cewa watarana Salim zai bi ka salla, zai kuma nemi fatawa a wurinka, wannan ni ce na gaya maka, domin kuwa Ina nan ina roka maka d'aukaka da shura ta fanninin addini anan gidan duniya, Kamalu idan Allah Ya yarda duniya da mutanan dake cikinta za su amfana da kai."
Hannu yasa ya goge hawayen dake zuba a kumatunsa. Na ce." Ka kyale mini komai a hannuna, ka ji ko ka cigaba da hakuri, ni kaina a wannan ga'bar ba zan ha'kura ba dole a yi wani abu kai, amma kada ka nunawa Momi komai, ka bar abin a zuciyarka."
A sanyaye ya ce." Shikkenan Mama, zan yi yadda ki ka ce din, amma ni ina so na koma can kano zan fi samu nutsuwa cigaba da gudanar da neman ilimina."
Na ce." Idan har hakan shine alheri za ka koma Kamalu, ka cigaba da addu'a ka kuma bar maganar tsakanina da kai."
To a daran na nemi maigidan a waya duk da nasan ba sosai yake amsa waya da daddare ba amma yadda nake jin zuciyata ba zan iya bari sai gari ya waye ba. Wayar ta katse bai daga ba sai na yi masa text na cewa Ina son magana dashi yanzu.
Wajan goma da rabi ya kira ni da kansa. Na daga muka gaisa a nutse.
Na ce." Baba ina son magana da kai amma kada ka juya mini don girman Allah da Annabi ka dubeta ta fuskar hankali da maslaha."
A nutse ya ce." To ina jinki ai ni mai hankali ne ba mahaukaci ba, kada dai ki ce mini kin yi 'bari domin kwana biyun nan mafarkai nake yi marasa kan gado, Ina ganin ma farkon watan nan za mu zo."
Na ce." Ban yi 'bari ba, amma ka sani cewa ni da kai ba mu da ikon komai akan abinda Allah Ya zartar. Idan har kaddara ta gifta cikin ya samu matsala ba za ka d'auki kaddara ba kenan?"
Ya ce." Zan d'auka mana, ai mafarkan da nake yi ne ya sanya ki ka ji na yi miki wannan maganar. Na tuba ga Allah duk yadda ya yi daidai ne."
Nasan dama ruwa baya tsami banza. Amma kuma sanin da na yi wa yaron a baya kafin ya tafi karatun ba haka yake ba. Yaro ne mai nutsuwa da son mutane irin d'an uwansa Adam ga barkwanci. Nusaiban dai ce mara fuska.
Na daure ban nuna b'acin raina a fili ba na ce." Kenan ba ku taba magana ba tunda ya dawo?"
Ya ce." Idan na mik'a masa hannu domin musabaha baya kar'ba. D'azu da safe a gaban Momi ya yi. Hakan ya 'bata mata rai sosai ta yi masa fad'a. Shine ya tashi ya fita bai dawo ba har na fito, wallahi mama kada ki so ki ga yadda hankalinta ya tashi, shine take cewa kada na gaya miki."
Shiru na yi ina nazarin al'amarin. Kamalu bai yi lefi ba domin kuwa anan ya yi aiki da hankali da kuma iliminsa. Na kuma ji dad'in abinda ya yi da har ya iya danne zuciyarsa bai biye masa ba. Shawarar da ya yanke itace mafita muddin kuwa ana son zaman lafiya. Idan har Salim bai gane abinda yake yi kuskure ba ne, to babu mamaki wataran gagarimar matsala ta faru tunda ni nasan wanene Kamalu a fagen zuciya.
Amma yadda zan yi na sanar da maigidan halin da ake ciki shine matsalata. Na riga nasan rikice ne akwance domin kuwa baya d'aukar abinda ya shafi matarsa da wasa. Maganarsa daya amanarsa ce 'ya'yanta ma amana ne, a wannan ga'bar kuwa ya zame masa dole ya bincika domin tabbatar da gaskiyar abinda yake faruwa ya kuma gyara matsalar kafin ta yi nisa.
[12/16, 7:43 PM] bintaumarabbale: 101
Na ce." Abinda za a yi yanzu shine ka d'an daure kad'an, ai ni ka burgeni sosai da har ka yi irin wannan tunanin wannan ya sake nuna mini cewa Kamaluna ya bambamta sosai da wanda na sani a baya. Ka cigaba da yi masa magana kada ka biye masa ni kuma zan yi magana da Baban nasan dai haka kawai ai ba zaka kirkiri karya don jin dadi ka gaya mini ba ko?''
"Wallahi Mama babu karya cikin maganata gaskiyar abinda yake faruwa na gaya miki, menene ribata idan na yi k'aryar kuma me ya yi mini da zan 'bata shi."
Na ce." To kada nunawa Momi damuwarka a fuska ka daure ka ji ko."
Ya ce." In sha Allah Mama.
Daga haka sai muka bar maganar muka shiga wata ina d'an jansa da wasa duk domin ganin ya manta abinda yake damunsa. Amma zahiri ni a can 'kasan zuciyata cike nake da fargabar yadda zan tunkari maigidan da maganar. Wala'ala ya fahimceni, wala'ala kuma ya juya mini manufa, amma dai tun yanzu ya kamata a ce ayi wa tufkar hanci kafin lamarin ya yi tsamari rayuka su zo suna 'baci.
Daf da magriba ya tashi ya fita da zummar shirin shiga massalaci.
Bayan kwana biyu ina cikin nazari domin har yanzu na kasa tsayar da abinda nake ganin shine daidai. Ba na so na yi magana ne a ce na goyi da bayan yarona wata'kila shi kansa zai iya ganin haka shiyasa hankalina bai kwanta ba har yanzu sai dai na gaza daurewa na sanar da Baba Tabawa abinda yake faruwa domin kuwa macace mai tsinkaye da nisan tunani.
Ta jima tana jimantawa kafin ta ce." Ai shurun ba shine mafita ba, gwara ki gaya masa tunda shine jagoran kowa a gidan ya yi wa tufkar hanci kada lamari ya yi k'wari hatsaniya ta tashi ya ce mai yasa ba a gaya masa ba. Ina ganin duk wanda zai ce kin so kanki da zummar kawo gyara to ya zalinceki domin kuwa abinda ki ka yi shine daidai, ai ba ki za'bi Kamalu kin fifita akan Salim ba, duka naki ne kamar yadda itama Momin take nunawa, to ya kamata a ce wannan 'barakar da take ko'karin kunnowa an yi maganinta.
Ajiyar zuciya na sauke bayan duk na gama sauraran maganganunta. Na ce." Shikkenan Baba, in sha Allah zan sanar da shi halin da ake ciki duk kuma yadda muka yi aki ji."
Ta ce." To shikkenan, Allah Ya maganta."
To daddare ina d'aki a kwance misalin takwas da rabi ya shigo mini cikin tsananin b'acin rai. Na tashi zaune da sauri gabana na fad'uwa. Ya zauna samar kujerar madubi na ce." Kai lafiya Kamalu."
"Mama barka da dare." Da abinda ya fara kenan. Na amsa a takaice na ce." Menene?"
Duk dauriyarsa sai da muryarsa ta yi rawa ya ce." Mama ba zan iya ba, ba zan iya jurewa ba, zan tafi kano gobe domin kuwa Salim baya neman zaman lafiya da ni."
"Mai ya yi maka kuma?" Na tambayeshi jikina sanyi kalau domin kuwa wani yanayi na shiga na tsananin tausayin yaron ba komai ne ya janyo hakan ba sai maraici da rashi domin kuwa duk abinda Salim yake yi yana yi ne domin ya ga a cikin rigar arziki sa yake.
"Salim tare da abokansa suke yi mini dariya har na ji daya daga cikinsu yana kirana da 'kolo, dayan kuma yana cewa mini criminal." Sai hawaye suka fara kasa tsare a kumatunansa.
Zuba masa ido na yi Ina kallo a yayin da hawayen ke ta zarya a dakalin fuskarsa bai goge ba, ni ma kuma ban ce masa ya yi shiru ba sanin da na yi cewar kukan shine zai sassauta masa takaicin abinda aka yi masa.
Idan an kira shi da 'kolo ai ba damuwa ba ne, ni na ji dad'i ma da ya zama 'kolon mahaddaci kuma marubucin al'kur'ani. Kalmar criminal din ce ta hargitsa dukkanin lissafina, Salim abin har ya kai haka. Abinda ya faru shekaru kusan shida yaro ya samu nutsuwa ya zama mutum shine yanzu za a tayar da shi.
Cikin jan ajiyar zuciya ya ce." Mama Salim na b'akinciki da yadda Allah ya yi mini jama'a a area nan, sannan yana kishi sosai ya ga na bude massalaci manya mutane na bina sallah suna gaisawa da ni. Wannan na ji da kunnena yana fad'in duk wanda ya bi b'arawo sallah shi ma bashi da maraba da 'barawo, Mama yaushe wannan sunan zai goge a tarihin kuruciyata."
Na ji kwalla ta ciko mini ido. Na daure ban yadda ta zuba ba, na ce." To share hawayenka ka daina kuka ka ajiye abinda yake faruwa a matsayin cigaba, domin kuwa haka siddin ba zaka cimma wata nasara ba tare da kalubale ba. Ita hassadar ai itace matakin komai. Kada ma ka damu, kuma ina mai tabbatar maka da cewa watarana Salim zai bi ka salla, zai kuma nemi fatawa a wurinka, wannan ni ce na gaya maka, domin kuwa Ina nan ina roka maka d'aukaka da shura ta fanninin addini anan gidan duniya, Kamalu idan Allah Ya yarda duniya da mutanan dake cikinta za su amfana da kai."
Hannu yasa ya goge hawayen dake zuba a kumatunsa. Na ce." Ka kyale mini komai a hannuna, ka ji ko ka cigaba da hakuri, ni kaina a wannan ga'bar ba zan ha'kura ba dole a yi wani abu kai, amma kada ka nunawa Momi komai, ka bar abin a zuciyarka."
A sanyaye ya ce." Shikkenan Mama, zan yi yadda ki ka ce din, amma ni ina so na koma can kano zan fi samu nutsuwa cigaba da gudanar da neman ilimina."
Na ce." Idan har hakan shine alheri za ka koma Kamalu, ka cigaba da addu'a ka kuma bar maganar tsakanina da kai."
To a daran na nemi maigidan a waya duk da nasan ba sosai yake amsa waya da daddare ba amma yadda nake jin zuciyata ba zan iya bari sai gari ya waye ba. Wayar ta katse bai daga ba sai na yi masa text na cewa Ina son magana dashi yanzu.
Wajan goma da rabi ya kira ni da kansa. Na daga muka gaisa a nutse.
Na ce." Baba ina son magana da kai amma kada ka juya mini don girman Allah da Annabi ka dubeta ta fuskar hankali da maslaha."
A nutse ya ce." To ina jinki ai ni mai hankali ne ba mahaukaci ba, kada dai ki ce mini kin yi 'bari domin kwana biyun nan mafarkai nake yi marasa kan gado, Ina ganin ma farkon watan nan za mu zo."
Na ce." Ban yi 'bari ba, amma ka sani cewa ni da kai ba mu da ikon komai akan abinda Allah Ya zartar. Idan har kaddara ta gifta cikin ya samu matsala ba za ka d'auki kaddara ba kenan?"
Ya ce." Zan d'auka mana, ai mafarkan da nake yi ne ya sanya ki ka ji na yi miki wannan maganar. Na tuba ga Allah duk yadda ya yi daidai ne."