Sashe 27
Gudun Aure Part 5 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Ba ni da niyyar sanar da kowa wannan lamarin a ganina hakan kamar bai shafe ni ba, yaro da na d'auka tunda ta tafi ta bar shi zan yi iyakar bakin kokarina. Amma tabbas Hauwa rikici da gangami ta shiryawa kanta kuma a zahiri naga wautarta domin ta aikata abu irin na marasa sanin ya kamata.
Cikin hukuncin Allah lafiya lau muka kwana da yaron bai yi kuka ba domin kuwa Baba Tabawa ta bada dukkanin kulawarta a kansa. Ni kaina cewa ta yi na tafi na kwanta za ta kula da shi. Ban kwanta ba kuwa sai da na nuna mata yadda za ta dama masa madararsa idan Allah ya sa ya farka ta ajiye komai a kusa da ita wanda za ta buk'ata.
Da safe kuwa kafin na fito ta shirya shi tsaf yana goye a bayanta yana bacci lukwi hankalina ya kwanta sosai domin duk juyin da zan yi sai ya fado mini a rai tare da takaici da b'acin ran abinda uwarsa ta aikata.
Sai bayan sallar azuhur tukkuna na samu Hauwa a waya. Ta daga hankalinta a kwance domin ban ji alamun nadama da danasani a muryarta ba.
Jikina ya mutu sosai da kyar na furta." Kina ina Hauwa?"
Kai tsaye ta ce." Ina nan Bauchi."
Na danne takaicina tare da cewa." Ashe kin shirya hakan tuntuni to hakan da ki ka yi a ganinki daidai ne ko?"
Da d'an murmushi ta ce." Shine daidai Amina, domin wa'adin zamana ya kare a gidan tunda na haihu yaro kuma ai gidan ubansa ne tunda ba dashi na zo ba, mai zai sanya na d'auko shi na kawo shi inda babu tarbiya Amina sunan Amadu fa ya fi sunan ubana an ce mini ubana ba komai ba ne a lokacin da na nuna shi din wani abu ne, tuntuni na gaya miki dama ba zan jure wannan rashin mutuncin ba."
Cike da takaici na furta." Amadu fa aka ce shine Mahmudu Muhammadu. Ki tuna mai wannan sunan shine wanda aka yi duniya dominsa Annabi Muhammadu S.a.w a ganina wannan abin alfahari ne a wurinki."
Ta yi murmushi tana cewa." A a ba da wannan niyyar ya sanya sunan Amadu ba. Abokinsa mai rasuwa fa shi yayi wa takwara na ce masa Ina son sunan mahaifina tunda na farko ya sanya sunan mahaifinsa daga fad'in haka ya fara gaya mini magana tabbacin dama haushina yake ji to menene saura a tsakaninmu na fita daga iddarsa da dama."
Na gyada kaina ina danne abinda nake ji a raina na ce." To kina ganin Allah ba zai kama ki da hakkin yaron ba shine ina ruwansa."
Ta yi Dariya tare da furta." Allah Ya yafe mini shi kuma idan rayayyene Allah Ya raya shi."
Na yi shiru domin kamar kalaman bakina sun kare da kyar na ce." Yanzu mai ki ka gayawa inna Uwani."
Da sauri ta furta." Tun daga farko a har karshe wallahi ban boye mata komai ba, Amina ai na yi hakuri na yi kuma biyayya, ke kan ki ban shure shawararki ba, na yi ta ha'kuri tsayin wattanin dana d'auka a matsayin sakakkiya mutumin nan baya kula ni kuma bai furta ya mayar da ni ba, duk wata dama ya samu bai yi magana ba yanzu kuma ai komai ya zo karshe na gaya mata komai haka zalika ma babu wanda bai sani na a family din Babanmu."
"Kenan Hajja ta ji komai?"
Na tambayata cikin zullumi.
Ta furta." Kwarai kuwa d'azu nan suka gama waya da Inna." Na yi shiru Ina nazari kafin daga bisani na furta." Hauwa idan zu'kata sun huce a daidaita don Allah kuma yaron nan da kaina zan kawo miki shi gobe in sha Allahu rabbi, ki yi hakuri don girman Allah ki kar'bi d'anki kada ki wulakantashi domin bakisan baiwar da take tare dashi ba."
"Na rantse da girman Allah a yanzu dai Amina ko kin zo da yaron nan sai dai ki koma dashi don wallahi tallahi ba zan karbe shi ba sai ubansa ya zo da k'afafunsa ya nuna nadama akan abinda ya yi mini, idan har ke za ki iya jure wulakancinsa ni kam ba zan iya ba. Ki ri'ke shi kawai na bar miki."
Bakina ne ya mutu murus na rasa abin cewa tunda har ta riga ta rantse nasan abu ne mai mutukar wahala ko na kai mata yaron ta kar'ba.
Zuwa yanzu kuwa na tabbatar da cewa tunda Hajja ta ji fasuwar maganar to babu shakka wanda ya asassa ma ya sani. Zan jira yi ji daga gare shi domin kuwa babu wani bangare da zan tuntunba Allah Ya ga zuciyata na yi iyakacin bakin k'okarinta.
Cikin hukuncin Allah lafiya lau muka kwana da yaron bai yi kuka ba domin kuwa Baba Tabawa ta bada dukkanin kulawarta a kansa. Ni kaina cewa ta yi na tafi na kwanta za ta kula da shi. Ban kwanta ba kuwa sai da na nuna mata yadda za ta dama masa madararsa idan Allah ya sa ya farka ta ajiye komai a kusa da ita wanda za ta buk'ata.
Da safe kuwa kafin na fito ta shirya shi tsaf yana goye a bayanta yana bacci lukwi hankalina ya kwanta sosai domin duk juyin da zan yi sai ya fado mini a rai tare da takaici da b'acin ran abinda uwarsa ta aikata.
Sai bayan sallar azuhur tukkuna na samu Hauwa a waya. Ta daga hankalinta a kwance domin ban ji alamun nadama da danasani a muryarta ba.
Jikina ya mutu sosai da kyar na furta." Kina ina Hauwa?"
Kai tsaye ta ce." Ina nan Bauchi."
Na danne takaicina tare da cewa." Ashe kin shirya hakan tuntuni to hakan da ki ka yi a ganinki daidai ne ko?"
Da d'an murmushi ta ce." Shine daidai Amina, domin wa'adin zamana ya kare a gidan tunda na haihu yaro kuma ai gidan ubansa ne tunda ba dashi na zo ba, mai zai sanya na d'auko shi na kawo shi inda babu tarbiya Amina sunan Amadu fa ya fi sunan ubana an ce mini ubana ba komai ba ne a lokacin da na nuna shi din wani abu ne, tuntuni na gaya miki dama ba zan jure wannan rashin mutuncin ba."
Cike da takaici na furta." Amadu fa aka ce shine Mahmudu Muhammadu. Ki tuna mai wannan sunan shine wanda aka yi duniya dominsa Annabi Muhammadu S.a.w a ganina wannan abin alfahari ne a wurinki."
Ta yi murmushi tana cewa." A a ba da wannan niyyar ya sanya sunan Amadu ba. Abokinsa mai rasuwa fa shi yayi wa takwara na ce masa Ina son sunan mahaifina tunda na farko ya sanya sunan mahaifinsa daga fad'in haka ya fara gaya mini magana tabbacin dama haushina yake ji to menene saura a tsakaninmu na fita daga iddarsa da dama."
Na gyada kaina ina danne abinda nake ji a raina na ce." To kina ganin Allah ba zai kama ki da hakkin yaron ba shine ina ruwansa."
Ta yi Dariya tare da furta." Allah Ya yafe mini shi kuma idan rayayyene Allah Ya raya shi."
Na yi shiru domin kamar kalaman bakina sun kare da kyar na ce." Yanzu mai ki ka gayawa inna Uwani."
Da sauri ta furta." Tun daga farko a har karshe wallahi ban boye mata komai ba, Amina ai na yi hakuri na yi kuma biyayya, ke kan ki ban shure shawararki ba, na yi ta ha'kuri tsayin wattanin dana d'auka a matsayin sakakkiya mutumin nan baya kula ni kuma bai furta ya mayar da ni ba, duk wata dama ya samu bai yi magana ba yanzu kuma ai komai ya zo karshe na gaya mata komai haka zalika ma babu wanda bai sani na a family din Babanmu."
"Kenan Hajja ta ji komai?"
Na tambayata cikin zullumi.
Ta furta." Kwarai kuwa d'azu nan suka gama waya da Inna." Na yi shiru Ina nazari kafin daga bisani na furta." Hauwa idan zu'kata sun huce a daidaita don Allah kuma yaron nan da kaina zan kawo miki shi gobe in sha Allahu rabbi, ki yi hakuri don girman Allah ki kar'bi d'anki kada ki wulakantashi domin bakisan baiwar da take tare dashi ba."
"Na rantse da girman Allah a yanzu dai Amina ko kin zo da yaron nan sai dai ki koma dashi don wallahi tallahi ba zan karbe shi ba sai ubansa ya zo da k'afafunsa ya nuna nadama akan abinda ya yi mini, idan har ke za ki iya jure wulakancinsa ni kam ba zan iya ba. Ki ri'ke shi kawai na bar miki."
Bakina ne ya mutu murus na rasa abin cewa tunda har ta riga ta rantse nasan abu ne mai mutukar wahala ko na kai mata yaron ta kar'ba.
Zuwa yanzu kuwa na tabbatar da cewa tunda Hajja ta ji fasuwar maganar to babu shakka wanda ya asassa ma ya sani. Zan jira yi ji daga gare shi domin kuwa babu wani bangare da zan tuntunba Allah Ya ga zuciyata na yi iyakacin bakin k'okarinta.