Sashe 32
Gudun Aure Book 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t
*@Arewabooks*
*Bintuumarabbale.*
*Free pege*
*19*
Tunda aka shiga hidimar sallar nan wata yarinya 'yar nan, ma'kotanmu ke shigowa gidan namu, a can wurin anti Maimuna take zama tunda nan din ne yara suka fi yawaita, tun kafin na ga yarinyar na ji sunanta a bakin Yusi Ihisan. 'Yar madamanciya ce dan bata fi shekara takwas ba, yawan ambaton sunanta da Yusi yake yi yasa nace idan ta shigo ya kawo mini ita na ganta, dan da alama jininsu ya hadu, yadda bashi da wahalar sabo ba haka itama take. Yarinya mai fara'a da ita. Na bata chocolate irin wad'anda nake ajiyewa suka fita tare da Yusi din. Can wurin anti Maimuna suka nufa cikin nishadi.
Da yamma likis ina kwance gajiya ta kayar da ni, ina ta lissafin abubuwan da zan saya dangane da bud'e shagunan dinkin da zanyi. Anti Maimuna ta shigo a kid'ime tana kiran sunana.
Na tashi zaune cikin tashin hankali don na d'auka mutuwa aka yi, ko maigidan na mu ne ya samu matsala.
Ta ce." Yarinyar nan Ihsan akayi wa fyad'e."
Gabana ya buga da karfin gaske na ce." Kada dai ki ce mini yar nan makota da take shigowa wasa wurin yara."
Ta ce." Itafa, yanzu nan yara suka shigo suna fad'a."
Na dinga nanata Innalillahi ina fad'in" Yarinya 'yar shekara bakwai, me za a samu a tare da ita, amma ya kamata ayi binkice akan wanda ya aikata wannan mummunan lamari."
Anti Maimuna za ta yi magana kenan. Uwar yarinyar ta shigo tana kuka da yarinyar a hannunta tana cewa." Ai tace Yusi ne kullum yake cire mata wando."
Cike da d'imuwa na ce." Yusi kuma? baiwar Allah wace irin magana ce wannan? Yusi me ya sani da har zai aikata haka."
Anti Jamila da shigowarta kenan ta bude baki tana cewa." Ai ba a shedar d'an yau, yo shekararsa sha d'aya fa, ai daf yake da balaga, yaron da aka haifa yau ma gabansa yana tashi balle saurayin da yayi wannan shekaru."
Na mi'ke tsaye da sauri ina fad'in." Karya kike yi munafuka yarona ba zai ta'ba aikata haka ba, a dai binkita a cikin yaranku."
Uwar yarinyar tana kuka take fad'in." Wallahi ba zan yarda ba fa."
Na dubeta tare da cewa." Kada Allah Ya sa ki yarda din, ki yi duk abinda za ki yi."
Ta juya ta fita a fusace.
Jamila ta bi bayanta tana kara zugata.
Na zube a kasan wurin cikin tashin hankali. Anti Maimuna ta dafa kafad'ata tana cewa." Amina a bi komai a hankali, tabbas na sheda Yusi ba zai yi wannan sakarcin ba. Dole dai a tsananta da bincike. A cikin gidan nan fa akayi can koridon da yake bayan dakina.
Na dubeta hawaye na ko'karin kwace mini na ce." Anti Maimuna lamarin nan ba na zama ba ne, ba yadda za a yi na yi lako-lako a d'orawa yaron nan abinda bai aikata ba."
Ta ce." Ni ma ban ce ki yadda ba, amma dai abi a hankali."
Ban ce mata komai ba har ta fita.
Kamalu ya shigo yana nishi kafafun wandonsa duk a tattare. Sai gumi yake yi.
Na dube shi zan yi magana ya katse ni Yana fad'in." Kokawa muka yi da su Turmuzi da Shahid Yayan Ihisan din, sun kama Yusi suna ta duka, sun d'auko almakashi wai zasu yanke masa wurin fitsari."
Cikin kad'uwa da d'imuwa na ce." Ina Yusi din, don sai a lokacin ma na tuna da cewa ban ga gilmawarsa ba tunda lamarin ya fasu. Kafin yayi magana Salima ta shigo tana kuka.
"Anti 'Yan-sanda ne a waje suka ri'ke Yusi gashi can a hannunsu. Suna neman Babanmu. yanzu Mamanmu ta kira shi a waya ya ce gashinan zuwa.
Hijabina nasa da sauri na kama hanyar fita yaran suka rufo mini baya.
Kofar gidan ta cika da mutane yara da manya. ga Yusi a hannun daya daga cikin jami'in yana kuka.
Yayin da wasu ke ta tambayar abinda yake faruwa.
Na iske wurin da yarona yake kai tsaye na ce." Sake shi domin ba shine ya aikata abinda ake zargi ba."
Jami'in ya ce." Ai magana ta kare tunda yarinya ta ce shine yake cire mata wando idan suna wasa, kuma kowa ya tabbatar da cewa shi din abokin wasanta ne, ke kin san haka, sannan iyayen yarinyar ma sun sani."
Wani zazzafan hawaye ya kwaranyo mini na ce." Wallahi ba shi ba ne, yaron ma guda nawa yake da zai aikata hakan, ku dai kara binkice, maraya ne, Allah ne gatansa, ni ce gatansa."
Ya ce." Ai marayun sun fi iyashege, saboda haka ba zamu sake shi ba sai mun gama gudanar da bincike."
Yusi ya rike gefan hijabina yana kuka, yana cewa." Mama wai me na yi?" Shi bai ma san akan me aka ri'ke shi ba."
Jami'in ya fizgeshi hannunsa daga jikina ya kwada masa mari mai tsanani!
"Tambaya kake yi me ka yi ko? za ka ci ubanka idan muka je station." Murya Kamalu na ji da k'arfi yana ce wa." Kai ma ubanka, shegu mugwaye sai Allah Ya saka masa." Sai kuka ya k'wace masa.
Wurin ya cika da hayaniya! wasu na fad'in." Dama ai yaron bashi da kunya, dan iska b'arawo ne shima, wasu kuma sai jajantawa suke yi. Yayin da wani jami'i daga cikinsu ya yi kukan kura zai cafko shi. Ganin haka ya sanya ya fafara da gudu ya yi gabas!
kaina na ya dinga bugawa kamar ana kwala mini guduma! Na dinga jin Hajijiya da kyar anti Maimuna ta zo ta janye ni daga wurin, rashin makama yasa na bi bayanta zuwa cikin gida tana rarrashinta tare da cewa na kwantar da hankalina inshallah gaskiya zata bayyana.
Na zube kasa cikin sanyi jiki na ce." Anti Maimuna ya zan yi ne?"
Ta ce." Addu'a za ki yi itace magani."
Da karfin gaske na furta." Inna lillahi wa'ina ilaihi raji'un!"
Tunda na dingi nanata Innalillahi na ji sauki yana saukar mini. Can kira ya shigo wayata dake uwardaki. Kafin na yi wani yun'kuri Salima ta shiga d'akin ta dauko mini da sauri ta ba ni. Hamusu ne ya kira. Na daga don ban yi mamaki ba tunda zan ce irin wannan sai ka tsince shi a wurin da baka ta'ba tsammani ba.
Cikin damuwa yake tambayata labarin da ya samu gaskiya ne. Na ce." Kai wanene yake gaya maka?" Kai tsaye ya ce." Kamalu ne." Na girgiza kai, ashe yaron can ya nufa lokacin da ya yi wa 'yansanda rashin kunya. Na ce." Haka dai iyayen yarinyar suke zargi Hamusu Amma a duniyar nan me Yusi ya sani da zai yi haka."
Ya ce." Wane police station suka tafi dashi?"
"Ka bari kawai ba sai ka je ba, Babansu Salima Yana can, in sha Allahu abun ba zai yi tsanani ba gaskiya zata bayyana. Kada ka gayawa Gwaggwo."
"Ba zan gaya mata ba in sha Allahu Amma anti Amina ki bari na je don Allah, kada duniya ta zage mu, wannan sharri ne?"
Na goge hawayen dake zuba a kumatuna na ce." Hamusu muddin aka binkita lamarin ba Babu gaskiya bisa zargin da suke yi wa yarona wallahi sai na d'aukaka kara ba zan yadda ba."
"Da damuwa mai yawa a tare dashi ya ce." Mu ma ba zamu yadda ba anti Amina, kawai ki gaya mini station din, zan je a yi komai a gabana."
Na ce." Ka bari zan kira ka zuwa an jima, don a halin yanzu ni ma ban san station ba, amma na gaya maka maigidan Yana can zamu yi waya idan an jima."
Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefana. Na kalli anti Maimuna tare da furta." Ba zan yadda ba wallahi sai na d'auki mataki akan wannan sharrin da aka yi mini."
Shiru ta yi ba tace komai ba, gabad'aya duk jikinta ya yi sanyi, yanayinta sai ya nuna kamar akwai abinda ke damunta ko take 'boyewa, shine dalilin da yasa take ta cewa da ni na yi hakuri na bar maganar. Ni Kuma ba ta san yadda nake ji a cikin raina ba.
Muna zaune ni da ita da yara cikin alhini maigidan ya shigo da Yusi a hannunsa. Gabad'aya muka zuba masa ido. Ni dai ganin yarona kalau, ya sanya na dinga godewa Allah, Amma yanayin mijin na mu shi ya fi d'aukar hankalina. Ya zauna kan kujera kamar mara laka. Ya dubi yaran tare da basu umarnin fita, Salima da yan'uwanta suka fice gabad'aya, Yusi din ma ya bi bayansu.
*@Arewabooks*
*Bintuumarabbale.*
*Free pege*
*19*
Tunda aka shiga hidimar sallar nan wata yarinya 'yar nan, ma'kotanmu ke shigowa gidan namu, a can wurin anti Maimuna take zama tunda nan din ne yara suka fi yawaita, tun kafin na ga yarinyar na ji sunanta a bakin Yusi Ihisan. 'Yar madamanciya ce dan bata fi shekara takwas ba, yawan ambaton sunanta da Yusi yake yi yasa nace idan ta shigo ya kawo mini ita na ganta, dan da alama jininsu ya hadu, yadda bashi da wahalar sabo ba haka itama take. Yarinya mai fara'a da ita. Na bata chocolate irin wad'anda nake ajiyewa suka fita tare da Yusi din. Can wurin anti Maimuna suka nufa cikin nishadi.
Da yamma likis ina kwance gajiya ta kayar da ni, ina ta lissafin abubuwan da zan saya dangane da bud'e shagunan dinkin da zanyi. Anti Maimuna ta shigo a kid'ime tana kiran sunana.
Na tashi zaune cikin tashin hankali don na d'auka mutuwa aka yi, ko maigidan na mu ne ya samu matsala.
Ta ce." Yarinyar nan Ihsan akayi wa fyad'e."
Gabana ya buga da karfin gaske na ce." Kada dai ki ce mini yar nan makota da take shigowa wasa wurin yara."
Ta ce." Itafa, yanzu nan yara suka shigo suna fad'a."
Na dinga nanata Innalillahi ina fad'in" Yarinya 'yar shekara bakwai, me za a samu a tare da ita, amma ya kamata ayi binkice akan wanda ya aikata wannan mummunan lamari."
Anti Maimuna za ta yi magana kenan. Uwar yarinyar ta shigo tana kuka da yarinyar a hannunta tana cewa." Ai tace Yusi ne kullum yake cire mata wando."
Cike da d'imuwa na ce." Yusi kuma? baiwar Allah wace irin magana ce wannan? Yusi me ya sani da har zai aikata haka."
Anti Jamila da shigowarta kenan ta bude baki tana cewa." Ai ba a shedar d'an yau, yo shekararsa sha d'aya fa, ai daf yake da balaga, yaron da aka haifa yau ma gabansa yana tashi balle saurayin da yayi wannan shekaru."
Na mi'ke tsaye da sauri ina fad'in." Karya kike yi munafuka yarona ba zai ta'ba aikata haka ba, a dai binkita a cikin yaranku."
Uwar yarinyar tana kuka take fad'in." Wallahi ba zan yarda ba fa."
Na dubeta tare da cewa." Kada Allah Ya sa ki yarda din, ki yi duk abinda za ki yi."
Ta juya ta fita a fusace.
Jamila ta bi bayanta tana kara zugata.
Na zube a kasan wurin cikin tashin hankali. Anti Maimuna ta dafa kafad'ata tana cewa." Amina a bi komai a hankali, tabbas na sheda Yusi ba zai yi wannan sakarcin ba. Dole dai a tsananta da bincike. A cikin gidan nan fa akayi can koridon da yake bayan dakina.
Na dubeta hawaye na ko'karin kwace mini na ce." Anti Maimuna lamarin nan ba na zama ba ne, ba yadda za a yi na yi lako-lako a d'orawa yaron nan abinda bai aikata ba."
Ta ce." Ni ma ban ce ki yadda ba, amma dai abi a hankali."
Ban ce mata komai ba har ta fita.
Kamalu ya shigo yana nishi kafafun wandonsa duk a tattare. Sai gumi yake yi.
Na dube shi zan yi magana ya katse ni Yana fad'in." Kokawa muka yi da su Turmuzi da Shahid Yayan Ihisan din, sun kama Yusi suna ta duka, sun d'auko almakashi wai zasu yanke masa wurin fitsari."
Cikin kad'uwa da d'imuwa na ce." Ina Yusi din, don sai a lokacin ma na tuna da cewa ban ga gilmawarsa ba tunda lamarin ya fasu. Kafin yayi magana Salima ta shigo tana kuka.
"Anti 'Yan-sanda ne a waje suka ri'ke Yusi gashi can a hannunsu. Suna neman Babanmu. yanzu Mamanmu ta kira shi a waya ya ce gashinan zuwa.
Hijabina nasa da sauri na kama hanyar fita yaran suka rufo mini baya.
Kofar gidan ta cika da mutane yara da manya. ga Yusi a hannun daya daga cikin jami'in yana kuka.
Yayin da wasu ke ta tambayar abinda yake faruwa.
Na iske wurin da yarona yake kai tsaye na ce." Sake shi domin ba shine ya aikata abinda ake zargi ba."
Jami'in ya ce." Ai magana ta kare tunda yarinya ta ce shine yake cire mata wando idan suna wasa, kuma kowa ya tabbatar da cewa shi din abokin wasanta ne, ke kin san haka, sannan iyayen yarinyar ma sun sani."
Wani zazzafan hawaye ya kwaranyo mini na ce." Wallahi ba shi ba ne, yaron ma guda nawa yake da zai aikata hakan, ku dai kara binkice, maraya ne, Allah ne gatansa, ni ce gatansa."
Ya ce." Ai marayun sun fi iyashege, saboda haka ba zamu sake shi ba sai mun gama gudanar da bincike."
Yusi ya rike gefan hijabina yana kuka, yana cewa." Mama wai me na yi?" Shi bai ma san akan me aka ri'ke shi ba."
Jami'in ya fizgeshi hannunsa daga jikina ya kwada masa mari mai tsanani!
"Tambaya kake yi me ka yi ko? za ka ci ubanka idan muka je station." Murya Kamalu na ji da k'arfi yana ce wa." Kai ma ubanka, shegu mugwaye sai Allah Ya saka masa." Sai kuka ya k'wace masa.
Wurin ya cika da hayaniya! wasu na fad'in." Dama ai yaron bashi da kunya, dan iska b'arawo ne shima, wasu kuma sai jajantawa suke yi. Yayin da wani jami'i daga cikinsu ya yi kukan kura zai cafko shi. Ganin haka ya sanya ya fafara da gudu ya yi gabas!
kaina na ya dinga bugawa kamar ana kwala mini guduma! Na dinga jin Hajijiya da kyar anti Maimuna ta zo ta janye ni daga wurin, rashin makama yasa na bi bayanta zuwa cikin gida tana rarrashinta tare da cewa na kwantar da hankalina inshallah gaskiya zata bayyana.
Na zube kasa cikin sanyi jiki na ce." Anti Maimuna ya zan yi ne?"
Ta ce." Addu'a za ki yi itace magani."
Da karfin gaske na furta." Inna lillahi wa'ina ilaihi raji'un!"
Tunda na dingi nanata Innalillahi na ji sauki yana saukar mini. Can kira ya shigo wayata dake uwardaki. Kafin na yi wani yun'kuri Salima ta shiga d'akin ta dauko mini da sauri ta ba ni. Hamusu ne ya kira. Na daga don ban yi mamaki ba tunda zan ce irin wannan sai ka tsince shi a wurin da baka ta'ba tsammani ba.
Cikin damuwa yake tambayata labarin da ya samu gaskiya ne. Na ce." Kai wanene yake gaya maka?" Kai tsaye ya ce." Kamalu ne." Na girgiza kai, ashe yaron can ya nufa lokacin da ya yi wa 'yansanda rashin kunya. Na ce." Haka dai iyayen yarinyar suke zargi Hamusu Amma a duniyar nan me Yusi ya sani da zai yi haka."
Ya ce." Wane police station suka tafi dashi?"
"Ka bari kawai ba sai ka je ba, Babansu Salima Yana can, in sha Allahu abun ba zai yi tsanani ba gaskiya zata bayyana. Kada ka gayawa Gwaggwo."
"Ba zan gaya mata ba in sha Allahu Amma anti Amina ki bari na je don Allah, kada duniya ta zage mu, wannan sharri ne?"
Na goge hawayen dake zuba a kumatuna na ce." Hamusu muddin aka binkita lamarin ba Babu gaskiya bisa zargin da suke yi wa yarona wallahi sai na d'aukaka kara ba zan yadda ba."
"Da damuwa mai yawa a tare dashi ya ce." Mu ma ba zamu yadda ba anti Amina, kawai ki gaya mini station din, zan je a yi komai a gabana."
Na ce." Ka bari zan kira ka zuwa an jima, don a halin yanzu ni ma ban san station ba, amma na gaya maka maigidan Yana can zamu yi waya idan an jima."
Na kashe wayar tare da ajiyeta a gefana. Na kalli anti Maimuna tare da furta." Ba zan yadda ba wallahi sai na d'auki mataki akan wannan sharrin da aka yi mini."
Shiru ta yi ba tace komai ba, gabad'aya duk jikinta ya yi sanyi, yanayinta sai ya nuna kamar akwai abinda ke damunta ko take 'boyewa, shine dalilin da yasa take ta cewa da ni na yi hakuri na bar maganar. Ni Kuma ba ta san yadda nake ji a cikin raina ba.
Muna zaune ni da ita da yara cikin alhini maigidan ya shigo da Yusi a hannunsa. Gabad'aya muka zuba masa ido. Ni dai ganin yarona kalau, ya sanya na dinga godewa Allah, Amma yanayin mijin na mu shi ya fi d'aukar hankalina. Ya zauna kan kujera kamar mara laka. Ya dubi yaran tare da basu umarnin fita, Salima da yan'uwanta suka fice gabad'aya, Yusi din ma ya bi bayansu.