Sashe 25
Gudun Aure Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
To cikin kwana uku kacal na fahimci yadda al'amuran suke gudana a gidan Alhaji Muntari. A kwai kusakurai masu girma da suka riga suka yi karfi a yanzu wanda idan an ce za a gyara su za a samu matsala babba, tunda tun fil'azal a haka suka gina gidan da kuma mijin nasu.
Alhaji Muntari rayuwarsa yake gudanarwa irin ta bahaushe zalla, karin abin kuma iyakacinsa sakandire bai yi zurfin karatun boko ba, na addinin ma akwai matsala domin Yana tafka kusakurai a sha'aninsa, kuma yadda na lura dashi ba mutum ne mai so a yi masa gyara ba. Irin mutana nan ne da duk abinda suka yi daidai ne. Tun ranar da ya fara auratayya da ni, na fuskance dhi. Idan mun kammala yana kallona zan shiga bandakin da yake cikin dakinsa na tsarkake jikina, amma sai dai na fito na same shi Yana bacci tare da najasar a jikinsa. Abin takaici kuma da ban haushi baya tashi sallar asubahi. Har sai gari ya yi haske tukkuna zai yi sallah.
Sun samu bambamci da Yaya Aminu ta wannan gefan, domin shi Abbansu Yusi akwai ibada. Ta inda dabi'arsu ta zo daya wurin mayatar yin jima'i, duk dare lokacin Yaya Aminu sai ya kwanta da ni, shiyasa da Allah Ya had'a ni da wannan din ban damu ba, tunda jikina ya riga ya saba da Hakan.
Alhaji Muntari d'an sharholiya, aji dad'in duniya kawai. Addini bai dame shi ka'in da na'in ba. Ya yi ado da kwalliya ya ci abinci, sannan ya kwanta da mace, wannan shine abinda ya fi bawa muhimmanci. Gidansa babu yunwa da abinci, Yana kuma ko'karin tsarewa kowa mutumcinta. Sai dai 'keta da matan gidan suka sanya a zukatunsu. Abinci d'anye dai gashinan a store. To duk wadda take da girki idan zai fita zai bata dubu biyu kudin kayan miya kawai da markade, tunda Yana Aiko da nama ko kaji daga kasuwa.
Ranar da na kar'bi girki, gabad'aya dubu biyun na karar da ita na yi komai a wadatace kamar yadda suke yi ba. Koda na dibi na maigidan da wanda zan ci sai na bar musu tukunyar domin ban san ya za a yi na raba.Na kira anti Maimuna ganin tana da sau'kin fahimta, na ce ta raba a hankali sai na koya.
Sai suka fara hayaniya. Anti Jamila na fad'in." Akan me, za ki kwashe miyar duk ki juye a kwanukan yaranki, haba anti Maimuna, akwai son zuciya fa."
Na yi shiru ina kallonsu da mamakin irin fitsarar da Jamila ke yi wa Anti Maimuna, ita kuma duk sai ta diririce, hannunta Yana kyarma tana raba abincin take cewa" Kowa za a zuba masa, Jamila ki kwantar da hankalinki."
Ta kalleni tana cewa." Ke ma ai da ki ka yi girkin ke ya cancanta ki raba abincinki, tunda dai kin san gidan iyali ki ka shigo, mijinki ya gaya miki komai, to ba sai ki k'arasa ladanki ba."
Uffan ban ce mata ba, na danne zuciyata da take shirin danna mata zagi.
Anti Maimuna ta ce." Jamila, wai me ki ke nufi ne, na gaji fa da wannan iyashegen da ki ke yi mini, ki dinga yi mini tsawa, tunda Amina ta zo gidan nan, ki ke neman fitina, ina lefi don ta yi abincin ta ce mu raba, ai yaran mu ne gabad'aya. Kuma idan ta ce za ta yi rabon ba ta san ya za ta yi ba, komai sai a hankali. Amma kin zo kina ta yi mini rashin kunya, me ki ke nufi ne?"
"To, ai gani na yi, kin fito da son zuciyarki 'karara, idan ke za ki yi miyar ai ba za ki saki jiki ki yi kamar wannan ba, kuma duk kin d'ibe kina zubawa a kwanukan yaranki, waccan ma da ki ka zuba a robar rufaida yogurt ta wacece?"
Cikin bacin rai na ce." Wai ke don Allah menene haka? Ba fa girma da mutunci ba ne, ya za a yi mata tana iyakacin k'okarinta a gida, kina yi mata abinda ki ke so, ga yaranta suna jinki, idan kuma watarana suka yi miki fitsara fa, don Allah ki daina haka anti Jamila, mu yi hakuri dukanmu."
"Kin ga, don Allah Ya isa, lefin ai na ki ne, me yasa ba za ki raba abincin da hannunki ba, ai mai iyali ki ka aure dole ki yi, ni ma kafin na ajiye nawa sai da na yi wannan bautar, ba zan yadda da sigar munafurci ba, shine za ki kira ta ki ce ta zo ta raba akan me?"
Na ce.'' Babu dole Hajiya, ina lefin ma girkin da na yi, kuma ni dai ki dubi tsabar idona da kyau ki ga ni, ba zan lamunci wannan daga wurinki ba, ban shigo domin tashin hankali ba, amma idan kin ce ayi to a shirye nake, haba ina dalili, mata tunda na zo gidan nan ki ke ta hayaniya, ko kin d'auka hakan zai sanya na ji tsoronki ne."
"To kada Allah Ya sa ki yi din mana, munafuka kawai, wallahi muddin ki ka ce ba za ki zauna lafiya da mu ba, ke ce a wahale, kuma maigidan zai dawo sai na gaya masa abubuwan da kuka fara yi mini. Ni ban iya rayuwar munafurci ba, kome za a yi to a fito fili a yi shi a gaban kowa."
Na ce." Idan Ya dawo ki sanya shi ya sallame ni, tunda ke ki ka sanya shi ya aure ni. Kuma wallahi ki daina kira na munafuka idan ba haka ba, ni duka nake yi ban iya cacar baki, jikinki ne zai gaya miki."
Turzumi babban yaronta ya ce." Aikuwa wallahi sai na kwala miki dutse' na fasa miki kai idan ki ka daketa."
Yaran gabad'aya suka kwashe da dariya. wadda hakan ya kara kona mini rai!
Anti Maimuna ta buga musu tsawa suka yi shiru, ta ce." Kowa ya d'auki abincinsa ya isa haka."
Suna fara hayaniyar d'aukar abincin. Na bar wurin raina a kuntacce wannan wane irin gidane ......
*1k on talgram via 0542382124...Binta Umar gtbank*
*07084653262*
[11/25, 10:29 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*
*TALLAH!*
*Gidan 'kawa ne da kece raini, abin ma sai wanda ya yi joning da su, nan zai kashe kwarkwartar idonsa ga sau'kin farashi!*
🛍️ “Ko ba ki da niyyar siya ba, ki zo ki shiga ki kalla kayayyaki — wallahi sai kin bude ido! Ballantana kuma nasan za ki tashi da kaya saboda kyau da araha.” ✨
🌸✨ “Shigo duniyar da kyau da jin daɗi suka haɗu — daga kyawawan laces na alfarma, Atamfa , abaya masu salo, zuwa kayan ado masu kyalli, kayan girki na zamani da sauran ƙarin abubuwa. A Meerah B Collection , muna adashen kayan kitchen daily 1k to pack 100k items weekly Monthly ✨🌸We are sale kitchen items, electronic, WE ALSO DEAL WITH CONTRIBUTE monthly weekly daily after 10 days for kitchen items or electronic gaba daya wanna package 60k nake had'a sa zaku iya mallaka ta hanyar adashi
https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t
*@Arewa book's*
*Bintuumarabbale*
*Free pege*
*16*
Ta ina zan yi sake na samu ciki har na haihu a irin wannan gida na alhaji Muntari. Lallai dole na yi takatsantsan, domin tashin farko na lura gidan ba irin wurin da za ka saki jiki ka haihu ba ne, dalilin rashin saiti, da gurguwar rayuwar da iyalinsa suka kafu akai. Wannan marayan da Allah ya jarabce ni dashi ya ishe ni. Ina ro'kon
Ubangiji ya ba ni ikon kula dashi tare da d'an'uwansa da kuma tarbiyarsu. Dole kuma koda yarana sun dawo gidan, na sanya ido kwarai a rayuwar da za su gudanar sabili da rashin gamsuwa da tarbiyar yaran gidan. lamarin dai sai da kawai mu ce Allah Ya magance mana.
A daran ranan na fara had'iyar maganin hana d'aukar ciki. Dama na yi guzurin abina, zahirin gaskiya ba zan iya haihuwa dashi a irin wannan yanayin da shi kansa bai san menene rayuwa ba.
Muka cigaba da tafiya a haka. Anti Maimuna macece mai sau'kin hali, kuma mara son hayaniya, yayin da ita Jamila ta kasance bagidajiya mara fahimta. Ko da yake babu mamaki idan an samu hakan daga wurinta domin a can karkara ya aurota wani kauye a karamar hukumar bichi, shiyasa komai nata take gudanar dashi cikin gidadanci, da kuma zargi. Gabad'aya jininmu bai hadu ba, tunda na fahimci halinta, sai nake takatsantsan, ban ta'ba yadda mun yi rigima ba, duk takalar da za ta yi mini, ba na nuna na san ta na yi. Sabgar gabana nake yi. Idan ba ranar girkina ba ma, ba na fitowa, ina ta sana'ata.
Sai dai kuma zamansu a Kamalu a gidan yana nema ya zama d'an zani, domin ko kwana uku ba su yi da dawowa ba, matsaltsalu suka fara kunno kai. Yusi yaro ne mai son jama'a, ba shi da wahalar sabo, kullum Yana cikin yaran gidan su yi ta wasa. Amma ba a k'arewa lafiya sai ya shigo mini yana kuka, Turzumi ya dake shi. Idan na tambaye shi dalili sai ya ce babu komai, kawai dukansa ya yi. Sai dai kawai na rarrashe shi amma abin yana damuna mutuka.
Kamalu ya yi ta kumbure-kumbure, yana jin haushi. Na hana shi motsi, domin dama tunda suka dawo gidan na zaunar dashi a gabana yana taimaka mini da wasu abubuwan na sana'ata
Ba ni da matsala da maigidan, domin kamar yadda ya fad'a tunda yaran suka dawo hannunsa yake iyakacin bakin kokarinsa. Ya kammala musu komai na makarantar boko da Islamiyya wadda yaransa suke zuwa. Satin da za mu shiga za a koma makaranta gabad'aya. Matsalata yadda Turmuzi ke cin zalin Yusi. Wanda na tabbatar da cewa ba zai yi masa lefin da zai kai hannun jikinsa ba, face dai cin zali da ganin gidansu ne. Sai kuma rashin kwa'ba daga wurin uwarsa.
Alhaji Muntari rayuwarsa yake gudanarwa irin ta bahaushe zalla, karin abin kuma iyakacinsa sakandire bai yi zurfin karatun boko ba, na addinin ma akwai matsala domin Yana tafka kusakurai a sha'aninsa, kuma yadda na lura dashi ba mutum ne mai so a yi masa gyara ba. Irin mutana nan ne da duk abinda suka yi daidai ne. Tun ranar da ya fara auratayya da ni, na fuskance dhi. Idan mun kammala yana kallona zan shiga bandakin da yake cikin dakinsa na tsarkake jikina, amma sai dai na fito na same shi Yana bacci tare da najasar a jikinsa. Abin takaici kuma da ban haushi baya tashi sallar asubahi. Har sai gari ya yi haske tukkuna zai yi sallah.
Sun samu bambamci da Yaya Aminu ta wannan gefan, domin shi Abbansu Yusi akwai ibada. Ta inda dabi'arsu ta zo daya wurin mayatar yin jima'i, duk dare lokacin Yaya Aminu sai ya kwanta da ni, shiyasa da Allah Ya had'a ni da wannan din ban damu ba, tunda jikina ya riga ya saba da Hakan.
Alhaji Muntari d'an sharholiya, aji dad'in duniya kawai. Addini bai dame shi ka'in da na'in ba. Ya yi ado da kwalliya ya ci abinci, sannan ya kwanta da mace, wannan shine abinda ya fi bawa muhimmanci. Gidansa babu yunwa da abinci, Yana kuma ko'karin tsarewa kowa mutumcinta. Sai dai 'keta da matan gidan suka sanya a zukatunsu. Abinci d'anye dai gashinan a store. To duk wadda take da girki idan zai fita zai bata dubu biyu kudin kayan miya kawai da markade, tunda Yana Aiko da nama ko kaji daga kasuwa.
Ranar da na kar'bi girki, gabad'aya dubu biyun na karar da ita na yi komai a wadatace kamar yadda suke yi ba. Koda na dibi na maigidan da wanda zan ci sai na bar musu tukunyar domin ban san ya za a yi na raba.Na kira anti Maimuna ganin tana da sau'kin fahimta, na ce ta raba a hankali sai na koya.
Sai suka fara hayaniya. Anti Jamila na fad'in." Akan me, za ki kwashe miyar duk ki juye a kwanukan yaranki, haba anti Maimuna, akwai son zuciya fa."
Na yi shiru ina kallonsu da mamakin irin fitsarar da Jamila ke yi wa Anti Maimuna, ita kuma duk sai ta diririce, hannunta Yana kyarma tana raba abincin take cewa" Kowa za a zuba masa, Jamila ki kwantar da hankalinki."
Ta kalleni tana cewa." Ke ma ai da ki ka yi girkin ke ya cancanta ki raba abincinki, tunda dai kin san gidan iyali ki ka shigo, mijinki ya gaya miki komai, to ba sai ki k'arasa ladanki ba."
Uffan ban ce mata ba, na danne zuciyata da take shirin danna mata zagi.
Anti Maimuna ta ce." Jamila, wai me ki ke nufi ne, na gaji fa da wannan iyashegen da ki ke yi mini, ki dinga yi mini tsawa, tunda Amina ta zo gidan nan, ki ke neman fitina, ina lefi don ta yi abincin ta ce mu raba, ai yaran mu ne gabad'aya. Kuma idan ta ce za ta yi rabon ba ta san ya za ta yi ba, komai sai a hankali. Amma kin zo kina ta yi mini rashin kunya, me ki ke nufi ne?"
"To, ai gani na yi, kin fito da son zuciyarki 'karara, idan ke za ki yi miyar ai ba za ki saki jiki ki yi kamar wannan ba, kuma duk kin d'ibe kina zubawa a kwanukan yaranki, waccan ma da ki ka zuba a robar rufaida yogurt ta wacece?"
Cikin bacin rai na ce." Wai ke don Allah menene haka? Ba fa girma da mutunci ba ne, ya za a yi mata tana iyakacin k'okarinta a gida, kina yi mata abinda ki ke so, ga yaranta suna jinki, idan kuma watarana suka yi miki fitsara fa, don Allah ki daina haka anti Jamila, mu yi hakuri dukanmu."
"Kin ga, don Allah Ya isa, lefin ai na ki ne, me yasa ba za ki raba abincin da hannunki ba, ai mai iyali ki ka aure dole ki yi, ni ma kafin na ajiye nawa sai da na yi wannan bautar, ba zan yadda da sigar munafurci ba, shine za ki kira ta ki ce ta zo ta raba akan me?"
Na ce.'' Babu dole Hajiya, ina lefin ma girkin da na yi, kuma ni dai ki dubi tsabar idona da kyau ki ga ni, ba zan lamunci wannan daga wurinki ba, ban shigo domin tashin hankali ba, amma idan kin ce ayi to a shirye nake, haba ina dalili, mata tunda na zo gidan nan ki ke ta hayaniya, ko kin d'auka hakan zai sanya na ji tsoronki ne."
"To kada Allah Ya sa ki yi din mana, munafuka kawai, wallahi muddin ki ka ce ba za ki zauna lafiya da mu ba, ke ce a wahale, kuma maigidan zai dawo sai na gaya masa abubuwan da kuka fara yi mini. Ni ban iya rayuwar munafurci ba, kome za a yi to a fito fili a yi shi a gaban kowa."
Na ce." Idan Ya dawo ki sanya shi ya sallame ni, tunda ke ki ka sanya shi ya aure ni. Kuma wallahi ki daina kira na munafuka idan ba haka ba, ni duka nake yi ban iya cacar baki, jikinki ne zai gaya miki."
Turzumi babban yaronta ya ce." Aikuwa wallahi sai na kwala miki dutse' na fasa miki kai idan ki ka daketa."
Yaran gabad'aya suka kwashe da dariya. wadda hakan ya kara kona mini rai!
Anti Maimuna ta buga musu tsawa suka yi shiru, ta ce." Kowa ya d'auki abincinsa ya isa haka."
Suna fara hayaniyar d'aukar abincin. Na bar wurin raina a kuntacce wannan wane irin gidane ......
*1k on talgram via 0542382124...Binta Umar gtbank*
*07084653262*
[11/25, 10:29 AM] Aunty B: *GUDUN AURE!*
*NA*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*M.W.A*
*TALLAH!*
*Gidan 'kawa ne da kece raini, abin ma sai wanda ya yi joning da su, nan zai kashe kwarkwartar idonsa ga sau'kin farashi!*
🛍️ “Ko ba ki da niyyar siya ba, ki zo ki shiga ki kalla kayayyaki — wallahi sai kin bude ido! Ballantana kuma nasan za ki tashi da kaya saboda kyau da araha.” ✨
🌸✨ “Shigo duniyar da kyau da jin daɗi suka haɗu — daga kyawawan laces na alfarma, Atamfa , abaya masu salo, zuwa kayan ado masu kyalli, kayan girki na zamani da sauran ƙarin abubuwa. A Meerah B Collection , muna adashen kayan kitchen daily 1k to pack 100k items weekly Monthly ✨🌸We are sale kitchen items, electronic, WE ALSO DEAL WITH CONTRIBUTE monthly weekly daily after 10 days for kitchen items or electronic gaba daya wanna package 60k nake had'a sa zaku iya mallaka ta hanyar adashi
https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t https://chat.whatsapp.com/KXsuo5E7syZ879Gcid3wCm?mode=ac_t
*@Arewa book's*
*Bintuumarabbale*
*Free pege*
*16*
Ta ina zan yi sake na samu ciki har na haihu a irin wannan gida na alhaji Muntari. Lallai dole na yi takatsantsan, domin tashin farko na lura gidan ba irin wurin da za ka saki jiki ka haihu ba ne, dalilin rashin saiti, da gurguwar rayuwar da iyalinsa suka kafu akai. Wannan marayan da Allah ya jarabce ni dashi ya ishe ni. Ina ro'kon
Ubangiji ya ba ni ikon kula dashi tare da d'an'uwansa da kuma tarbiyarsu. Dole kuma koda yarana sun dawo gidan, na sanya ido kwarai a rayuwar da za su gudanar sabili da rashin gamsuwa da tarbiyar yaran gidan. lamarin dai sai da kawai mu ce Allah Ya magance mana.
A daran ranan na fara had'iyar maganin hana d'aukar ciki. Dama na yi guzurin abina, zahirin gaskiya ba zan iya haihuwa dashi a irin wannan yanayin da shi kansa bai san menene rayuwa ba.
Muka cigaba da tafiya a haka. Anti Maimuna macece mai sau'kin hali, kuma mara son hayaniya, yayin da ita Jamila ta kasance bagidajiya mara fahimta. Ko da yake babu mamaki idan an samu hakan daga wurinta domin a can karkara ya aurota wani kauye a karamar hukumar bichi, shiyasa komai nata take gudanar dashi cikin gidadanci, da kuma zargi. Gabad'aya jininmu bai hadu ba, tunda na fahimci halinta, sai nake takatsantsan, ban ta'ba yadda mun yi rigima ba, duk takalar da za ta yi mini, ba na nuna na san ta na yi. Sabgar gabana nake yi. Idan ba ranar girkina ba ma, ba na fitowa, ina ta sana'ata.
Sai dai kuma zamansu a Kamalu a gidan yana nema ya zama d'an zani, domin ko kwana uku ba su yi da dawowa ba, matsaltsalu suka fara kunno kai. Yusi yaro ne mai son jama'a, ba shi da wahalar sabo, kullum Yana cikin yaran gidan su yi ta wasa. Amma ba a k'arewa lafiya sai ya shigo mini yana kuka, Turzumi ya dake shi. Idan na tambaye shi dalili sai ya ce babu komai, kawai dukansa ya yi. Sai dai kawai na rarrashe shi amma abin yana damuna mutuka.
Kamalu ya yi ta kumbure-kumbure, yana jin haushi. Na hana shi motsi, domin dama tunda suka dawo gidan na zaunar dashi a gabana yana taimaka mini da wasu abubuwan na sana'ata
Ba ni da matsala da maigidan, domin kamar yadda ya fad'a tunda yaran suka dawo hannunsa yake iyakacin bakin kokarinsa. Ya kammala musu komai na makarantar boko da Islamiyya wadda yaransa suke zuwa. Satin da za mu shiga za a koma makaranta gabad'aya. Matsalata yadda Turmuzi ke cin zalin Yusi. Wanda na tabbatar da cewa ba zai yi masa lefin da zai kai hannun jikinsa ba, face dai cin zali da ganin gidansu ne. Sai kuma rashin kwa'ba daga wurin uwarsa.