← Book details Gudun Aure Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 35

Sashe 24

Gudun Aure Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*@Arewa books*
*Bintuumarabbale*
*Free peges*
*15*
Gabad'aya jikina ya mutu da kalaminsa na karshe. Dole haka na ha'kura tunda ya riga ya gama kashe mini jiki da tabbatar mini cewa zai kula mini da yarana, wanda dama duk abinda nake yi saboda su nake yi. Na kuma yi nazari sosai, akwai tazara mai mugun tsayi tsakanin nan kawo jirga da gwale makarantar da nake koyarwa, za a dinga samun tsaiko da tangard'a na makara da sauran matsaltsalu. Dole dai babu yadda zan yi na ha'kura, na ajiye aikin, na rungumi sana'ar hannun, tunda bai nuna mini keta a kanta ba.
A d'akina ya shirya sosai, ya yi gayu, nan na sake fahimtar mutum ne shi mai son ado da nuna 'kawa, hatta waya da biyu yake amfani, kuma masu girma da kudi. Kafin ya fita yake gaya mini idan ya gama kwanaki ukun da musulunci ya ba ni, sai na fara binsa dakinsa kamar yadda sauran suke masa.
Na ce." To shikkenan hakan ya yi." Sai bayan da ya fita da kamar minti ashirin tukkuna na zura hijabi na fito babban tsakargidan. Gashinan dai babu gyara, bakin kicin duk kwanuka. Da takalman yaran gidan a watse.
Na dinga jin kayaniyar yara a d'akin da yake fuskanto ni. Kai tsaye can na nufa cikin nutsuwa na shiga da sallama.
Tana kwance kan duguwar kujera, da kayan bacci a jikinta. fara ce gajera, kamar dai yadda ya nuna mini ita a hoto, ba ta da muni. yaran suna ta wasa, wasu daga ciki da littafain makaranta, wasu kuma game suke yi a wayar da nake tsammanin ta ta ce. Ta mike zaune da sakakkiyar fuska tana cewa." Shigo mana." Na saki fuskata sosai na shiga na zauna kan kujera, ina fad'in." Yaran duk suna nan kenan, ko da yake ai da sauran hutun tukkuna."
Tana gyara zamanta ta ce." Ai hutu kuma ya kare tunda litinin za a koma, kada ki so ki ya yadda zaman nan nasu ya isheni, dan bacci nan na safe basa barina na yi."
Dariya na yi, ina kallonsu yayin da suke yi mini wani irin kallo, na rashin sani, cikinsu kuma babu wanda ya yi tunanin ya gaisheni.
Na ce." Ina kwana, ya yaran, fatan na sameku lafiya."
Ta amsa a sake tana cewa." Lafiya Lou ki ka same mu, yanzu nan dama Babansu da ya shigo yake gaya mini za ki zo mu gaisa."
Wani d'an matashin yaro da tun zamana a wurin na ji ana kiransa da Turmuzi Ya ce." Mama itace amaryar Babanmu ne?"
Ta ce." E, ita ce" Shiru ya yi bai ce komai ba, sai kuma can ya tashi ya fita da sauri. Sauran yaran kuma suka cigaba da sha'aninsu babu wanda ya gaisheni a cikinsu.
Na cika da mamaki sosai, kuma ita Anti Maimuna haka sunanta yake ba ta tsawatar musu ba.
Minti kusan goma ina zaune muna dan ta'ba hira. Na lura tana da sakin fuska, kuma dai a haka kamar babu wani kulli a zuciyarta. Tana gaya mini yadda tsare-tsaren gidan yake. Sai dai yadda na fahimta tana da son jiki da kazanta a jikinta da falonta na lura da hakan, tafin 'kafafunta duk sun yi daud'a. Kuma kayan bacci ne a jikinta masu ruwan haske,
Amma sun dafe, gashi dai safiya ce, amma kusancina da ita hancina yana ta sha'ko mini warin hammatarta, dukda hallita ne, amma dai akwai kazanta a sha'aninta, tunda mutum ya san yana da ki'bar da za ta ajiye masa gumi sai ya bi matakan gyarawa.
Shigowa ta yi babu sallama tana cewa." Tun d'azu Turmuzi ya je yana gaya mini ga amarya nan a sashenki, anti Maimuna ai sai ki ce na zo ni ma a zauna da ni, a kalla fa kun fi minti ashirin a tare, ni ba fa na son haka."
Cikin kausasa harshe take yin maganar. Ita kuma sai ta fara dariya tana cewa." Yanzu nan nake cewa Salima ta zo ta rakata wurinki ku gaisa, ai na yi tsammanin bacci ki ke yi ne."
Ta zauna tana d'an kallona kafin ta ce." Ba bacci nake yi ba, kuma da ki ke cewa Salima ta rakota wurina makauniya ce ita, ai babu wanda ya yi mata jagora ta shigo wurinki, haka Turmuzi ya gaya mini.

Anti Sakina ta ce." Ke fa matsalata dake Jamila gajan ha'kuri wallahi, wannan ba a bin damuwa ba ne fa."
"Gajan ha'kuri kamar yaya Anti Maimuna, gaskiya na fada fa, kin san ni komai a bud'e nake yinsa."
Na ce."Haba baiwar Allah, kya bari mu gaisa ko? Ai zan shigo har wurin naki dama bisa bin umarin maigidan, ina fata dai na sameku lafiya."
"Lafiyarmu lau wallahi, ya hidima fatan an tashi taro lafiya."
"Alhamdulillahi, na shigo cikinku da kyakykyawar zuciya, ina fatan zaku karbe ni hannu biyu." Ta ce." In sha Allahu rabbi."
Falon ya yi shiru. Yaran duk sun zubo mana Ido. Sai na dube su a tsanake na ce.' Babu wanda ya gaishe ni a cikinku, kuma duk ku gaya mini sunayenku." Da yar dariya na yi maganar.

Sai suka fara rige-rigen gaisheni, kowa yana ko'karin gaya mini sunansa. Na dubu Anti Maimuna da fad'in." Salima ce babbarsu ko?" Ta ce." E, itace gata nan sai tsawon kafar tsiya." Na ce." Ai girman 'ya mace ba shi da wahala, daga zarar ka fara da mace sai girma ya kamaka."
Ta yi dariya tana cewa." Wallahi hakane. "
Anti Jamila tasha kunu bata tofa mana ba. Ni Kuma ina sane ban sanya maganata da ita ba, saboda karon farko na fahimci bata da hankali, sannan yadda take nuna gadara akan Uwargidan, tana gaya mata magana kausasa bayan ko banza ta girme mata, to ni ba zan d'auka ba, duk cikinmu babu yaro, ba na tsammanin itama ta ba ni wasu shekaru da yawa. Shiyasa tun bayan gaisuwar da muka yi da ita, ban 'kara tanka mata ba, daga karshe ma sai na tashi na yi musu sallama na koma wurina da tunanin yanayin zamantakewar da suke gudanarwa mara kangado.

Ciki da falo ne wadatattu, kuma kayan katakon da ya zuba mini masu kyau ne da tsada da manyan labuleye. Harda tibi irin ta bango. Na yaba masa sosai domin d'akin nawa ya yi kyau k'warai ko na wata budurwar albarka. Matsalar dai kawai babu bandaki a d'akin duk suna can waje. Dakinsa ne kawai dashi. Kicin din ma na had'aka ne. Amma gidan akwai yalwa irin gini ne na wadata babu takura. Har da wurin saukar baki a cikin gidan
Na d'an gyara abinda bai yi mini, na ware kwanukan da zan zuba a kwando, da fulasai, da duk abinda zan nema domin ba na tunanin zan kwashi kayana na kai kicin din gabad'aya, domin fitar da na yi d'azu, na hasashi akwai gyara sosai a tare dasu, gidan gabad'aya babu tsafta har kicin din, kudaje sai bi suke yi, ban sani ba ko suna da mai aiki oho. Na zauna ina hutuwa amma gabad'aya hankalina na kan yaran, mussaman Yusi jiya ya sharbi kuka lokacin da za mu taho sai wayo aka yi masa aka fita dashi daga gidan.
Gwaggo wayarta ta lalace sai na nemi ta Hamusu dukda ba ni da tabbacin Yana gidan, amma dai ai garin yanzu ya waye.
Muka gaisa Yana 'yar dariya yake cewa."Amina Anya yau kin yi bacci arziki kuwa, na san hanalinki Yana kan yaran nan."
Ni ma cikin barkwanci na ce." Ban yi ba gaskiya, ai shiyasa ma na gaza ha'kuri na ce bari na kira ka, na ji ya suka kwana."

Ya ce." Suna nan lafiya lau, ga Yusi nan ya warware Yana ta wasansa. Shi kuma Kamalu gashi nan, Yana zubawa Gwaggo ruwa."
Na ce." To fara ba ni Gwaggon mu gaisa tukkuna."
Ya mika mata watar. Na ce." Gwaggo ina kwana, Kun tashi lafiya?".

Cike da kulawa ta amsa tana cewa." Ya kwanan bakunta Kuma." Na ce." Alhamdulillahi Gwaggo. Sai ta dora da cewa ." Ai ana ta fad'in nagartar abokanan zamanki, an ce kansu a had'e yake ba su ta'ba fad'a ba, kema ki bi su a yadda ki ka gansu domin samun daidaito. Ubangiji Allah Ya sanya alheri."
Na ce." Amin Ya Allah, ai kam babu lefi, akwai fahimta a tsakaninsu, in sha Allahu zan zauna dasu lafiya."
Ta ce.'"To Allah Ya kad'e fitina."
Hamusu Ya kar'bi wayar yana fad'in." Fita zan yi anti Amina, ga Yusi ku gaisa, idan na dawo da yamma zan kira ki sai ku gaisa da Kamalu, don ya fita yanzu, na ce miki dama Yana zubawa Gwaggo ruwa, yau me ruwanta ne bai kawo mata ba."
Na ce." To shikkenan bawa Yusi wayar." Ya mika masa da zumud'i a tare dashi Yana dariya yake cewa." Mama shine jiya ku ka yi mini wayo kuka gudu ko?"
Na sauke ajiyar zuciya a nutse na ce." Babu gaisuwa sai korafi ko Yusi."
"Yi hakuri Mama, ina kwana ya kuke?"
"Na ce." Ina lafiya lau, zaka zauna a hannun Gwaggo ko?"
"Um-um!" Ya furta da sauri."
Na yi dariya tare da cewa." Shikkenan zan zo na d'aukeku sati mai zuwa in sha Allahu." Farincikinsa Ya tsananta ya ce." To daga yau zan fara lissafi Mama." Na yi dariya tare da cewa." Ba wa Baba Hamusu wayar zan yi magana dashi."

Yana kar'ba na ce." Don Allah da yamma idan babu takurawa kai da Usaini ku kawo mini kekunan d'inkina mana, akwai sauran kayan jama'a a hannuna. Maigidan Ya ce na ajiye aiki Hamusu, shiyasa gabad'aya yanzu hankalina ya karkarta wurin ganin na kafu anan din. Dukda na san da yawa wad'anda za su biyo nan din, amma ina so nan din ma a san ni akan sana'ata."
Ya ce."Anti Amina dadina dake akwai himma, kina da zuciya da neman na kanki, Allah Ya dafa miki, in sha Allahu kuma daga na dawo daga kasuwa zan je can gidan naku na samu Usainin."
Na ce." Shi ma na gaya masa Ya na jiranka."
Ya ce." To shikkenan za mu zo in sha Allahu."

Muka yi sallama na kashe wayar na ajiye. Ina sake nazarin yadda al'amurana za su kasance a sabuwar rayuwar da na tsinci kaina a cikinta.
Chapter 24 · 0% Book details