← Book details Gudun Aure Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 35

Sashe 12

Gudun Aure Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*@Arewa books.*
*Bintuumarabbale.*
*8*
Duk yadda naso tursasa zuciyata ganin hasken Alhaji Muntari hakan bai samu ba. Domin na riga na gama amincewa da cewa da wahala na samu namiji da yake kaunata fiye da Yaya Aminu
Ban sani ba ko saboda auran ya fice daga raina ne ya sanya nake ganin duhun duk wani namaji da zai ra'be ni. Shi kansa Alhaji Muntari zan aure shi ne domin kawar da 'kalabulan da yake tunkaro ni na rushewar tarbiyar yarona. Ina ganin idan muka bar gidan za a samu saukin wasu al'amuran.
Da yamma ya kira ni yake gaya mini ya turo mini dubu talatin na duba na gani. Cike da mamaki na ce." Kudin sun yi yawa Alhaji jiya fa da ka zo ka ba ni wasu ." Ya ce." Babu matsala Amina ai ba rokata ki ka yi ba, ni na yi ra'ayi na baki, saboda haka babu Kalmar godiya a tsakaninmu."
Jikina ya sake yin sanyi da sha'aninsa. Na ce." To na gode sosai, Allah Ya biya ka."
Ya amsa yana cewa" Zan kira ki da daddare sai mu sake tattaunawa."
Na ce." To shikkenan." Ya kashe wayar. Na yi shiru ina zullumi. Wato mai bushasha ne mutumin nan, wata'kila abinda Baba Sule ya hanga kenan ya rikice.
Da daddare ilai kuwa sai gashi ya zo gidan. Ya shigo ya same ni a d'aki Ina aikin had'awa mutane d'inkunansu.
Na gaishe shi ya amsa fuskarsa a sake har yana tambayar su Kamalu.
Na ce." Sun tafi makarantar dare.
Ya nisa kafin ya ce." Ai yau Alhaji Muntari yake fad'a mini yadda ku ka yi, na yi miki murna domin mutumin kirki ne abinda nake miki sha'awa kenan, shiyasa na hadaki dashi, kuma ya tabbatar mini da cewa zai ri'ke miki yaranki duka biyun."
A takaice na ce." E, haka ya fada."
Ya gyara tsayuwa yana cewa." Yanzu yaushe ki ka yanke maganar d'aurin aure, kin ga shi fa babban mutum ne, ba na son shiririta."
Na ce." Sai mun je Maiduguri mun dawo bikin Babandi."
"To babu lefi, daga dai kun dawo din sai a yi magana, ba na so na zama dattijon banza ."
Ni dai shiru na yi masa ban ce komai ba. Ya gama maganarsa ya kama hanya ya fita.

***
Ranar da za mu tafi Saminu ya sanya rigima lallai sai an tafi dashi har da kuka. Babanmu to ya ce ya yi sauri ya shirya. Jin haka ya sanya na yanke shawarar barin Kamalu a gida tunda saboda za a tafi dashi ne yake rigima sai kace karamin yaro, gabad'aya haushi yake ba ni. Ba tafiyar da shi ne matsala ba halinsa ne abin gudu yaje garin mutane ya aikata son zuciya 'kan'kanin yaro dashi. Baba ya ce." Hakan ya yi, tunda tare suke wasa kin ga ba za a d'auke masa abokinsa ba. Shi ma Kamalun ya zauna. Ai ba wani jimawa za mu yi ba, kwana uku ne.
Akan dole Kamalu ya ha'kura ya shige d'aki yana rusa kuka. Na rarrashe shi sosai tare da kwakwkwafarsa akan ya kula kada bayan bana nan ya d'auko mini magana.
Da zamu tafi na bawa Ummansu Hadiza dubu uku nace idan za ta yi girki ta dinga zuba masa da kudin karin kummalo dana makaranta. Hakan ya 'bata wa Ummansu Saminu rai. Ko adawo lafiya ba ta yi mana ba har muka fita daga gidan. Yusi duk ya takura har da 'yar kwalla ganin mun tafi ba tare da d'an'uwansa ba.

Anti Yagana ta yi murna sosai mussaman da ta ga har da Babanmu farincikina ya tsananta. A gidanta muka sauka tunda mijinta ba lefi yana da yar wadata direban babbar mota ne ta sauke mu da abinci mai rai da lafiya. Wajejen shida na yamma Babanmu ya fita zaga gari domin dama garin ba bakonsa ba ne, ya saba zuwa tun yana saurayi yake hada-hadar kasuwancin huluna tsakanin kano da maiduguri.

Anti Yagana ta kalle ni a nutse ta ce." Na ga duk kwarmin Idonki ya zurma Amina ke da jikinki ya baya nuna rama amma wannan karon ya nuna wuyanki da yake cike da guru ya rairaiye akwai abinda yake damun ki ko?"

Maganarta ta fama mini miki da yake yi mini ciwo hawaye suka fara kasa tsare a kumatuna. Ta ce." Ke dama can abin kad'an sai ki sa masa kuka, ba ki da juriya, idan matsalar gidanmu ce ya ci ace kin saba da ita, ki godewa Allah tunda baki rasa komai ba, kowane bawa fa da irin kaddararsa ."

Cikin kukan da yake yun'kuro mini na ce." Anti Yagana ki sanya Kamalu a addu'a da sauran al'ummar muslimi bakidaya. Matsalarsa ce ta fi damuna a yanzu."

Cike da damuwa ta ce." D'azu na so na hasashi wani abu da muna magana da Babanmu akan yaran gidan, amma ban kawo wani mummunan abu daga gare shi ba. Ki fad'a mini me yake yi da har zai zame miki matsala."
Nasa hannu na gogewa hawayen da suke ta zuba a kumatunna. Na ce." Anti Kamalu da Saminu suna nema su fita zakka a zuri'ar gidanmu." Gabad'aya kaf na kwashe duk abinda yake faruwa na fad'a mata.
Na cigaba da cewa." Auran dai da nake gudu shi zan yi anti saboda ina ganin kamar shine zai katange Kamalu da Saminu, tunda sun yi nesa da juna.

Ta nisa kafin ta ce. " Kina da wanda ki ka tsayar ne? kuma kina da tabbatacin zai ri'ke miki yara har biyu Amina mazan nan fa basu da kirki kad'an ne suke iya kawar da kansu akan yaran da basu suka haife su ba, gashi idan suna nema sun iya dadin baki."
Nasa hannu na goge hawayen kumatuna a sanyaye na ce." To anti ya zan yi ne? Baba Sule ya matsanta mini har dasu duka akan sai na auri Ubangidansa Alhaji muntari. Gashi kullum baya fad'in alheri akan yarana, zagi da gori irin Wanda baya yi musu."

Cikin bacin rai ta ce." Kamarki Amina da shekaru talatin da yaranki zai fitar da hannu ya dake ki, me ya yi zafi, wai don Allah me yake damun Baba Sule ne, Ashe har yanzu bai canza d'abi'a ba, ai kin wuce duka."

"Wallahi anti ba dukan ne ya fi damuna ba yadda yake zagin Kamalu Yana aibata shi da mugun fata shine abinda ya fi damuna."

Ta gyad'a kanta cikin takaici ta ce." To yanzu me Babanmu ya ce akan maganar ni gaskiya lamarin bai kwanta mini a rai ba, na lura kudi ne suka rud'i Baba Sulen ya daga hankalinsa, ki nutsu sosai, kada ki yi gaggawa a zo ana lissafa miki aure Amina "

"Anti Babanmu fa ya amince, kema kin san tuntuni kin sani bashi da katabus sai abinda Baba Sule ya zartar a gidansa. Kuma haka kowa zai ha'kura, tunda ya ji maganar Alhaji Muntari ya yi na'am da ita, yanzu maganar da nake miki daga mun koma gida za a yi maganar d'aurin aure."

Ta zuba mini ido da damuwa mai yawa a tare da ita ta ce." To ke ya ki ke ganin kamun ludayin mutumin, ke ba yarinya ba ce Amina, ki zauna ki karance shi tsaf da dabi'u da halayensa sannan kuma na san ba zai rasa iyali ba."

"Matansa biyu, da Yara takawas anti, ba lefi dai karon farko ya fito mini da kyawawan halayensa. Ya yi alkawarin ri'ke mini yara, sannan yana da sanyin hali da Kyauta, abinda na yi nazari akansa kenan. Anti kin san ai ba zai bud'e mini mununan halaye ba tunda nema yake yi zai danne sai zama ya yi zama tukkuna, amma ni shawarar da na yanke shine ba zan yarda na haihu ba tukkuna sai na ga kamun ludayinsa da zamantakewatarmu."

"To kin yi shawara mai kyau anan, idan Allah Ya kaddara auran naku sai ki yi takatsantsan da kyau.
Idan kin lura gidan zama ne, kuma tsayayye ne akan komai sai ki fara ajiye yaranki, domin yanzu mafi akasarin mazan yanzu auran dandano suke yi, ko kiga sun aureki da wata manufa, tafiya kad'an a fara samun matsala. Ba na fatan haka ta faru dake, sannan ki yi istahara akan sha'anin, Allah Ya tabbatar da alheri."

Maganganunta suka sake karfafa mini gwiwa, na ji a raina zan iya auran mutumin koda ba na jin sonsa a raina zan zauna dashi muddin na fahimci cewa yana da nagartar da za a had'a zuri'a dashi zan saki jikina na haihu kamar yadda yake buk'atar Allah Ya wadata shi da zuri'a.

Washe gari da wuri muka shirya muka nufi can family house su Mamanmu. Da yake 'yar dangi ce, gidan a cike mata da maza ana ta hidima.
'Yan'uwanta suka dinga murnar zuwa. Na shiga cikinsu sosai Muna gaisawa da tambayar bayan rabuwa. anti Falmata itace 'yar autarsusu sa'ar anti Yagana ce don Mamanmu da mahaifiyarta da muke kiranta da Dada sun had'a wankan jego tazarar da take tsakaninsu ta kwana tara ce.
Ta shigo cikin irin shigarsu tana fad'in." Amina Idonki kenan ko? kin manta da mu a duniyar ko a waya ba kya kira a gaisa, duk wanda ya damu dake sai dai ya kira ki, idan kudin motar zuwa ne ba ki dashi ba sai ki fad'a a tura miki ba .
Na ce." Wallahi ko daya antina, ayyukane sukayi yawa. Kin san ina koyarwa, Ina yin d'inki sosai na mata, bayan haka na kan yi huluna da jakunkuna akai mini kasuwa, ke har aikatau Ina yi wa mutane, wannan shine dalilin da ya sanya ba na samun lokacin kaina anti, ku yi hakuri."
Dada dake zaune cikin kwalliya jikinta nanna'de da lifaya taci jan kunshi kafa da hannu.
Ta harare ni tana cewa." Ke kya ji dashi dai, dama can ba kirki ne dake ba, kin fi karkarta can dangin babanki, sau nawa ana kawo ki nan tunda kuruciya ki dasa mana kukan safe daban na rana daban, ke sai kin koma cikin 'yan-uwanki da suke azabtar dake "

Dariya na yi na ce." Dada ai lokacin da kuruciya. Kuma kin ga ku baku da k'ananun yara irina a lokaci sai Babandi, duk da ya girme ni dashi muke wasa. idan ya tafi makaranta ko gidansu sai na zama ni kadai, shiyasa nake yi muku kuka."
Chapter 12 · 0% Book details