← Book details Fil'azal Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 29

Sashe 9

Fil'azal Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*** *** *** *** *** *** *** *** *SHIN WANENE JAROOD?* *** *** *** *** *** *** *** *** Asalin mahaifinsa Sarkin Agadez Abdulmuminu Haifaffen cikin garin Agadez ne, shi kadai iyayensa suka haifa amatsayin namiji, yanada yayyi hudu duk mata ne. Abdulmud’allab da Fa’iza sune iyayensu. mahaifinsa Abdulmud’allab ya gaji sarauta ne agurin mahaifinsa, kasancewarsa shi kadai namiji a yaran babansa. Shima se ubangiji ya bashi namiji d’aya wato Abdulmuminu, bayan rasuwar mahaifinsa Abdulmud’allab da mahaifiyarsa hajiya Faiza mace me kirki duksun rasu. Abdulmuminu ya Auri Hajiya Fatima matarsa ta farko itama cikakkiyar buzuwa ce, kmr yadda yake shima buzu ne, tin tana 10yrs ya aureta har takai 20yrs bata samu haihuwa ba, dan haka ya karo aure saboda haihuwa yake nema ido rufe musammamma ta d’ana miji saboda yanaso yasamu magaji. Ya Auro hajiya Sadiya itama cikakkiyar buzuwa ce, hajiya sadiya tinda tashiga gidan sarki Abdulmuminu taketa neman yadda za ayi tasamu haihuwa kota halin yayane, amma abu yaci tura, ko bari takasa yi itama duk bin bokayenta da malamanta Amma abu ya faskara. Ana çıkın haka ubangiji yabawa Hajiya Fatima Wacce Ake kira da Giwar Sarki ciki, nanfa sarki ya rikice da murna, ya ninka tarairayarsa da kauna Akan hajiya fatima daman yana santa kowa ma yasan yana santa sbda Auren Soyayya sukayi da ita, Hakan ne yasa yake kiranta Da giwar Sarki Abdulmuminu. ita kuma hajiya sadiya ya Aureta ne danta haifa masa yara, sam baya santa zan iya cewa de arashin uwa ne yayi uwar daki. Hajiya sadiya tinda takula hajiya fatima nada ciki tashiga shige ficen yadda za’ayi çıkın ya zube, tayı-tayi abu ya faskara, seda aka haifi cikinnan akayi rashin sa’a agareta aka haifa d’ana miji. Ranar hajiya sadiya batayi bacci ba, tanada Aminiya Hajiya bara’atu ta kirata a rikice tini suka dunguma gurin boka sukace akashe yaron, boka be boye Musu ba yace baze yuba akashe yaron, ya sanar dasu in suka matsa se sun kashe yaron su suna iya mutuwa har lahira. Jin hakan ya matukar firgita Hajiya sadiya ta kalli kawarta tace “Toh meye mafita…” hajiya bara’atu tace ba wata mafita domin ita kanta ya kulle. Hajiya sadiya tayi jim can wata dabara ta fado ranta, ta roki bokan daya kashe masa gabansa na har abadan ta yadda baze moruba har abadan a tunanin hakan zeyi sanadin daze kashe kansa da kansa, sbda namiji ba Bura Ai ba namiji , wato de ze zama Gashi a raye amma matacce ma yafisa daraja. Tini boka ya aiwatar mata da hakan, sannan ta karada asa masa tsanar sarauta da masarauta, tasa a nisanta zuciyarsa ma da kasar Agadez baki daya, acewarta bataso ya girma ya mulqa kasar Agadez tinda ita bata haihu ba kwara kowa ya rasa mulkin ita da hajiya fatima. Batare da Hajiya fatima da sarki sun sani ba akasha suna yaro ya amsa Sunan mahaifin babansa wato kakansa Abdulmud’allib ake masa lakabi da JAROOD, sarki ya dauki san duka duniya ya daurama JAROOD, Hajiya sadiya takasa cire San JAROOD azuciyar sarki, wannan San na Allah ne tayi kadan ta rabasa, haka bokanta yagaya mata. JAROOD Yanada 5yrs aka haifi Mardiya,. Kasancewarta mace yasa Hajiya sadiya rashin jin damuwa sosai amma fa bakin ciki kmr ya kasheta ganin ita shekaru nata tafiya Amma shiru bata haihu ba bama alamar zata haihu kullum tana ziryar yawon zuwa gun bokaye amma ba riba, kullum se kara dilmiyewa takeyi kudinta nagun bokaye Gashi ba kudine dasu ba se abinda tasamu agun miji, amma taki nutsuwa kai inka ganta bakace matar sarki bace kullum a lalace take sbda tasawa rayuwarta mugun Abu da hassada da bakin ciki, ta rantse tukunyar Hajiya fatima bazata tafasa ba, gashi ta-ta ko zafi takiyi, karfin asirinta ke zaunar da ita agidan Sarki Amma Sam ba kaunarta yake ba, danginsama sam basa santa saboda bakin halinta da rashin haihuwar da batayi ba. ita kuma hajiya Fatima daman yar Waziri mahaifin Abdulmuminu ce, sam ba ruwanta ga hakuri ga Addini, ko magana ma bata dameta ba, seda Aka Auro Hajiya Sadiya shine tayi baki na dole ganin irin cutarta da Hajiya Sadiyar keyi, tashigo tasameta da mijinta amma kuma ta dage dole seta fitar da ita a dakin mijinta bayan ita tazo tasameta. Hajiya Fatima tazo ta kara haihuwar yarinya mace Sajeeda,. Hajiya sadiya tashiga shige da fice har seda taga ta dakatar da hajiya Fatima daga haihuwa tinda ita bata haihu ba, ahakama bada san ranta aka haifa ukun ba, da ace da yadda zatayi databisu dukta kashe yara ukun. Sarki yakuma san hajiya fatima ita da yaranta saboda yafi samun kwanciyar hankali da hajiya fatima ita hajiya sadiya ko iya tarairayar miji da kulawa batayi ba se hauka dabin bokaye da makirci. Haka JAROOD ya taso kwata-kwata bayasan harkar sarauta, har zuwa balagarsa, ko irin mafarkannan na balaga sam bayayi, bayasan mata kwat-kwata, koya gansu basa burgesa kuma basa bashi sha’awa ko kadan, baruwansa da kowa, inka gansa da wani toh da malam wanzan ne shine ko ina zasuje tare suke zuwa , makaranta ma tare suke zuwa kafin dağa bisani yazo yabar kasar yake Egypt yayi karatunsa Akan Kasuwanci, burinsa kawai kasuwanci bayasan wani harkar sarauta ko mulki-mulkinnan. Seda JAROOD yakai 20yrs mahaifiyarsa ta fahimci a gaskiya beda lafiya saboda sam bata ganin yana Abu yadda maza keyi , Ya taso da kyau sosai da kwarjini ga kwakwalwa mata nasanshi sosai amma seta kula shi sam mata basa gabansa, sema daya zauna taji yanata sukar mata yana zaginsu, afari tasha aljanace ta auresa. Dan haka ta dukufa nemo masa magani. seda yakai 25yrs ne sukaje gun wani me magani shi yake tabbatar musu da gabansa be Aiki acewarsa kuma gaban nasa baze taba Aiki ba har abadan. Ba karamin tashin hankali hajiya fatima da sarki suka shiga ba harshi JAROOD din hankalinsa ya tashi. Hajiya Fatima tadinga kuka tin kafin ace asiri aka masa taji Ajikinta asirin aka masa kuma tasan hajiya sadiya ce ta masa dukda de batasan gaibu ba amma biri yayi kama da mutum. Me martaba ya dinga bata hakuri yace insha Allahu ta kwantar da hankalinta duk inda magani yake seya nemo masa. Aka fitar da JAROOD kasashen waje domin a nemo masa lafiyar gabansa Amma duk inda akaje sede likitoci suce su lafiya lau suka gansa basuga wani ciwo a tattare da gabansa ba. Ko ina akajefa mgnr daya ce agun lokitoci har şarkı ya gaji ya dawo ga magungunan gargajiya sune basu can basu nan, amma har yanzu ba’adace ba, hajiya sadiya kam tana gefe tana dariya zuwa yanzuma wanda yama JAROOD mugun asirin ya rasu tanada tabbacin bawanda ya isa ya karya asirin afadin duniya acewarta. A haka har JAROOD yakai 30yrs har yanzu yana kan karatunsa a egypt ya hadu da Abokai yan Nigeria harma yakan bisu Nigeria ağarın Kano, in anyi Hutu a school dinsu, da haka yasaba da Nigeria yaji Tafi masa dadih Akan Niger, tin me martaba beson zuwansa Nigeria har yazo ya hakura ganin yadda JAROOD din keson nigeria suma suka fara zuwa Nigeria gün iyayen abokanayen nasa sbda JAROOD din zumunci ya kullu atsakani toh acikin abokan nasa Akwai wani Hassan dan kaduna ne, JAROOD yazo yana Binsa kaduna daga kanon gidansu İbrahim, har yazoma yafi sabawa da kadunan, yazamana har gidaje sarki yasaya a kadunan sbda JAROOD suma kuma sukazo suka saba da kadunan, JAROOD ya fara kasuwanci kadan-kadan a kano da kaduna yana duba abinda babu seya Saro Akasar waje, a haka yadinga habbaka yana karatu kuma yana kasuwanci shide ba ruwansa da mace. Zuwa lokacin tini anyima mardiya aure anan cikin agadez din. Hajiya fatima taje nemawa JAROOD magani awani kauye dake Cikin Agadez, anan me maganin yace ai warakar JAROOD na jikin mace, yace amasa aure. Hajiya fatima Nadawo wa tasanar dame martaba, ya gayama Babban amininsa wato wazirinsa sarki beda wani Amini daya wuce Waziri İbrahim,. Tini Waziri İbrahim yace ya bama JAROOD yarsa Zulaikha dukda kuwa yasan da rashin lafiyar gabansa. Şarkı yayi murna sosai, hajiya fatima ma tayi murna sosai Abangaren JAROOD sam beyi murna ba sbda shide yasan beda abinda zeci yarinyar mutane, dan haka besan yazeyi ba, yaso subarsa ya mutu a haka. Mahaifiyar Zulaikha da Zulaikha sunyi murna sosai, mahaifiyar Zulaikha bahaushiya ce Hajiya Safiya cikakkiyar yar nigeria ce haifaffiyar kano. Zulaikha daman tanasan JAROOD amma Sam batasha abinda ake fadi nacewar gabansa be Aiki da gaske bane seda akayi Aure, akasha bikin da ba atabayin irinsa ba Akab garin Agadez din. Amarya ta tare a gidan sarauta Agadez, tanata jira taga miji yazo dakinta amma har Akayi 1week bezoba, Zulaikha atime din kusan 20yrs take daman a hannu, a hannu take takosa taji namiji a gabanta. Seda tayı 2month agidan taji still shiru bata rasa ciba bata rasa shaba, amma sede ango beshigo ba sbda koya shigo besan meze mata ba. Seda tayi 1Month agidan zuwa lokacin JAROOD ya shigo dakinta sun kwana tare ma sun tashi shiru, tafiya tayi tafiya har akayi 3yrs shiru Zulaikha se atime din ta tabbatar da dagaske ne abinda ake fadi, sbda ko hannunta JAROOD be taba rikewa ba, kuma gata cikakkiyar mace ta tara kayan ruwa ajikinta. Akayi 5yrs zuwa lokacin taje ga iyayenta da niyar araba Auren mahaifinta ya mata fada sosai, ya tabbatar mata da duk randa tasake ta rabu da JAROOD toh karta dawo masa gıda kuma ta tabbatar da tsinuwarsa ta tabbata akanta inhar tamatsawa JAROOD yasaketa. Sarki Abdulmuminu beji dadin wannan hukukçun da Waziri ya yanke ba, ya basa hakuri akan kawai araba Auren, Waziri yace ai baze yuba Yarima ba mata ai mutumcinsu ze zube, hakan kuma zesa mutanen Niger su dinga zargin JAROOD wasuma bacewa zasuyi beda lafiyar Gaba ba, sede akwakulo wani sharrin amasa. Dole Zulaikha takoma dakin Aurenta taci gaba da zaman hakuri, bata inda JAROOD be wadata ba kawai matsalarta rashin Bura, ita daze dena mata komi ya bata bura yafi mata komi dadih wallahi ita kadai tasan me takeji, dataji ta koshi se gabanta ya fara Ruwaaaaa, da vibrating. Daman karatun likitanci takeyi taci gaba da karatunta, har JAROOD ya gama nashi karatun ya roki iyayensu Dazu yadda ya koma nigeria domin zuwa lokacin kasuwancinsa yayi kwari sosai a nigeria musamman a arewar nigeria dama
Chapter 9 · 0% Book details