← Book details Exiled Prince Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 27

Sashe 4

Exiled Prince Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shiru Malik dan ba kariya ya fada ba
" Shi ya sa na ce ka zama mai tsare gaba da bayan ka , ba ka san wanda ka ke tare da shi ba , ko da ya na zaune da kai da zuciya daya , wata rana zai iya juya maka baya "

Dogon nunfashi Malik ya ja kafin ya ce " kai ni fa hirar nan ta ka mara ma'ana ta fara isa ta "

Murmushi kadan AMIR ya yi kafin ya ce " ban rike ka ba tashi ka tafi "
" ban son shirme , part di na ne ka ke ciki "
Dariya AMIR ya yi ya na fadin " ba wajen matar ka ba za ka kwana , tashi ka je ni a nan zan kwana "

" kai eh fa haka ne ka ma tuno min , bari na tashi na tafi wajen baby na " ya kai karshen ya na mikewa tsaye

Da sauri AMIR ya taro shi ya na fadin " Wait, Abbi wa ka ke kira da baby "
Hararrar wassa Malik ya yi mishi kafin ya ce " Mummyn ka mana " ya kai karshen ya na kashe mishi ido guda

Dariya sosai AMIR ya yi har da dafe ciki idanun shi na kawo ruwa
Shi ma dai Malik yar dariya ya yi kafin ya tako kusa da AMIR ya dan sunkuyar da kai
Ya rage sautin Muryar shi kamar mai rada ya ce " Ka na ji na ko , ita fa mace yar shagwaba ce ka bar ganin dan ta haifi zankadeden saurayi kamar ka , kullum ta na son a dinga ririta ta , a na shagwaba ta kamar baby , dan ba ka da matar ne shi ya sa ba za ka gane ba "

" ba ni ma son na gane " AMIR ya fada ya na yar dariya

" hmmm AMIR ina guje maka ranar da so zai maka mugun kamu , wlh sai ka yi kuka "

Dan matsowa AMIR ya yi kusa da face din Malik murya kassa kassa ya ce " Har yanzu ba a yi macen da za ta Mallaki zuciyar AL-AMIR NAWFEL BIN JAABAR d'a tilo ga MALIK HICHAM BIN JAABAR jikan MALIK ABDOUL LATIF BIN SAUD , Har yanzu ba ta shigo duniya ba "

Jinjina kan shi Malik ya yi kafin ya ce " Gaskia ne kam , izza a jinin ka ta ke , amma ka sani , mace ce ta haife ka , kamar yadda ta haife ka haka zalika , za ta haifi wadda za ta malake zuciyar ka , duk wannan izzar da ka ke nuna wa sai ta zube a gaban ta , ka jira ka gani "

" Abbi , dubi wuce ka tafi wajen babyn ka , ni kyale ni film zan kala "
Yar karamar dariya Malik ya yi kafin ya kai bakin shi ya sumbaci forehead din AMIR sannan ya ce " ai kai ma baby na , I love you "

Dan murmushi AMIR ya yi kafin ya ce " I LOVE YOU dad "
Jinjina mishi kai Malik ya yi kafin ya mike ya juya ya fara takawa
Har ya yi nisa ya jiyo Muryar AMIR ya na fadin " ka yi min magana da Azim "
Jinjina mishi kai kawai Malik ya yi ba tare da ya ce komai ba har ya ficewar shi ya bar AMIR shi kadai

Bai yi five minutes da fita ba wani mutumin ya shigo parlourn ya na sallama
Ya sha ruwan mamaki ganin AMIR zaune saman kujerar da Malik ke zama , a sanin shi bayan Malik ba wanda ya taba zama saman ta sai yau ga AMIR zaune sama

Karasowa gaban AMIR ya yi ya Zube saman guyiwowin shi ya sunkuyar da kai ya na fadin " Allah ya ja zamanin yarima , dan sarki jikan Sarki , ina mika gaisuwa na ga Adalin shugaba na , Umarnin kadai na ke jira "

Daga mishi hannu AMIR ya yi kafin ya ce " ya isa haka Azim wani aiki na ke son ka yi min , kuma zan so ya tsaya a tsakanin mu "

" umarnin kadai na ke jira ya shugaba na , yadda ka so haka za a yi "

" ina son ka je part di na , Bedroom na farko ba wanda na ke barci ciki ba , ka duba cikin bedside drawer , akwai passport di na , da Visa , duk ka dauko su , sannan ka shiga ka duba cikin closet , ka dauko jakar cumputer di ta ka saka su a ciki ka kawo min ina jiran ka "

Da sauri Azim ya ce " An gama shugaba na " ya na gama fadar hakan ya tashi da sauri ya fice parlourn
[16/09 à 09:57] M.N.M:

❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤

(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥

( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny )

⚘🕊 MALLAKIN MEERAH 🕊⚘

【 THE ROYALTY LOVE ✌👑🌹】

Marubuciyar littafin :【 TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺 】

YOU CAN FOLLOW MY WHATSAPP CHANEL
👇👇👇👇👇👇👇👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i

BOOK .............. 2 🌹👑

________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊________________

{PAGE 3 ❤🔥}

Ya na fita AMIR ya mike tsaye ya nufi glass din da ke bayan shi dan duk ginin na glass ne
Ya tsaya ya na kallon masarautar ya na nade hanayan shi a baya

Ya dauki wajen good ten minutes a hakan kafin Azim ya dawo cikin parlourn ya na sallama
Ba tare da ya juyo ba ya amsa mishi sannan shi cen kassa kassa
Geffen shi Azim ya karaso ya Zube saman guyiwowin shi ya na fadin " An gama ya shugaba na , ga abun da ku ka bukata "

" Ajiye saman Sofa ka zo ina son magana da kai "
Ba musu Azim ya tashi ya koma cikin parlourn ya ajiye jakar saman sofa kafin ya komo geffen AMIR ya Zube saman guyiwowin shi

Cikin nitsuwa AMIR ya ce mishi " mike tsaye Azim , ka san fa ka girme ni a shekaru "

Mikewa tsaye Azim ya yi ya dan ja baya kadan ya tsaya ya na sunkuyar da kan shi sannan ya ce " ya shugaba na , tabass na girme ka da shekaru , amma ai matsayin ka sama da nawa ya ke "

Dan karamin murmushi AMIR ya yi kafin ya ce " Azim duk wannan matsayin ba komai ba ne , a wajen Allah duk daya mu ke , zan tambaye ka wani abu Azim kuma ka fada min gaskia "

" in sha Allah shugaba na idan na sani zan fada maka "

Gyada kan shi kadan AMIR ya yi kafin ya ce " ina son ka fada min , a ganin ka zan iya yin mulkin saudiya kamar na Malik "

Dan karamin murmushi Azim ya yi cikin girmamawa ya ce " Ba zan yi maka kariya ba Shugaba na "

Da sauri AMIR ya katse shi da cewa "ka kira ni da suna na "
Kara fadada murmushin shi Azim ya yi kafin ya ce " ba zan yi maka kariya AMIR amma ina ji a jiki na ba za ka yi mulki irin na Malik ba , no ! Na ka na musaman ne , da sabon salo zai zowa , na san za ka zama Adalin shugaba , Za ka yi Mulki kamar na MALIK AL SAUD dan mulkin shi har yanzu tarihi ne , ka na da zuciya mai kyau ya shugaba na , ina fatan za ka mulke mu da wannan kyakyawar zuciyar ta ka "

Dan karamin murmushi AMIR ya yi kafin ya ce " yanzu a ce ba na nan "

Da sauri Azim ya ce " ba na fatan hakan AMIR domin duk cikin yaran shi Malik ya fi kaunar ka , wannan kowa ya shaide shi cikin masarautar nan , na san ba zai iya jure rashin ka ba "

Shiru AMIR ya yi na dan mintina kafin ya ce " na gode Azim za ka iya tafiya "
Dan sunkuyar da kai Azim ya yi kafin ya ce " na gode ya shugaba na , Sai da Safe " ya fada kafin ya juya ya fice parlourn

Sai da Amir ya dauki wajen good 30 minutes ya na kallon cikin masarautar , ya na kallon yadda jami'an tsaro ke kai kawo
Kafin ya daga kafa slowly ya juyo ya nufi wannan bakar Jakar da Azim ya ajiye saman Sofa ya dauke ta kafin ya juya ya nufi wani corridor da ke fuskantar sofar

Sai da ya wuce kofa uku sannan ya iso ta hudun ya daura yatsar shi saman finger print
Nan take kofar ta bude kan ta har da fadin sunnan shi
A hankali ya shiga cikin dakin yanzu na sallama kassa kassa
Wani tanpasheshen bedroom ne da ga gani ka san na Malik din ne da kan shi dan dakin ya kai girman parlourn da ya fito

bai tsaya wani dube dube ba ya nufi bedside drawer da ke cen da ga cikin dakin
Ya zauna bakin gadon , ya kai hannu ya bude box na farko
Nan ya ga bandir bandir din kudi dirham shakke a wajen
Jakar hannun shi ya bude ya sa hannu ya fara jidar kudin nan ya na saka wa a cikin jakar nan
Sai da ya debi rabin kudin sannan ya meda box din ya bude na kassa
Nan wajen kuma bandir din Dollar ne , cike a wajen
Nan ma sai da ya debi wajen rabin kudin ya saka a cikin yar jakar nan sannan ya hakura ya meda box din ya like , jakar har ta yi yauni ta cika kamar za ta fashe

Rufe zip din jakar ya yi sannan ya ajiye ta geffen shi kafin ya tashi ya nufi wata door
Ya na isa ta bude kan ta ya shiga ciki
Ya na shiga kofar ta meda ta kan ta
Chapter 4 · 0% Book details