← Book details Exiled Prince Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 27

Sashe 20

Exiled Prince Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

a hankali ya gyada kan shi kafin ya ce " in sha Allah za ki sani , zan sa a karo miki Four Milliard saboda kudin ba za su isa ba , Five milliards kennan , ina son ki raba kudin nan tsakanin Gidan Marayu , zan sa a fitar da duk wani kayan abinci na cikin Store da ya wuce Two months , za a raba tsakanin Al'uma musaman manoma da kananan yan kasuwa , haka zalika kudin za a raba su tsakanin Manoma har wajen masarautar , su ma bayin da ke cikin masarautar nan a fidda na su rabon , sannan kuma mutanan Gari ma su karancin hali , kar ki manta da gidajen marayu massalatai da public Schools , Ammie dalilin da ya sa na ce a baki kudin ba momy ba saboda na san wacece ke , na san za ki rabon nan yadda ya dace , kar ki damu ita ma momy za a kai mata nata kudin , kuma in sha Allah bisa wannan tsarin za mu ci gaba "

" Masha Allah " MALIKAT INAS ta fada cikin zuciyar ta , ta na sakin wani kyawatencen murmushi gaskiya abun da ya fada ba karamin burge ta ya yi ba , tabass ya cika sunan shi na magajin Malik

ya na a haka ya juyo Muryar shi ya na fadin " Zan iya tafiya ? "

" Ina kuma za ka je " ta fada ta na mishi hararrar wassa

cikin ko in kula ya ce mata " wajen matata zan je ko da magana "

yar karamar dariya MALIKAT ta yi kafin ta ce " ko daya , yanzu ina uwar gidan ka , za ka tashi ka bar ni ka je wajen Amaryar ka ? "

" In kishi ki ke , yanzu za ki fara " ya kai karshen ya na mikewa tsaye
dan tabe baki MALIKAT ta yi ta na fadin " yanzu Amir ni za ka fadawa haka , dan ka yi amarya , shi ne za ka manta da uwar gida ? "

ko sannu bai ce mata ba ya nufi corridor abun shi
da kallo ta raka shi har sai da ya shiga sannan ta yi wata yar karamar dariya ita kadai

❤⚘ E X I L E D P R I N C E ⚘❤

(LOVE MEETS POWER ) 👑🔥

💔🥀 ( A heart touching love story , Romance , injustice & destiny ) 💔🥀

👑❤ MALLAKIN MEERAH ❤👑

【THE ROYALTY LOVE 👑🕊💖】

Marubuciyar littafin

【TAURIN ZUCIYA 💖💍🌺】

【 BOOK …………………… 2 ❤ 👑】

____________________🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊___________________

PAGE 12 ✍📚

Amir kuwa kai tsaye bedroom din Inaya ya nufa
bakin shi dauke da sallama ya shigo cikin bedroom din kai a sunkuye sannan ya juya ya rufe kofar , ya danna wani button a jikin kofar ya saka mata security
sannan ya juya ya dago kai ya kali cikin dakin

dum ya ji gaban shi ya fadi ya zaro idanu ya na kallon ta

konce ta ke saman bed din ta , ta juyawa kofar dakin baya
ta na sanye da kananan kayan barcin ta
pink colour , wando da kadan ya wuce hips din ta , da yar karamar Riga ko cibi ba ta kai ba , ta na da shilalen hannu , sai hanayan Bra din ta da a ke iya gani , a yi mata wasu kitso guda biyu da gashin ta , sun kai mata har tsakiyar baya , ga kugun nan nata a waje ta saka wata yar siririyar sarka

A hankali ya sauke ajiyar zuciya kafin ya fara takawa ya karaso cikin dakin sannan ya tsaya bakin gadon
nan ya ga ashe ba barci ta ke yi ba , ta na rike da wayar ta , ta na kallon pic din shi , tun lokacin da ya ke 20 years , ya yi matukar mamakin yadda a ka yi ta samu wannan pics din

amma bai ce mata komai ba ya tsaya ya ci gaba da kallon ta
ya na a haka ya ga ta wuce pic din sai saman wani pic din nashi kuma , a wannan ya zaune saman sofa ya daga kai sama saki wani kyawatencen murmushi har wadanan fararen teeth din nashi sun bayana idanun shi na lumshe da allamun ya na tsaka da dariya a ka yi pic din , gaskia pic din ya hadu kamar ba Amir ba

dan karamin murmushi ta saki kafin ta ce " Gaskiya yaya Zayd murmushi na yi maka kyau , why ka daina ? "

ta na gama rufe bakin ta , ya ce mata " ki na so na yi miki ? "
kara fadada murmushin ta ta yi ta na fadin " Eh ina so , amma fara zama tun dazu ka na tsaye saman kai na "

dan zaro idanu ya yi ya na fadin " ta ya a ka yi ki ka san ina nan ? " ya fada dan shi duk a tunanin shi ba ta san ya na cikin dakin ba

murmushi mai dan sauti ta yi ba tare da ta ce komai ba
a hankali ya nufi wajen kafafun ta , ya zauna sannan ya dan sunkuyo ya sa hannu ya cire sneakers din kafafun shi sannan ya dago ya kale ta ya ce " ko za ki iya zama ina son mu yi wata magana "

ba musu ta kashe wayar ta , ta ajiye sannan ta mike zaune ta juyo ta kale shi
sai da ya ji gaban shi ya fadi da ya ci karo da face din ta
gaskiya ba karamin kyau ta kara ba , dama kwana biyu bai saka ta a idanun shi ba , sai ya ga kamar ta sauya mishi lokaci guda
bare kuma ta na shan gyara da ga wajen RIANNA da ita kan ta MALIKAT INAS , abun dai Masha Allah har wani haske ta kara
ta sha wani kunshi Red color saman Hanyan ta gwanin burgewa kamar na sace ta na gudu

ganin yadda ya tsare ta da idanu ya sa ta sakin wani cool murmushi ta ce " yaya Zayd maganar me za mu yi "

sai a lokacin ya dawo cikin hayacin shi , a hankali ya dan sunkuyar da kan shi ya kali hanayan ta
nan ya ga kunshin da a ka yi mata , an yi mata zanen wasu flowers abun ba karamin burge shi ya yi ba

a hankali ya kai hannun shi ya riko nata hannun murya kassa kassa ya ce " wa ya yi miki wannan "

yar karamar dariya ta yi kafin ta ce " Aunty RIANNA ta saka a ka yi mana ni da Nesi "

ba ta gama rufe bakin ta ba ta ga ya dago hannun shi a hankali ya kai saitin bakin shi ya manna mata kiss har da lumshe idanun shi ya yi
wani cool murmushi ta saki ta na kallon shi

sai da ya yi mata kiss sannan ya dago ya kale ta ya ce " gobe za a fara azumi kin sani ko ? "

gyada mishi kai ta yi ta na fadin " Eh yaya Zayd na sani " ta kai karshen ta na komawa ta konta ta na fuskantar ceiling

" kin san gobe za mu tafi Ko ? " ya fada a hankali ya na kallon cibin ta

sai da ta dan dauki lokaci kafin ta ce " na sani yaya Zayd , har na fara kewar ka " ta kai karshen ta na yar karamar dariya

a hankali ya dago da hannu shi ya saka dan yatsar shi cikin hudar cibin ta
a hankali ta dago kai ta mike zaune ta na lekon cibin nata a tunanin ta wani abu ne a ciki ita ba ta san Amir ya ga abun ya ja hankalin shi

janye hannun shi ya yi ya na fadin " ba komai , har yanzu ba ki fada min abun da ki ke so na sayo miki a cen ba " ya fada ya na dago kai ya kali face din ta

komawa ta yi ta konta ta , ta kai hannu ta riko chain din kugun ta , ta fara juya ta ta ce " ni yaya Zayd duk abun da ka kawo min ina so , amma ni kai na fi so " ta kai karshen ta na yar karamar dariya ta lumshe idanun ta

dan lumshe idanun shi kadan ya yi kamar mai jin barci , yarinyar nan ta na neman ta birkice mishi tunani shi da ya zo yi mata bankwana kadai

a hankali ya kai hannu shi ya riko nata ya janye shi gefe ya daura nashi hankali saman flat tunbin ta ya fara shafawa a hankali
shi kan shi bai san ya hakan ta faru ba kawai sai jin kan shi ya yi ya kai bakin shi saman cikin ta ya manna mata kiss sannan ya fido tongue din shi ya saka cikin hudar cibin ta

a dubu dari Inaya ta bude idanun ta , ta mike zaune Muryar ta har kerma ta ke yi ta na fadin " yaya Zayd me k... " ba ta kai karshen maganar ba ta ji saukar yatsar shi saman lips din ta

ya zame tongue din shi , ya dago kai ya kawo face din shi saitin ta ta murya cen kassan makoshi ya ce " kar ki ji tsoro ba abun da zan yi miki "
wani cool murmushi ta saki ta na gyada mishi kai

a hankali ya zame hannun shi ya na fadin " na yi kewar ki sosai idan na tafi , specially wannan dan bakin tsiwar " ya kai karshen ya na kai yatsa ya shafi lips din ta

" da gaske yaya Zayd za ka yi kewa ta " ta fada ta na murmushi

a hankali ya gyada mata kai allamun eh

nan take idanun ta su ka kawo ruwa
da sauri ya girgiza mata kai ya na fadin " please kar ki min kuka , so ki ke na kassa samun nitsuwa "
Chapter 20 · 0% Book details